Iyalan Sarkin Da Aka Kama Suna Neman Taimakon Kudin Fanso Shi Miliyan ₦50
Published: 19th, May 2025 GMT
Iyalan sarkin Okoloke na jihar Kogi, Oba James Dada Ogunyanda, sun yi kira ga al’umma don taimakawa wajen tara kuɗin fansa Naira miliyan ₦50 da masu garkuwa suka buƙata. An sace Sarkin ne daga fadarsa a Yagba West LGA ranar Alhamis da ta wuce.
Duk da cewa sun tara miliyan ₦25 ta hanyar sayar da kayansu, iyalan sun ce wasu ‘yan siyasa da suke tsammanin za su taimaka sun har yanzu sun ji shiru.
Masu garkuwar sun fara buƙatar miliyan ₦100 kafin su rage zuwa miliyan 50. Iyalan sun ƙaryata labarin cewa an ƙara rage kuɗin zuwa miliyan, suna mai cewa har yanzu masu garkuwar sun dage kan miliyan 50.
Sun yi kira ga manyan ‘yan siyasa na Kogi ciki har da Sanata Dino Melaye, Sanata Sunday Karimi, Hon Leke Abejide, Hon Faleke da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan da su taimaka wajen cikasa sauran kuɗin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Sarayal Kuds Ta Kai Wa Matsugunin ‘Yan Mamaya Na Sydriot Hari Da Makamai Masu Linzami
Rundunar Sarayar Kudus dake karkashin kungiyar Jihadul-Islami ta sanar da kai wa matsugunin ‘yan share wuri zauna na Sydriot hari da makamai masu linzami da su ka yi sanadiyyar kashe da jikkata sojojin mamaya.
Su kuwa kafafen watsa labarun HKI sun samar da cewa, an tsinkayo harba makamai masu linzami guda 3 daga Gaza zuwa Sydriot.
A gefe daya dakarun “Kassam” na kungiyar Hamas sun sanar da cewa sun kai wasu hare-haren da makamai masu linzami zuwa yankin Q20 a sansanin ‘yan share wuri zauna na ” Nir-Ishaq” da “Miftahim.
Bugu da kari dakarun na “Sarayal-Kuds’ sun sanar da kai wa tankar yaki samfurin Mirkava hari ta hanyar wata nakiya mai karfi akan hanyar Zannah,dake gabashin unguwar Shuja’iyyah a birnin Gaza.
Abinda ya biyo baya shi ne kai wani harin da “Sarayal-Kuds’ ta yi akan sojojin mamaya da suke cikin wani gida, ta hanyar amfani da makamin TBG. Da dama daga cikin sojojin mamayar sun halaka da kuma jikkata.
A ranar Talatar da ta gabata ma dai dakarun “Sarayal-Kuds” sun kai wasu hare-haren na hadin gwiwa da ‘ Kassam’ akan cincirindon sojojin mamaya a arewacin Khan-Yunus.