Aminiya:
2025-11-03@00:15:13 GMT

Ghana ta ci tarar ministoci saboda rashin bayyana kadarorin da suka mallaka

Published: 6th, May 2025 GMT

Shugaban Ghana a wannan Litinin ɗin ya bayyana ɗaukar mataki kan ministoci da sauran masu riƙe da muƙaman siyasa fiye da 40 da suka gaza bayyana kadarorin da suka mallaka.

Wannan na zuwa ne a yayin da Shugaba John Mahama ke ci gaba da zage dantse wajen yaƙi da cin hanci da rashawa a ƙasar da ke yammacin Afirka.

’Yan bindiga sun kashe matar aure bayan karɓar N10m kuɗin fansa ’Yan fashi sun kashe matashi a Kano

A yayin karɓar rantsuwar kama aiki a watan Janairun bana ne Shugaban Ghana ya sha alwashin yaƙi da rashawa domin fitar da ƙasar daga ƙangin matsalar tattalin arziki

A watan Afrilun da ya gabata ne mahukunta suka gurfanar da wani babban jami’in tsaro kan wawure miliyoyin daloli daga wata kwangilar tsaron yanar gizo.

Sai dai ana ganin matakin da Shugaba Mahama ya ɗauka wani babban yunƙuri ne na ladabtar da jami’an gwamnati.

Kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP ya ruwaito cewa muƙarraban gwamnatin da aka samu da laifin rashin bayyana kadarorin da suka mallaka ba za a biya su albashi ba har na tsawon watanni huɗu.

Bayanai sun ce a ranar 31 ga watan Maris ne wa’adin bayyana kadarorin da muƙarraban gwamnatin suka mallaka ya cika, inda za a hana su albashinsu na watanni huɗu.

Sai dai za a riƙe albashinsu na watanni uku a matsayin ladabtarwa yayin da albashin wata ɗaya zai zama gudunmawar da aka tilasta musu domin kafa sabuwar Hukumar Kula da Asusun Lafiya ta Ghana Medical Trust Fund da ake laƙabi fa “Mahama Cares”.

“Ya zuwa rufe aiki a ranar Laraba, 7 ga watan Mayun 2025, duk wanda ya gaza bayyana kadarorin da ya mallaka ya sallami kansa daga nan take” a cewar wata sanarwa da Shugaba Mahama ya yi a birnin Accra.

Sabuwar dokar ta shafi dukkan masu riƙe da muƙaman siyasa da suka haɗa da ministoci, hadimin shugaban ƙasa da shi kansa shugaban ƙasar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kadarori bayyana kadarorin da

এছাড়াও পড়ুন:

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Wannan mataki ne awanni kaɗan bayan ɓangaren Damagum ya dakatar da Anyanwu da wasu mutane uku, lamarin da ya ƙara ta’azzaea rikicin shugabanci a cikin jam’iyyar PDP.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami November 1, 2025 Manyan Labarai Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su November 1, 2025 Manyan Labarai Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar
  • Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
  • Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik
  • Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Iran Ta Sanya  Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3
  • Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta