Aminiya:
2025-05-05@20:48:54 GMT

’Yan fashi sun kashe matashi a Kano

Published: 5th, May 2025 GMT

Ana fargabar cewa wasu da ake zargin ’yan fashi da makami ne sun kashe wani matashi a unguwar Ɗanbare da ke Ƙaramar Hukumar Kumbotso a Jihar Kano.

Bayanai sun ce waɗanda ake zargin sun kashe matashin ne mai suna Shuaibu Muhammad da adda, bayan sun shiga gidan da yake zaune da nufin sata.

Wani abokin kasuwancinsa, Haruna Nuhu Hussain, ya ce gungun ’yan fashin sun shigo gidan da suke zama a daidai lokacin da suke shirye-shiryen tafiya sallar Asuba.

To sai dai mazauna unguwar sun bayyana wa Aminiya cewa sun samu nasarar kama wanda suke zargin shugaban ’yan fashin ne, sun kuma miƙa shi ofishin ’yan sanda na Ɗorayi.

Kimanin mutum 10 sun bayyana cewa ko a kwanakin nan jagoran ’yan fashin da aka kama ya yi wa wasu mazauna fashi da makami.

Ƙoƙarin jin ta bakin jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya ci tura har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan fashi Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda ’yan fashi suka yi wa mafarauta kisan gilla a Bauchi

’Yan fashi sun harbe mafarauta da fararen hula kimanin 19 har lahira a Karamar Hukumar Alƙaleri ta Jihar Bauchi.

A yayin ziyarar da ya kai wurin, Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Bauchi, Sani-Omolori Aliyu, ya ba da umarnin yin cikakken bincike da kuma tura karin jami’an tsaro yankin.

Mazauna kauyen Mansur sun ce an kashe ’yan farauta guda tara da kuma fararen hula guda goma, kuma an yi jana’izar ’yan bangar a kauyen Mansur kamar yadda addinin Musulunci ya tanada. Amma ’yan sanad da jami’an Ƙaramar Hukumar Alƙaleri ba su ce komai ba kan adadin mamatan ba.

Kakakin ’yan sanda na jihar, CSP Ahmed Mohammed Wakil, ya ce kwamishinan ya tattauna da masu ruwa da tsaki a yankin, inda ya buƙaci jama’a kwantar da hankalinsa, ya kuma kasance a cikin shiri, tare da bai wa ’yan sanda goyon baya wajen gudanar da binciken su.

Kwankwaso: Abba ya mayar wa Baffa Bichi martani Umaru ’Yar’adua da shugabannin Najeriya da suka rasu a kan mulki NAJERIYA A YAU: Abin da ke kai matasan Najeriya ci-rani wasu ƙasashen Afirka

Wakil ya ce, “A ranar 4 ga watan Mayu, 2025 mun samu rahoto cewa tawagar hadin gwiwar mafarauta daga Duguri da Gundumar Gwana, da ke sintiri a kan hanyar Duguri, Mansur, da dajin Madam da ke kan iyakar jihar Bauchi da Filato, sun yi araba da ’yan fashi, inda a arangamar aka kashe mutane da dama daga bangarorin biyu.

“Mun tura tawagar jami’an tsaro wurin, inda suka gano gawarwakin jami’an tsaro da fararen hula daga kauyen Sabuwar Sara, wadanda ’yan fashin suka harbe su a yayin da suke kokarin tserewa daga harin suka mutu.

“Rundunar ta tura tawaga ta musamman domin kamo duk masu alaƙa da wannan aika-aika.”

Ya kuma ba da  tabbacin cewa za a yi bincike cikin gaskiya da adalci domin gurfanar da wadanda suka aikata laifin a gaban ƙuliya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Umarci Ƙananan Hukumomi Da Su Ba Da Gudunmawar Miliyan 670 Domin Siyo Motoci Ga Masarautar Kano
  • Artabu Tsakanin ‘Yan Bindiga Da ‘Yan Banga Ya Ci Rayuka Da Dama A Bauchi
  • ’Yan fashi sun kashe magidanci a Kano
  • Yadda ’yan fashi suka yi wa mafarauta kisan gilla a Bauchi
  • ’Yan fashi sun yi wa mafarauta kisan gilla a Bauchi
  • Kwankwaso: Abba ya mayar wa Baffa Bichi martani
  • Kotu za ta rataye matashi kan kisan karuwa
  • Iran Ta Jaddada Cewa: Kungiyoyin Gwagwarmaya Ba Su Karbar Umarni Daga Wani Bangare, Gashin Kansu Suke Ci
  • Hajjin Bana: Gwamnatin Jigawa ta aika wa NAHCON Naira biliyan 6