Iran ta watsi da zargin Isra’ila da Amurka cewa ta na da hannu a harin ramuwar gayya na Yemen
Published: 5th, May 2025 GMT
Iran ta yi kakkausar suka da kakkausar murya kan zargin Amurka da da na Isra’ila suka cewa ta na da hannu a hare-haren ramuwar gayya na kasar Yemen.
Iran ta ce zarge zagren basu da tushe balle makama.
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ya fada a yammacin jiya Lahadi cewa, matakin da kasar Yemen ta dauka na goyon bayan al’ummar Falasdinu, wani mataki ne mai cin gashin kansa, wanda aka dauka a matsayin goyan bayan Palasdinawa.
Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya jaddada cewa, sojojin Amurka ne suka shiga yakin domin tallafawa kisan kiyashin da gwamnatin sahyoniyawa ke ci gaba da yi a zirin Gaza.
Don haka Araghchi ya soki Amurka da aikata laifukan yaki ta hanyar kai hare-hare kan ababen more rayuwa da wuraren fararen hula a garuruwan Yemen.
Araghchi ya kira hare-haren da Amurka ta kai kan kasar Yemen a matsayin cin zarafi ga kundin tsarin mulkin Majalisar Dinkin Duniya da muhimman ka’idojin dokokin kasa da kasa.
Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya ci gaba da cewa zargin da ake yi na baya-bayan nan wata dabara ce ta karkatar da hankali daga laifukan da gwamnatin sahyoniyawan ta ke aikatawa a Falastinu, da boye irin gazawar da Isra’ila da kawayenta suka yi a cikin dabarunta, da kuma tabbatar da ci gaba da tada zaune tsaye a yankin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Limamin Sallar Juma’a Ya Ce; Iran Zata Mayar Da Isra’ila Kufai Idan Ta Sake Kai Hari Kan Kasarta
Limamin da ya jagoranci sallar Juma’ar birnin Tehran ya bayyana cewa: Iran za ta mayar da birnin Tel Aviv kufai idan ta maimaita wautar ta
Limamin da ya jagoranci sallar Juma’a a birnin Tehran fadar mulkin kasar Iran, Ayatullah Ahmad Khatami, ya gargadi shugabannin yahudawan sahayoniyya kan illar duk wani keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka cimma, yana mai jaddada cewa: Idan aka sake yin wani wauta, to Iran za ta kaddamar da wani mummunan martani da zai mayar da Tel Aviv garin fatalwa.”
A hudubar sallarsa ta Juma’a a a yau, Ayatullah Khatami ya bayyana cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran ita ce ta yi nasara a yakin wuce gona da iri da aka shafe kwanaki 12 ana yi, yayin da yahudawan sahayoniyya suka kasance mafiya hasara.
Limamin ya yaba da irin jarumtar da al’ummar Iran suka nuna a yakin da aka yi a baya-bayan nan, inda ya tunatar da shahadar manyan kwamandojin soji da masana kimiyyar nukiliya. Ya mai nanata cewa: Iran ba zata rushe ba, kuma ba za a taba yin nasara kanta ba, da yardan Allah, amma za ta ci gaba da tsayawa tsayin daka da alfahari duk da irin makircin da ake kullawa kanta.
Ayatullah Khatami ya kara da cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta tabbatar da karfinta a lokacin da ta kai hari kan sansanonin Amurka irin su Ain al-Assad da Udeid da makamai masu linzami, inda ta kasance kasa daya tilo tun bayan yakin duniya na biyu da ta kai wa Amurka hari sau biyu.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasar Slovenia Da Haramta Tura Makamai Zuwa Haramtacciyar Kasar Isra’ila August 1, 2025 Kasar Spain Ta Bayyana Abin Da Ke Faruwa A Gaza A Matsayin Abin Kunya Ga Bil’Adama August 1, 2025 Iran ta yi watsi da zargin gwamnatocin turai na yunkurin kashe wasu mutane a kasashensu August 1, 2025 Mali da Rasha sun tattauna kan hadin gwiwar makamashi August 1, 2025 Afirka ta Kudu na shirin daukar matakan kauce wa tasirin harajin Amurka August 1, 2025 Haaretz: Sojojin Isra’ila 7 ne suka kashe kansu a watan Yuli August 1, 2025 Gaza: Mutane Da Dama Sun Yi Shahada A Yau Wasu Kuma Sun Jikkata August 1, 2025 Kungiyar AU Ta Yi Watsi Da Kafa Gwamnatin Adawa Da Kungiyar RSF Ta Yi A Sudan August 1, 2025 Shugaban Kasar Iran Zai Ziyarci Pakistan A Gobe Asabar August 1, 2025 Habasha Ta Kaddamar Da Shirin Shuka Bishiyoyi Miliyan 700 A Rana Daya August 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci