Aminiya:
2025-08-04@13:33:26 GMT

’Yan fashi sun kashe matashi a Kano

Published: 5th, May 2025 GMT

Ana fargabar cewa wasu da ake zargin ’yan fashi da makami ne sun kashe wani matashi a unguwar Ɗanbare da ke Ƙaramar Hukumar Kumbotso a Jihar Kano.

Bayanai sun ce waɗanda ake zargin sun kashe matashin ne mai suna Shuaibu Muhammad da adda, bayan sun shiga gidan da yake zaune da nufin sata.

Wani abokin kasuwancinsa, Haruna Nuhu Hussain, ya ce gungun ’yan fashin sun shigo gidan da suke zama a daidai lokacin da suke shirye-shiryen tafiya sallar Asuba.

To sai dai mazauna unguwar sun bayyana wa Aminiya cewa sun samu nasarar kama wanda suke zargin shugaban ’yan fashin ne, sun kuma miƙa shi ofishin ’yan sanda na Ɗorayi.

Kimanin mutum 10 sun bayyana cewa ko a kwanakin nan jagoran ’yan fashin da aka kama ya yi wa wasu mazauna fashi da makami.

Ƙoƙarin jin ta bakin jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya ci tura har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan fashi Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar Hamas Ta Bayyana Cewa Ba za ta Ajiye Makamanta ba Sai Bayan samar Da Kasar falasdinu

Kungiyar Hamas wacce takr iko da Gaza kuma take gwagwarmaya da HKI tun shekara ta 2023 a baya-bayan nan, ta bayyana cewa ba za ta ajiye makamanta ba sai an kafa kasar falasdinu mai zaman kanta, wanda yin watsi ne da bukatar HKI na shafe kungiyar daga doron kasa.

Shafin labarai na Internet Arab News na kasar Saudiya ya nakalto kungiyar tana fadar haka bayan da taron tattaunawa ta tsagaita budewa juna wuta na kwanaki 60 ya tashi baram-baram a birnin Doha na kasar Qatar.

Labarin ya kara da cewa, a ranar Talatan da ta gabata ce, kasashen Qatar da Masar suka amince da ra’ayin samar da kasashe biyu a kan kasar Falasdinu da aka mamaye, a matsayin hanya Tilo ta warware rikicin Falasdinawa da yahudawan HKI, sannan a lokacin ne Hamas zata mika makamanta ga gwamnatin jeka na yika ta Palasdinawa waccea take samun goyon bayan kasashen yamma da kasashen larabawa.

Amma kungiyar Hamas ta amsawa wadannan kasashe kan cewa kungiyar ba zata taba ajiye makamanta ba, sai bayan an kafa kasar Falasdinu mai cikekken yenci da kuma birnin Qudus a matsayin babban birnin Qasar.

HKI tana ganin duk wata yarjeniyar da za’a cimma da Hamas idan bai hada da karbe makamanta b aba abin amincewa ne gareta ba.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kungiyar Hamas Ta Wallafa Hotunan bidiyo Na Fursinan HKI tsare A Gaza August 3, 2025 Sojojin HKI, Daga Jiya Zuwa Yau lahadi Kadai Sun Kashe Falasdinawa 62 August 3, 2025 Pezeskkian Ya Ce: Suna Fatan Musayar Kasuwancin Tsakanin Iran Da Pakistan Ta Haura Dala Biliyan 10 August 2, 2025 Araqchi: Abokantaka Da Ke Tsakanin Iran Da Pakistan Wata babbar Jari Ce Nan Gaba August 2, 2025 Jaridar Isra’ila Ta Ce: Gwamnatin Mamayar Isra’ila Ta Sha Kashi A Yakin Gaza   August 2, 2025 Dakarun Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Da Ke Haramtacciyar Kasar Isra’ila August 2, 2025 Rahoton Majalisar Dinkin Duniya Ya Yi Gargadi Kan Barazanar Kungiyoyin ‘Yan Ta’adda A Afirka August 2, 2025 Shugaba Pezeshkiyan Ya Yi Juyayin Shahadar Haniya Bayan Shekara Guda Da Shahada August 2, 2025 MDD: HKI Ta Kashe Falasdinawa Fiye Da 100 A Cikin Kwanaki 2 A Lokacinda Suka Karban Abinci August 2, 2025 Mutanen Kasar Siriya Sun Fito Zanga-Zanga Yin Allawadai Da Kissan Alawiyya A Kasar August 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara
  • Kungiyar Hamas Ta Bayyana Cewa Ba za ta Ajiye Makamanta ba Sai Bayan samar Da Kasar falasdinu
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji
  • Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya
  • An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo
  • Yadda binciken zargin tallafa wa Boko Haram ke tafiyar hawainiya a Majalisa
  • Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa
  • PDP ta mutu murus a Kano — Shugaban NNPP
  • NBRDA Za Ta Hada Gwiwa Da KIRCT Domin Habaka Magunguna Da Yaki Da Cututtuka
  • Ɗaliban da aka sace a Binuwai sun kuɓuta