Ministan Tsaron kasar Iran ya jaddada cewa: Za su mayar da martani mai tsanani da karfi kan duk wani ta’addanci da kasarsu za ta fuskanta

Ministan tsaron kasar Iran Birgediya Janar Aziz Nasirzadeh, yayin da yake mayar da martani ga barazanar Amurka, ya tabbatar da cewa Iran za ta mayar da martani mai karfi tare da kai hare-hare kan dukkanin wasu muradun Amurka da sansanoninta da suke wannan yankin.

Birgediya Janar Nasirzadeh ya kara da cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana da tarin makamai masu linzami, kuma idan aka kakaba mata yaki, to za ta yi amfani da su ba tare da bata lokaci ba, ko kuma a duk kan muradun makiya.

Ministan ya jaddada cewa: “Ba su da wata kiyayya da kasashe makwabta, amma tabbas idan sansanonin Amurka suka kai hari kan Iran, to lallai muradintaa duk inda suke zasu fuskancin hare-haren daukan fansa,” yana mai cewa: Makami mai linzami na Qasem Basir yana da juriya a fagen yakin na’ura mai kwakwalwa kuma yana iya ketare tsarin makamai masu linzami.”

Ya bayyana cewa: “makamin na Qasem Basir yana da saukin sarrafawa tare da cimma wurin da aka harba shi a kowane yanayi saboda sabon tsarin ci gaban da ya samu da kuma yadda aka sarrafa jikin sa da sinadarin carbon fiber, wanda ke kubuta daga makamai masu linzami da na’urorin radar.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 Yemen Ta Kai Wa HKI Hari Da Makami Mai Linzami  Na  “Falasdinu 2”

Sojojin kasar ta Yemen sun sanar da kai wa yankin  Yafa hari da makami mai linzami da ya fi sauti sauri mai suna ” Falasdinu 2″, tare da tabbatar da cewa, ya fada inda aka harba shi.

A yau Asabar ne dai sojojin na Yemen su ka kai wa HKI harin da makami mai linzami mai tsananin sauri bisa abinda su ka kira da cewa; Mayar da martani ne akan ci gaba da yakin da yakin da ‘yan sahayoniya suke ci gaba da kai wa Gaza, da kuma jefa yankin cikin yunwa.

Kakakin sojan kasar Yemen, janar Yahya Sari, ya bayyana cewa; Makami mai linzamin da aka yi amfani da shi sunashi; “Falasdinu 2” kuma ya isa inda aka harba shi.

Janar Yahya Sari ya kuma ce: Dukkanin al’ummar musulmi ne suke da alhakin yin shiru akan abinda yake faruwa a Gaza, da kuma kin taimaka musu, sannan kuma ya ce: Ko ba dade-ko bajima, samamakon  yin shiru akan wuce gona da irin ‘yan sahayoniya zai isa cikin sauran kasashe.”

Janar Sari ya kuma ce; Gaza, tana kare dukkanin al’umma ne a wannan lokacin, domin taimaka mata shi ne ya fi dacewa da a tsumayi lokacin da sharri zai isa gidan kowa.”

Da safiyar yau Asabar ne dai  jiniyar gargadi ta kada a yankuna da yawa na HKI da su ka hada yankin Kudus, Tel Aviv da kuma ” “Dead Sea” bayan da aka harbo makami mai linzami daga kasar ta Yemen.

Makamin na dazu dai ne karo na uku da sojojin Yemen su ka harba a cikin sa’o’i 24.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Jaddada Cewa: Kungiyoyin Gwagwarmaya Ba Su Karbar Umarni Daga Wani Bangare, Gashin Kansu Suke Ci
  • Gwamna Abba Kabir Ya Mayar Wa Da Bappa Bichi Martani
  • Wani harin makami mai linzami daga Yemen ya fada filin jirgin saman Ben Gurion na Isra’ila
  • Kasar Yemen Ta Kakaba Takunkumi Kan Amurka A harkokin Fitar Da Man Fetur Din Kasarta
  • Pakistan Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Mai Cin Tazarar Kilo Mita Fiye Da 400
  •  Yemen Ta Kai Wa HKI Hari Da Makami Mai Linzami  Na  “Falasdinu 2”
  • Araghchi : Duk wani ci gaba ya dogara da muhimmancin da Washington za ta ba tattauwar  
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Tattauna Da Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya Kan Zaman Tattaunawan Amurka Da Iran
  • Iran Ta Ce Ba Zata Amince Da Barazana Da Kuma Takurawa A Lokaci Guda Da Tattaunawa ba