Aminiya:
2025-06-20@02:47:35 GMT

’Yan fashi sun kashe matashi a Kano

Published: 5th, May 2025 GMT

Ana fargabar cewa wasu da ake zargin ’yan fashi da makami ne sun kashe wani matashi a unguwar Ɗanbare da ke Ƙaramar Hukumar Kumbotso a Jihar Kano.

Bayanai sun ce waɗanda ake zargin sun kashe matashin ne mai suna Shuaibu Muhammad da adda, bayan sun shiga gidan da yake zaune da nufin sata.

Wani abokin kasuwancinsa, Haruna Nuhu Hussain, ya ce gungun ’yan fashin sun shigo gidan da suke zama a daidai lokacin da suke shirye-shiryen tafiya sallar Asuba.

To sai dai mazauna unguwar sun bayyana wa Aminiya cewa sun samu nasarar kama wanda suke zargin shugaban ’yan fashin ne, sun kuma miƙa shi ofishin ’yan sanda na Ɗorayi.

Kimanin mutum 10 sun bayyana cewa ko a kwanakin nan jagoran ’yan fashin da aka kama ya yi wa wasu mazauna fashi da makami.

Ƙoƙarin jin ta bakin jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya ci tura har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan fashi Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

An Kashe ‘Yan Ta’adda 6,260, An Ceto Mutane 5,365 Acikin Shekaru Biyu – Hedikwatar Tsaro 

Brig.-Gen. Abu-Mawashi ya kara da cewa an kama ‘yan ta’adda 14,138 da sauran masu aikata laifuka yayin da aka ceto mutane 5,365 a cikin wannan lokaci.

 

Abu-Mawashi ya ci gaba da cewa, sojojin sun kwato daruruwan makamai da kuma harsashi da yawa duk acikin wannan lokaci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kashe ‘Yan Ta’adda 6,260, An Ceto Mutane 5,365 Acikin Shekaru Biyu – Hedikwatar Tsaro 
  • Kotu ta ba da belin Natasha kan N50m kan zargin bata sunan Akpabio
  • Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano
  • An ɗaure mutum 7 kan yi wa ɗan sanda rauni a Kano
  • EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana
  • Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 
  • An Kama Mutane 26 Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Kogi
  • Amurka na iya kashe jagoran addini na Iran don mun san inda yake — Trump
  • Yaƙin Iran da Isra’ila: Amurka za ta tura jami’anta don tattaunawa da Tehran
  • Matatar man Isra’ila ta daina aiki bayan sabon harin Iran