Manzon Shugaban Kasar Sin Ya Halarci Bikin Rantsar Da Shugaba Nguema Na Gabon
Published: 5th, May 2025 GMT
Bisa gayyatar da shugaban kasar Gabon Brice Nguema ya yi, Mu Hong, manzon musamman na shugaban kasar Sin Xi Jinping, kuma mataimakin shugaban majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta jama’ar kasar Sin, ya halarci bikin rantsuwar kama aiki na shugaba Nguema, a birnin Libreville na Gabon, a ranar Asabar da ta gabata.
Yayin ganawarsu, Mu Hong ya ce kasar Sin na son karfafa hadin gwiwa tare da kasar Gabon, da daga huldar dake tsakanin kasashen 2 zuwa wani sabon matsayi. A nasa bangare, shugaba Brice Nguema ya ce kasarsa za ta ci gaba da tsayawa kan manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, da kokarin zurfafa hadin kai tare da kasar Sin a bangarori daban daban. (Bello Wang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Yi Alƙawarin Kwato Dazuzzuka Daga Hannun Ƴan Bindiga
Shugaba Bola Tinubu ya yi alƙawarin ƙwato dazuzzuka da sauran yankuna a Arewa-Maso-Yamma da sauran sassan Nijeriya, yayin da yake jawabi a wata liyafa da tsofaffin shugabannin Katsina suka shirya. Ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta ƙara amfani da fasahar sa ido don yaƙar ta’addanci da ƴan fashi.
A cewar sanarwar kakakin shugaban ƙasa, Tinubu ya ce: “Za mu zuba hannun jari a fasaha domin kwato dazuzzuka. Tsaro batu ne na ƙasa baki ɗaya, ba na yanki ko gunduma kawai ba.” Shugaban ya kuma yi alƙawarin inganta filin jirgin sama na Katsina domin samar da ayyukan yi.
Gidauniyar TY Buratai Ta Yi Kira Ga Tinubu Ya Ƙarawa Ma’aikata Albashi Kasar Sin Ta Goyi Bayan Rawar Da Hukumar IAEA Ke Takawa Wajen Warware Batun Nukiliyar Iran Ta Hanyar DiflomasiyyaGwamna Dikko Radda na Katsina ya bayyana cewa jihar ta kafa wani tsarin tsaro na musamman don tattara bayanan sirri, yana mai cewa inganta filin jirgin saman zai samar da ayyukan yi ga mutane 2,700. Tsohon gwamna Aminu Masari ya yaba wa shugaban saboda naɗa ‘yan asalin jihar a muƙamai mabambanta a gwamnatin tarayya.
Tinubu ya kuma yi godiya ga gwamnonin jihohin Kaduna, Jigawa, Borno, Benue, Yobe, Sokoto da Kwara da suka halarci bikin auren ‘yarsa da ƙaddamar da ayyukan gwamnati a Katsina. Ya kuma yaba wa tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari a matsayin mutum mai gaskiya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp