Wulayati Ya Ce Samun Kalamai Masu Karo Da Juna Tsakanin Trump Da Mukarrabansa Yana Zubar Da Kwarin Gwiwa
Published: 21st, May 2025 GMT
Mai ba da shawara ga jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa: Kalamai masu karo da juna na Trump da mataimakansa sun zubar da kwarin gwiwa ga gwamnatin Amurka
Mai bai wa Jagoran juyin juya halin Musulunci shawara ya bayyana cewa: Sabani da ake ci gaba da yi a cikin maganganu da ayyukan Trump da takwarorinsa na haifar da rashin amincewa da gaskiyar gwamnatin Amurka.
Ali Akbar Velayati mashawarcin Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran ya yi tsokaci a cikin wani sako da ya wallafa a dandalin X kan kalamai masu cin karo da juna da jami’an Amurka suka yi.
Mai bai wa Jagoran juyin juya halin Musulunci shawara ya ce ci gaba da cin karo da juna a cikin maganganu da ayyukan Trump da mukarrabansa ya haifar da rashin amincewa da gaskata gwamnatin Amurka.
Velayati ya kara da cewa: Wannan batu ba a taba ganin irinsa ba a tarihin diflomasiyya a duniya kuma yana nuni da halin da ake ciki a cikin gwamnatin Amurka.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: juyin juya halin Musulunci gwamnatin Amurka
এছাড়াও পড়ুন:
Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna
Don haka, a cikin sanarwar da aka fitar a wannan karo, kasashen Afirka sun nuna yabo kan jajircewar kasar Sin, da kuma kudurin da kasar ta dauka na kare adalci, da kuma ingancin tsare-tsaren tattalin arziki da cinikayya na kasa da kasa. Har ila yau, kasar Sin ita ma ta nuna godiya ga kasashen Afirka, kan yadda suke bin ka’idojin kare ‘yancin kai, da adalci, tare da tsayawa kan matsaya guda wajen fuskantar matsin lamba da aka sanya musu.
Hakika idan mun tantance kwarin gwiwar Sin da Afirka, za mu ga da farko ya zo daga dangantakarsu mai dorewa ta hadin gwiwa da juna. Za mu iya daukar misalin bangaren ciniki: daga shekarar 2000, lokacin da aka kafa dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka, zuwa bara, yawan ciniki tsakanin Sin da Afirka ya karu daga dalar Amurka biliyan 13.92 zuwa dalar Amurka biliyan 295.56, wanda ya karu da fiye da sau 20. Kana kasar Sin ta kasance abokiyar ciniki ta Afirka mafi girma a duniya tsawon shekaru 16 a jere. Sa’an nan, a watanni hudu na farkon bana, darajar ciniki tsakanin Sin da Afirka ta kai dalar Amurka biliyan 103.1, adadin da ya karu da kashi 8.1% bisa na makamancin lokacin bara. Kana idan mun duba nan gaba, a cikin wasikar taya murna ga taron da aka gudanar a birnin Changsha, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana cewa, za a aiwatar da shirin ba da damar yafe harajin fito 100% ga kasashe 53 dake nahiyar Afirka masu huldar diflomasiyya da kasar Sin, kana a sa’i daya kuma, zai samar da karin sauki ga kasashe mafin karancin tattalin arziki a Afirka don su fitar da kayayyaki zuwa kasar Sin. Wadannan alkaluman da na ambata sun nuna cewa, daga a baya har zuwa yau, da kuma nan gaba, hadin gwiwar cinikayya tsakanin Sin da Afirka na kara habaka. Wannan ya nuna yadda amintattun abokan hadin gwiwa ya kamata su kasance tare da juna.
Ko ta yaya wasu kasashe ke tayar da hankali a duniya, za mu iya ganin wannan hoto: Sin da Afirka, aminai na kwarai, suna tsayawa tare da juna, rike da hannayen juna, a kokarin tabbatar da ci gaban kasashensu na bai daya. (Bello Wang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp