Artabu Tsakanin ‘Yan Bindiga Da ‘Yan Banga Ya Ci Rayuka Da Dama A Bauchi
Published: 5th, May 2025 GMT
An labarto cewa harin ya wakana ne da safiyar ranar Lahadi kuma ‘yan bindigan sun yi awun gaba da shanu da sauran dabbobin al’umman yankin a yayin farmaƙin.
Kazalika, wakilinmu ya gano cewa baya ga ‘yan bijilante da suka rasa rayukansu akwai wasu fararen hula mazauna ƙauyen Sabuwar Sara su ma sun gamu da ajalinsu yayin da suke ƙoƙarin gudun neman tsira bisa harbe-harben ‘yan bindigan.
Sai dai bayanai sun tabbatar da cewa su ma ɓangaren ‘yan fashin dajin sun rasa mutanensu da dama da ake hasashen sun ma fi ‘yan Bangan mutuwa.
Rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta tabbatar da faruwar lamarin, sai dai ba ta bayyana haƙiƙanin adadin mutanen da suka rasa rayukansu a ɓangaren ‘yan Banga da ‘yan fashin ba.
A sanarwar manema labarai da ya fitar a ranar Litinin, kakakin rundunar , CSP Ahmed Mohammed Wakil, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 05:40 a ranar 4 ga watan Mayun 2025, inda aka kai rahoton faruwar hakan ga shalkwatar ‘yansanda da ke Alkaleri da ƙarfe 09:40.
“Haɗakar ƙwararrun mafarauta daga gundumomin Duguri da Gwana a lokacin da suke aikinsu na sintiri a dajin Mansur, da Dajin Mada, iyaka da jihar Bauchi da jihar Filato, kwatsam sai suka ci karo da tawagar ‘yan fashin daji inda suka musu kwantan ɓauna domin farmaƙarsu,” Wakil ya shaida.
Ya ƙara da cewa bisa musayar wuta da aka yi a tsakaninsu, dukkanin ɓangaren sun raunata daga su kansu ‘yan Bijilante da kuma maharan.
Kakakin ya ce an tura jami’an ‘yansanda wurin da abun ya faru inda suka kwaso gawarwakin da aka kashe.
Binciken farko-farko na ‘yansansa shi ma ya tabbatar da cewa waɗanda suka rasu an samesu ne a dukkanin ɓangarorin biyu har ma wasu fararen hula daga ƙauyen Sabuwar Sara lamarin ya shafa a lokacin da suke neman tsira da rayukansu.
Sai dai, rundunar ta ce tunin aka ƙaddamar da bincike domin ganin an kamo ‘yan fashin dajin domin tabbatar da kare rayuka da dukiyar jama’a.
Kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi, CP Sani-Omolori Aliyu, ya yi tur da harin tare da tura jami’ai domin su gana da al’ummar kauyen Mansur domin neman hanyoyin da za a inganta tsaro.
Ya jajanta wa iyalan wadanda aka kashe inda ya ba su tabbacin nema musu adalci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
An Share Filin Noma Kadada 100 Don Karfafa Matasa Su Yi Noma A Babura Jihar Jigawa
Shugaban karamar hukumar Babura ta jihar Jigawa, Malam Hamisu Muhammad Garu, ya kaddamar da shirin karfafa aikin gona da nufin sanya matasa aikin noman shinkafa a wani bangare na kokarin inganta ayyukan yi da samar da abinci a yankin.
Da yake jawabi yayin bikin kaddamar da aikin aka gudanar a garin Babura, shugaban ya bayyana cewa, Gwamna Malam Umar Namadi ne ya bullo da shirin a matsayin wani muhimmin mataki na samar da guraben ayyukan yi ga matasa, da habaka tattalin arzikin kananan hukumomi, da karfafa samar da abinci a fadin jihar.
A cewarsa, gwamnatin jihar ta samar da muhimman kayayyakin amfanin gona da suka hada da takin zamani, magungunan kashe kwari, irin shinkafa mai yawan gaske, da injinan feshi.
Malam Hamisu Garu ya yi nuni da cewa, za a raba kayayyakin ga matasa 200 da aka zabo daga sassa daban-daban na karamar hukumar.
Ya kara da cewa, karamar hukumar ta ware tare da share fili mai fadin hekta 100 domin fara aikin.
Shugaban ya nuna jin dadinsa ga gwamnatin jihar da ta fara shirin.
Ya ce, shirin zai hana matasa yin kaura zuwa birane domin neman ayyukan yi, lamarin da yakan jefa su cikin hatsari da kuma gurgunta makomarsu.
A nasa jawabin, babban daraktan cibiyar bincike ta jiha Dakta Suleman Rufa’i, ya bayyana shirin a matsayin wani kokari na farko, inda ya kara da cewa akwai shirye-shiryen kara fadada shi bisa burin gwamnati na mayar da jihar Jigawa a matsayin jihar da ke kan gaba wajen samar da abinci a Nijeriya.
Rediyon Nijeriya ya ruwaito cewa, sarakunan gargajiya da suka halarci taron sun hada da Hakimin Babura, Sarkin Ban Ringim, Alhaji Muhammad Nata’ala Mustapha, da Hakimin Garu, Dan-makwayon Ringim, Alhaji Suhailu Abubakar Usman, sun yabawa gwamnati kan wannan shiri.
Shugabannin sun bukaci wadanda suka ci gajiyar shirin su nuna kishin kasa da alhaki ta hanyar amfani da tallafin yadda ya kamata domin tabbatar da nasarar shirin.
USMAN MZ/Dutse