Gwamna Fintiri Ba Zai Bar PDP Ba – Humwashi
Published: 5th, May 2025 GMT
Kakakin Gwamnan Jihar Adamawa, Humwashi Wonosikou, ya ƙaryata jita-jitar cewa Gwamna Ahmadu Fintiri na shirin barin jam’iyyar PDP, yana mai cewa shugaban jihar ya cikin jam’iyyar kafada daram.
A wata hira da manema labarai a Yola, Wonosikou ya bayyana cewa Gwamna Fintiri ya mai da hankali kan ayyukansa na shugabancin kwamitin taron jam’iyyar PDP, ba shirin komawa wata jam’iyya ba.
Labarin ya zo ne a lokacin da wasu manyan ‘yan PDP ke komawa jam’iyyar APC, kamar yadda Gwamnan Delta, Sheriff Oborevwori, ya yi tare da tsohon gwamnan jihar Ifeanyi Okowa da dukkan tsarin PDP a jihar.
Shugaban APC, Dr. Abdullahi Ganduje, ya ce jam’iyyarsa tana sa ran samun ƙarin gwamnonin PDP da za su shigo cikinta. Taron ya kuma yi nazari kan nasarorin gwamnatin Fintiri a cikin shekarar 2025.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Adamawa Gwamna Fintiri
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda Jama’a Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
A lokacin dokar ta-ɓaci, Tinubu ya naɗa tsohon Hafsan sojin ruwa, Vice Admiral Ibok-Ete Ibas (mai ritaya), a matsayin wanda zai yi mulki na rikon ƙwarya.
A jawabin bankwana da ya yi da safiyar ranar Alhamis, Ibas ya roƙi ’yan siyasa a jihar su ci gaba da kiyaye zaman lafiya da haɗin kai da gwamnatinsa ta samar a jihar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp