Aminiya:
2025-09-17@23:28:55 GMT

Yadda ’yan fashi suka yi wa mafarauta kisan gilla a Bauchi

Published: 5th, May 2025 GMT

’Yan fashi sun harbe mafarauta da fararen hula kimanin 19 har lahira a Karamar Hukumar Alƙaleri ta Jihar Bauchi.

A yayin ziyarar da ya kai wurin, Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Bauchi, Sani-Omolori Aliyu, ya ba da umarnin yin cikakken bincike da kuma tura karin jami’an tsaro yankin.

Mazauna kauyen Mansur sun ce an kashe ’yan farauta guda tara da kuma fararen hula guda goma, kuma an yi jana’izar ’yan bangar a kauyen Mansur kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

Amma ’yan sanad da jami’an Ƙaramar Hukumar Alƙaleri ba su ce komai ba kan adadin mamatan ba.

Kakakin ’yan sanda na jihar, CSP Ahmed Mohammed Wakil, ya ce kwamishinan ya tattauna da masu ruwa da tsaki a yankin, inda ya buƙaci jama’a kwantar da hankalinsa, ya kuma kasance a cikin shiri, tare da bai wa ’yan sanda goyon baya wajen gudanar da binciken su.

Kwankwaso: Abba ya mayar wa Baffa Bichi martani Umaru ’Yar’adua da shugabannin Najeriya da suka rasu a kan mulki NAJERIYA A YAU: Abin da ke kai matasan Najeriya ci-rani wasu ƙasashen Afirka

Wakil ya ce, “A ranar 4 ga watan Mayu, 2025 mun samu rahoto cewa tawagar hadin gwiwar mafarauta daga Duguri da Gundumar Gwana, da ke sintiri a kan hanyar Duguri, Mansur, da dajin Madam da ke kan iyakar jihar Bauchi da Filato, sun yi araba da ’yan fashi, inda a arangamar aka kashe mutane da dama daga bangarorin biyu.

“Mun tura tawagar jami’an tsaro wurin, inda suka gano gawarwakin jami’an tsaro da fararen hula daga kauyen Sabuwar Sara, wadanda ’yan fashin suka harbe su a yayin da suke kokarin tserewa daga harin suka mutu.

“Rundunar ta tura tawaga ta musamman domin kamo duk masu alaƙa da wannan aika-aika.”

Ya kuma ba da  tabbacin cewa za a yi bincike cikin gaskiya da adalci domin gurfanar da wadanda suka aikata laifin a gaban ƙuliya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda yan fashi mafarauta

এছাড়াও পড়ুন:

Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza

Kwamitin bincike mai zaman kansa na Majalisar Dinkin Duniya, ya fitar da wani rahoto mai zargin Isra’ila da laifin aikata kisan kiyashi a zirin Gaza.

A cikin sabon rahoto da ta gabatar a ranar Talata, MDD ta zargi shugaban kasar Isra’ila Isaac Herzog, da firaministan kasar Benjamin Netanyahu, da kuma tsohon ministan tsaro Yoav Gallant da “kimsa kisan kiyashi.”.

Rahoton ya tattara batutuwan da suka shafi farar hula kai tsaye, ciki har da yara, ya kuma bayyana cewa kisan kiyashin da ake yi ya fi yawa fiye da yadda aka yi tashe-tashen hankula a baya.

Masu binciken sun kuma tabbatar da cewa da gangan Isra’ila ta haifar da yanayin da ke barazana ga rayuwar Falasdinawa ta hanyar toshe hanyoyin samun muhimman kayayyaki na wannan al’umma.

Rahoton ya biyo bayan wani bincike da aka yi na tsawon shekaru biyu, kuma ya yi nuni da yadda ayyukan Isra’ila ke a matsayin kisan kare dangi.

A martanin da ta mayar, Isra’ila ta yi watsi da sakamakon binciken da cewa “karya ce “, ta kuma bukaci da a rusa hukumar nan take.

A sa’i daya kuma, kwamitin bincike na MDD ya yi kira ga kasashe da su daina baiwa Isra’ila makamai da kayan aikin da za a iya amfani da su wajen aikata kisan kare dangi.

Fitar da rahoton na zuwa ne mako guda gabanin babban taron Majalisar Dinkin Duniya a birnin New York, inda ake sa ran kasashe da dama za su amince da kasar Falasdinu a hukumance.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran da Saudiyya sun bukaci hadin Musulmi game da halin da ake ci a yankin September 17, 2025 Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza September 17, 2025 Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza September 17, 2025 Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza. September 16, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaida Dake Yamen September 16, 2025 Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki 5 A Wajen Taron kere-kere . September 16, 2025 Iran Ta Bukaci IAEA Tayi Tir Da Harin Da Isra’ila Ta Kai A Tashoshin Nukiyarta. September 16, 2025 Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana September 16, 2025 Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi September 16, 2025 Pezeshkian: Ta’addancin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Kan Kasar Qatar Zalunci Ne Ga Diflomasiyya September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025
  • Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa