Aminiya:
2025-07-05@23:42:58 GMT

A soke sakamakon jarabawar JAMB na 2025 gaba ɗaya —Ɗalibai

Published: 15th, May 2025 GMT

Ɗaliban da suka rubuta jarabawar shiga jami’a (UTME) na shekarar 2025 da Hukumar Jarabawar Shiga Manyan Makarantu (JAMB) ta gudanar sun buƙaci a soke sakamakon ɗungurungum.

Ɗaliban sun bayyana haka ne bayan da Hukumar JAMB ta amsa laifin kurakurai da aka samu da suka haifar da yawan rashin ƙoƙarin ɗalibai a jarabawar.

Rashin kyawun sakamakon jarabawar, wadda sama da ɗalibai miliyan 1.5 suka kasa samun mako 200 ya haifar da ce-ce-ku-ce a faɗin Najeriya.

A yayin da wasu suka ɗora laifin a kan matsalar na’ura, wasu kuma sun zargi rashin kyakkyawan shiri da kuma rashin iya kula da lokaci daga ɓanagaren dalibai.

NAJERIYA A YAU: Kuskuren JAMB Da Ya Haddasa Faduwar Ɗalibai A Jarabawa JAMB ta ɗauki alhakin faɗuwar ɗalibai jarrabawar 2025, ta nemi afuwa

Sai dai a ranar Laraba Shugaban Hukumar JAMB, Farfesa ls-haq Oloyede ya kira taron ’yan jarida, inda ya amsa cewa hukumar ta gano cewa laifinta ne, ya kuma ba da haƙuri kan kurakuran da aka samu a jarabawar.

Farfesa Oloyede wanda a yayin jawabin ya fashe da kuka ya bayyana cewa hukumar ta gano haka ne bayan ta sake nazari kan sakamakon jarabawar. Ya ce yawan ƙorafin jama’a ya sa hukumar ta hanzarta yin bitar jarabawar da wuri, maimakon ta jira har sai lokacin da ta saba yi a watan Yuni.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: jarabawar Kurakurai

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin HKI Kimani 40 Ne Suka Halaka Ko Suka Jikata A Jiya Jumma’a A Yankin Shuja’iyya Na Birnin Gaza

Kungiyar Falasdinawa ta Jihadul Islami a Gaza, ta bada sanarwan halaka ko jikatar sojojin yahudawan Sahyoniyya 40 a gaza a wani tarko mai sarkakiyan da suka dana masu.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar Saraya Qudus” reshen soje na kungiyar Jihadul Islamim yana fadar haka a jiya Jumma’a.

Daya daga cikin kwamnadojin dakarun ya bayyana cewa da farko halakar yahudawan ta faru ne a garin Gaza a kuma unguwar shuja’iyya. Inda da farko suka halaka sojojin yahudawa kimani 10 a cikin wani ginin da suka shiga cikinsa tare da amfani da makamai mai linzami, sannan a wani gidan

Sannan waso sojojin kimani 20 sun halaka ko sun ji rauni a lokacin dakarun suka yi am,fani da makamin TBG wanda yake watsa isakar gas da ruwa da kuma gari a inda ya fashe don kona jikin wadanda ya fashe a cikinsu.

Na uku kuma sun tana nakiyoyi masu karfi kan tankar yaki dauke da akalla sojojin yahudawa 6 suka kone .

Labarin ya kara da cewa sojojin makiya a irin wannan halin sun kasa daukar wani mataki in banda gudu daga wurin. Daga karshe ba abinda zaka gani sai gawakin sojoji a waste a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Na’im Kassim: Kare Kasa Ba Ya Da Bukatuwa Da Izinin Kowa
  • Sojojin HKI Kimani 40 Ne Suka Halaka Ko Suka Jikata A Jiya Jumma’a A Yankin Shuja’iyya Na Birnin Gaza
  • Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Masu Neman Karbar Kayan Agaji A Gaza
  • ’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja
  • Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda da ƙwato makamai a Borno
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Harin Kan Cibiyar Makamashin Nukiliya Cin Amanar Diflomasiyya Ce
  • Buhari ba ya cikin mawuyacin hali — Bashir Ahmad
  • ‘Yan Sanda Sun Hana Yunqurin Fasa Shago a Gombe, Tare da Kwato Babur