Aminiya:
2025-09-18@20:51:34 GMT

Ghana ta ci tarar ministoci saboda rashin bayyana kadarorin da suka mallaka

Published: 6th, May 2025 GMT

Shugaban Ghana a wannan Litinin ɗin ya bayyana ɗaukar mataki kan ministoci da sauran masu riƙe da muƙaman siyasa fiye da 40 da suka gaza bayyana kadarorin da suka mallaka.

Wannan na zuwa ne a yayin da Shugaba John Mahama ke ci gaba da zage dantse wajen yaƙi da cin hanci da rashawa a ƙasar da ke yammacin Afirka.

’Yan bindiga sun kashe matar aure bayan karɓar N10m kuɗin fansa ’Yan fashi sun kashe matashi a Kano

A yayin karɓar rantsuwar kama aiki a watan Janairun bana ne Shugaban Ghana ya sha alwashin yaƙi da rashawa domin fitar da ƙasar daga ƙangin matsalar tattalin arziki

A watan Afrilun da ya gabata ne mahukunta suka gurfanar da wani babban jami’in tsaro kan wawure miliyoyin daloli daga wata kwangilar tsaron yanar gizo.

Sai dai ana ganin matakin da Shugaba Mahama ya ɗauka wani babban yunƙuri ne na ladabtar da jami’an gwamnati.

Kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP ya ruwaito cewa muƙarraban gwamnatin da aka samu da laifin rashin bayyana kadarorin da suka mallaka ba za a biya su albashi ba har na tsawon watanni huɗu.

Bayanai sun ce a ranar 31 ga watan Maris ne wa’adin bayyana kadarorin da muƙarraban gwamnatin suka mallaka ya cika, inda za a hana su albashinsu na watanni huɗu.

Sai dai za a riƙe albashinsu na watanni uku a matsayin ladabtarwa yayin da albashin wata ɗaya zai zama gudunmawar da aka tilasta musu domin kafa sabuwar Hukumar Kula da Asusun Lafiya ta Ghana Medical Trust Fund da ake laƙabi fa “Mahama Cares”.

“Ya zuwa rufe aiki a ranar Laraba, 7 ga watan Mayun 2025, duk wanda ya gaza bayyana kadarorin da ya mallaka ya sallami kansa daga nan take” a cewar wata sanarwa da Shugaba Mahama ya yi a birnin Accra.

Sabuwar dokar ta shafi dukkan masu riƙe da muƙaman siyasa da suka haɗa da ministoci, hadimin shugaban ƙasa da shi kansa shugaban ƙasar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kadarori bayyana kadarorin da

এছাড়াও পড়ুন:

An kashe ’yan ta’addan IPOB da yawa a Imo — ’Yan Sanda

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Imo, ta ce jami’an tsaro da suka haɗa da ’yan sanda, sojoji da DSS sun kashe ’yan ta’addan ƙungiyar IPOB da yawa.

Kakakin rundunar, DSP Henry Okoye, ya ce tawagar ta lalata sansanonin IPOB a yankin Ezioha da ke Ƙaramar Hukumar Mbaitoli, da kuma a Umuele, Ubuakpu, da Amakor a Ƙaramar Hukumar Njaba.

’Yan bindiga sun sako ma’auratan da suka sace a Katsina bayan biyan N50m NAJERIYA A YAU: Wadanne Kalubale Gwamna Fubara Zai Fuskanta Bayan Dawowa Mulkin Ribas?

Ya ce da yawa daga cikin mambobin ƙungiyar sun mutu yayin samamen, wasu kuma an kama su, yayin da wasu suka tsere da raunuka.

Okoye, ya ƙara da cewa an gano bindigogi da harsasai da dama a sansanonin, haka kuma ƙwararru sun lalata abubuwan fashewa da aka samu wuraren.

Rundunar ta jadadda ƙudirinta na wanzar da zaman lafiya a yankunan da abin ya shafa tare da roƙon jama’a su yi aiki tare da jami’an tsaro.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Tinubu Zai Ziyarci Kaduna Ranar Juma’a
  • Yadda jariri ya rasu a bayan mahaifiyarsa yayin tsere wa harin ’yan bindiga a Neja
  • An kashe ’yan ta’addan IPOB da yawa a Imo — ’Yan Sanda
  • Karamar Hukumar Malam Madori Ta Horar Da Mata Kare Kai Daga Cututtukan Mahaifa
  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana
  • Espania Ta Soke Cinikin Makamai Na EUR Miliyon 700 Da HKI Saboda Kissan Kiyashi A Gaza