Iran ta watsi da zargin Isra’ila da Amurka cewa ta na da hannu a harin ramuwar gayya na Yemen
Published: 5th, May 2025 GMT
Iran ta yi kakkausar suka da kakkausar murya kan zargin Amurka da da na Isra’ila suka cewa ta na da hannu a hare-haren ramuwar gayya na kasar Yemen.
Iran ta ce zarge zagren basu da tushe balle makama.
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ya fada a yammacin jiya Lahadi cewa, matakin da kasar Yemen ta dauka na goyon bayan al’ummar Falasdinu, wani mataki ne mai cin gashin kansa, wanda aka dauka a matsayin goyan bayan Palasdinawa.
Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya jaddada cewa, sojojin Amurka ne suka shiga yakin domin tallafawa kisan kiyashin da gwamnatin sahyoniyawa ke ci gaba da yi a zirin Gaza.
Don haka Araghchi ya soki Amurka da aikata laifukan yaki ta hanyar kai hare-hare kan ababen more rayuwa da wuraren fararen hula a garuruwan Yemen.
Araghchi ya kira hare-haren da Amurka ta kai kan kasar Yemen a matsayin cin zarafi ga kundin tsarin mulkin Majalisar Dinkin Duniya da muhimman ka’idojin dokokin kasa da kasa.
Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya ci gaba da cewa zargin da ake yi na baya-bayan nan wata dabara ce ta karkatar da hankali daga laifukan da gwamnatin sahyoniyawan ta ke aikatawa a Falastinu, da boye irin gazawar da Isra’ila da kawayenta suka yi a cikin dabarunta, da kuma tabbatar da ci gaba da tada zaune tsaye a yankin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Za mu iya galaba kan Iran ko babu Amurka — Isra’ila
Shugaban Isra’ila, Isaac Herzog, ya bayyana cewa ƙasarsa za ta iya samun nasara a yaƙin da take yi da Iran ko da kuwa Amurka ba ta shigar mata ba.
Sai dai Herzog ya shaida wa ABC News cewa kawar da barazanar nukiliyar Iran yana da muhimmanci ga “duniya mai ’yanci”, ciki har da Amurka.
Nan da mako biyu za mu yanke shawara kan shigar wa Isra’ila yaƙi — Trump Muna shawartar Trump kada ya shiga yaƙin Iran da Isra’ila — BirtaniyaDa yake amsa tambayar ko me zai ce dangane da yiwuwar shigar wa ƙasarsa yaƙin da take yi da Iran da Shugaba Donald Trump ya yi iƙirari, Herzog ya ce “ina da cikakkiyar yarda a kan duk wani hukunci da zai yanke kuma ina da tabbacin duk abin da ya yanke shi ne daidai.
Herzog ya ce mako guda ke nan da fara yaƙin amma ya tabbatar da cewa barazanar Iran ba za ta kau ba nan take.
“Babbar nasarar da za mu samu ita ce kawo ƙarshen barazanar nukiliyar Iran,” a cewar Herzog.
“[Jagoran addini na Iran, Ayotallah Ali Khamenei] shi ne kan macijin da ke jagorantar duk wata barazana da Iran take yi da muke buƙatar mu sare.
“Tun ba yanzu ba yake babatun ganin bayan ƙasarmu da al’ummarta. Saboda haka ba mu da wata manufa a yanzu face mun yi maganinsa,” kamar yadda Herzog ya shaida wa gidan talabijin na ABC.