Aminiya:
2025-05-05@18:19:47 GMT

Yadda ’yan fashi suka yi wa mafarauta kisan gilla a Bauchi

Published: 5th, May 2025 GMT

’Yan fashi sun harbe mafarauta da fararen hula kimanin 19 har lahira a Karamar Hukumar Alƙaleri ta Jihar Bauchi.

A yayin ziyarar da ya kai wurin, Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Bauchi, Sani-Omolori Aliyu, ya ba da umarnin yin cikakken bincike da kuma tura karin jami’an tsaro yankin.

Mazauna kauyen Mansur sun ce an kashe ’yan farauta guda tara da kuma fararen hula guda goma, kuma an yi jana’izar ’yan bangar a kauyen Mansur kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

Amma ’yan sanad da jami’an Ƙaramar Hukumar Alƙaleri ba su ce komai ba kan adadin mamatan ba.

Kakakin ’yan sanda na jihar, CSP Ahmed Mohammed Wakil, ya ce kwamishinan ya tattauna da masu ruwa da tsaki a yankin, inda ya buƙaci jama’a kwantar da hankalinsa, ya kuma kasance a cikin shiri, tare da bai wa ’yan sanda goyon baya wajen gudanar da binciken su.

Kwankwaso: Abba ya mayar wa Baffa Bichi martani Umaru ’Yar’adua da shugabannin Najeriya da suka rasu a kan mulki NAJERIYA A YAU: Abin da ke kai matasan Najeriya ci-rani wasu ƙasashen Afirka

Wakil ya ce, “A ranar 4 ga watan Mayu, 2025 mun samu rahoto cewa tawagar hadin gwiwar mafarauta daga Duguri da Gundumar Gwana, da ke sintiri a kan hanyar Duguri, Mansur, da dajin Madam da ke kan iyakar jihar Bauchi da Filato, sun yi araba da ’yan fashi, inda a arangamar aka kashe mutane da dama daga bangarorin biyu.

“Mun tura tawagar jami’an tsaro wurin, inda suka gano gawarwakin jami’an tsaro da fararen hula daga kauyen Sabuwar Sara, wadanda ’yan fashin suka harbe su a yayin da suke kokarin tserewa daga harin suka mutu.

“Rundunar ta tura tawaga ta musamman domin kamo duk masu alaƙa da wannan aika-aika.”

Ya kuma ba da  tabbacin cewa za a yi bincike cikin gaskiya da adalci domin gurfanar da wadanda suka aikata laifin a gaban ƙuliya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda yan fashi mafarauta

এছাড়াও পড়ুন:

Maniyyata Daga Turai Akan Dawakai Sun Isa Kasar Saudiyya Domin Yin Aikin Hajjin 2025

Mahajjata hudu – daya daga Maroko sauran kuma daga Sifaniya – sun isa kasar Saudiyya a kan dawakai a wannan makon da ya fice don gudanar da aikin Hajjin 2025, wanda hakan ke tunatar da al’ummar Musulumi tsarin zuwa aikin hajji a shekaru da dama da suka gabata. Mahajjatan sun isa zuwa kasar Saudiyya ne ta kan iyakar Al Hadithah da ke Al Qurayyat, inda jami’an gwamnati suka tarbe su tare da duba lafiyarsu, da kuma basu abubuwan sha don jinjin irin tafiyar da suka yi ta tsawon makonni. Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe Nijeriya Ta Yi Asarar Naira Biliyan 118 Sakamakon Barnatar Da Iskar Gas A Watanni 2 Hotunan yadda suka yi kura amma cikin nasara sun bazu a yanar gizo, inda suka nuna aniyarsu ta isa Makka ta hanyar amfani da hanyoyin tafiye-tafiye irin na tarihi. “Wannan irin tafiya, tana nuna tsantsar ibada ga Ubangiji,” in ji Mamdouh Al Mutairi, shugaban ofishin kan iyakar Al Hadithah, wanda da kansa ya gaishe da mahayan. Zabin mahayan na ratsa hamada da tsaunuka ya nuna yadda mahajjata ke tafiye-tafiyen aikin Hajji kafin fara amfani da ababen jigilar kayayyaki na zamani. Jami’an Saudiyya sun dauki nauyin duk wata buƙatar mahayan ta musamman. Wannan tafiya ta haifar da muhawara a duk duniya game da daidaita al’ada da zamani a cikin ayyukan addini. Kamar yadda sama da mahajjata miliyan 1.8 ke shirin Hajjin 2025, wannan yunkuri ya fito fili a matsayin shaida na dawwama da imani da juriya akan mabiya addinin Musulunci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Artabu Tsakanin ‘Yan Bindiga Da ‘Yan Banga Ya Ci Rayuka Da Dama A Bauchi
  • ‘Yansanda Sun Daƙile Yunƙurin Yin Garkuwa Da Mutane A Katsina
  • ’Yan fashi sun yi wa mafarauta kisan gilla a Bauchi
  • Umaru ’Yar’adua da shugabannin Najeriya da suka rasu a kan mulki
  • Lakurawa: Yadda mafarauta 13 suka gamu da ajalinsu a Sakkwato
  • Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga 3, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace
  • Maniyyata Daga Turai Akan Dawakai Sun Isa Kasar Saudiyya Domin Yin Aikin Hajjin 2025
  • Sojoji sun kama jami’an tsaro da ke haɗa baki da ’yan ta’adda
  • ISWAP sun kai wa sojoji hari a Yobe