Iran ta watsi da zargin Isra’ila da Amurka cewa ta na da hannu a harin ramuwar gayya na Yemen
Published: 5th, May 2025 GMT
Iran ta yi kakkausar suka da kakkausar murya kan zargin Amurka da da na Isra’ila suka cewa ta na da hannu a hare-haren ramuwar gayya na kasar Yemen.
Iran ta ce zarge zagren basu da tushe balle makama.
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ya fada a yammacin jiya Lahadi cewa, matakin da kasar Yemen ta dauka na goyon bayan al’ummar Falasdinu, wani mataki ne mai cin gashin kansa, wanda aka dauka a matsayin goyan bayan Palasdinawa.
Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya jaddada cewa, sojojin Amurka ne suka shiga yakin domin tallafawa kisan kiyashin da gwamnatin sahyoniyawa ke ci gaba da yi a zirin Gaza.
Don haka Araghchi ya soki Amurka da aikata laifukan yaki ta hanyar kai hare-hare kan ababen more rayuwa da wuraren fararen hula a garuruwan Yemen.
Araghchi ya kira hare-haren da Amurka ta kai kan kasar Yemen a matsayin cin zarafi ga kundin tsarin mulkin Majalisar Dinkin Duniya da muhimman ka’idojin dokokin kasa da kasa.
Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya ci gaba da cewa zargin da ake yi na baya-bayan nan wata dabara ce ta karkatar da hankali daga laifukan da gwamnatin sahyoniyawan ta ke aikatawa a Falastinu, da boye irin gazawar da Isra’ila da kawayenta suka yi a cikin dabarunta, da kuma tabbatar da ci gaba da tada zaune tsaye a yankin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Jaddada Cewa: Kungiyoyin Gwagwarmaya Ba Su Karbar Umarni Daga Wani Bangare, Gashin Kansu Suke Ci
Iran ta mayar da martani kan zargin da ake mata game da alakar ta da Yemen tana cewa; Taimakon da Yemen ke yi wa Falasdinu hukunci ne mai cin gashin kansa
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta fitar da wata sanarwa dangane da zargin da ake yi wa Iran dangane da alakar da ke tsakaninta da kasar Yemen, inda ta yi la’akari da wadannan tuhume-tuhumen a matsayin maimaita zargin karya da nufin karkatar da hankali daga laifukan yahudawan sahayoniyya ‘yan mamaya.
A sanarwar da ma’aikatar harkokin wajen kasar ta fitar ta ce: Wadannan tuhume-tuhume ne da maimaita zarge-zargen karya da ke alakanta matakan gwagwarmaya da al’ummar Yemen suka dauka na kare kansu da kuma goyon bayan al’ummar Falastinu ga Iran. Wannan cin mutunci ne ga al’umma masu yakar zalunci.
Sanarwar ta kara da cewa: Amurka ta hanyar goyon bayan kisan kiyashin da yahudawan sahayoniyya suke yi, ita ce ta shiga yakin da take yi da al’ummar kasar Yemen, kuma tana aikata laifukan yaki ta hanyar kai hare-hare kan ababen more rayuwa da farar hula a garuruwa daban-daban na kasar ta Yamen. Harkar Yemen na goyon bayan Falasdinawa wani mataki ne mai cin gashin kansa, wanda ya samo asali daga zurfin jin kai da kuma fahimtar Musulunci na hadin kai da al’ummar Falasdinu da ke da alhakin wannan mataki na Iran.