Aminiya:
2025-05-06@00:14:23 GMT

Ghana ta ci tarar ministoci saboda rashin bayyana kadarorin da suka mallaka

Published: 6th, May 2025 GMT

Shugaban Ghana a wannan Litinin ɗin ya bayyana ɗaukar mataki kan ministoci da sauran masu riƙe da muƙaman siyasa fiye da 40 da suka gaza bayyana kadarorin da suka mallaka.

Wannan na zuwa ne a yayin da Shugaba John Mahama ke ci gaba da zage dantse wajen yaƙi da cin hanci da rashawa a ƙasar da ke yammacin Afirka.

’Yan bindiga sun kashe matar aure bayan karɓar N10m kuɗin fansa ’Yan fashi sun kashe matashi a Kano

A yayin karɓar rantsuwar kama aiki a watan Janairun bana ne Shugaban Ghana ya sha alwashin yaƙi da rashawa domin fitar da ƙasar daga ƙangin matsalar tattalin arziki

A watan Afrilun da ya gabata ne mahukunta suka gurfanar da wani babban jami’in tsaro kan wawure miliyoyin daloli daga wata kwangilar tsaron yanar gizo.

Sai dai ana ganin matakin da Shugaba Mahama ya ɗauka wani babban yunƙuri ne na ladabtar da jami’an gwamnati.

Kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP ya ruwaito cewa muƙarraban gwamnatin da aka samu da laifin rashin bayyana kadarorin da suka mallaka ba za a biya su albashi ba har na tsawon watanni huɗu.

Bayanai sun ce a ranar 31 ga watan Maris ne wa’adin bayyana kadarorin da muƙarraban gwamnatin suka mallaka ya cika, inda za a hana su albashinsu na watanni huɗu.

Sai dai za a riƙe albashinsu na watanni uku a matsayin ladabtarwa yayin da albashin wata ɗaya zai zama gudunmawar da aka tilasta musu domin kafa sabuwar Hukumar Kula da Asusun Lafiya ta Ghana Medical Trust Fund da ake laƙabi fa “Mahama Cares”.

“Ya zuwa rufe aiki a ranar Laraba, 7 ga watan Mayun 2025, duk wanda ya gaza bayyana kadarorin da ya mallaka ya sallami kansa daga nan take” a cewar wata sanarwa da Shugaba Mahama ya yi a birnin Accra.

Sabuwar dokar ta shafi dukkan masu riƙe da muƙaman siyasa da suka haɗa da ministoci, hadimin shugaban ƙasa da shi kansa shugaban ƙasar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kadarori bayyana kadarorin da

এছাড়াও পড়ুন:

An kama masu garkuwa da mutane 3 da kuɓutar da wasu

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta sashen tawagarta masu tattara bayanan sirri (IRT), ta kuɓutar da wasu ’yan ƙasar Ghana biyu da aka yi garkuwa da su tare da damƙe wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da ke aiki a kan iyakokin ƙasashen duniya.

Rundunar ’yan sandan a ranar Juma’ar  ta ce hakan ya biyo bayan rahoton da aka shigar gaban babban ofishin hukumar a Abuja a ranar 27 ga Afrilu, 2025, game da yin garkuwa da wani Anastasia Arthur da aka fi sani da Baidoo, ɗan ƙasar Ghana mai shekara 48.

An gano shanu 25 da suka ɓace a dajin Sakkwato ’Yan kungiyar asiri: Mutum 95 sun shiga hannu a Edo

A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Olumuyiwa Adejobi, ya fitar, ta bayyana cewa binciken farko ya nuna cewa sace Baidoo ya samo asali ne daga wata zamba ta soyayya ta Facebook.

Adejobi ya ce ci gaba da bincike na fasaha ya nuna wani muhimmin wuri da ke da alaƙa da waɗanda suka aikata laifin, kuma an tura jami’ai domin ɗaukar mataki cikin gaggawa.

Ya ce, tare da haɗin gwiwa da hukumar ’yan sandan Ghana, jami’an IRT sun gano wata ƙungiyar masu aikata laifuka da masu garkuwan da ke aiki a ƙasashen Ghana da Najeriya.

Ya ce, “Babban nasarar da aka samu a binciken sun haɗa da kama wani Emeka Christian, ɗan Najeriya mai shekara 27 da ke zaune a Bolgatanga, Upper Eastern Ghana, wanda ya amsa laifin karɓar kuɗi cedis GH10,000 a matsayin kuɗin fansa ga wanda aka yi garkuwa da shi ta hanyar asusun wayarsa na Ghana.

“Ya kuma amince da tura Naira kwatankwacin kuɗin zuwa wani asusun bankin Najeriya mallakar wani Peter Okoye.”

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Manzon Shugaban Kasar Sin Ya Halarci Bikin Rantsar Da Shugaba Nguema Na Gabon
  • Lakurawa: Yadda mafarauta 13 suka gamu da ajalinsu a Sakkwato
  • HKI Ta Tabbatar Da Halakar Sojojinta 2 A Yankin Rafa Na Zirin Gaza
  • OPEC+ Zata Kara Yawan Man Fetur Da Take Haka Da Ganga 411,000 A Cikin Watan Yuli Mai Zuwa
  • Shugaba Xi Zai Kai Ziyara Kasar Rasha
  • Ghana Za Ta Hada Gwiwa Da Gwamnatin Jihar Kebbi Kan Noma
  • An kama masu garkuwa da mutane 3 da kuɓutar da wasu
  • Sin: Adadin Tafiye-tafiye Yayin Ranakun Hutun Murnar Ranar ‘Yan Kwadago Ta Duniya Ya Kafa Tarihi 
  • Yadda sojoji suka kashe manyan ’yan bindiga 5 a Zamfara