Kasar Iran Zata Mayar Da Martani Mai Tsanani Kan Duk Wani Hari Da Zata Fuskanta Daga Makiya
Published: 5th, May 2025 GMT
Ministan Tsaron kasar Iran ya jaddada cewa: Za su mayar da martani mai tsanani da karfi kan duk wani ta’addanci da kasarsu za ta fuskanta
Ministan tsaron kasar Iran Birgediya Janar Aziz Nasirzadeh, yayin da yake mayar da martani ga barazanar Amurka, ya tabbatar da cewa Iran za ta mayar da martani mai karfi tare da kai hare-hare kan dukkanin wasu muradun Amurka da sansanoninta da suke wannan yankin.
Birgediya Janar Nasirzadeh ya kara da cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana da tarin makamai masu linzami, kuma idan aka kakaba mata yaki, to za ta yi amfani da su ba tare da bata lokaci ba, ko kuma a duk kan muradun makiya.
Ministan ya jaddada cewa: “Ba su da wata kiyayya da kasashe makwabta, amma tabbas idan sansanonin Amurka suka kai hari kan Iran, to lallai muradintaa duk inda suke zasu fuskancin hare-haren daukan fansa,” yana mai cewa: Makami mai linzami na Qasem Basir yana da juriya a fagen yakin na’ura mai kwakwalwa kuma yana iya ketare tsarin makamai masu linzami.”
Ya bayyana cewa: “makamin na Qasem Basir yana da saukin sarrafawa tare da cimma wurin da aka harba shi a kowane yanayi saboda sabon tsarin ci gaban da ya samu da kuma yadda aka sarrafa jikin sa da sinadarin carbon fiber, wanda ke kubuta daga makamai masu linzami da na’urorin radar.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Iran Ta Sauke Hakkin Da Ya Hau Kanta Sauran Bangaren Turai
Ministan harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Iran ta cika hakkinta, yanzu kuma turai ne ake jiran ta cika nata hakkokin
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya jaddada cewa, a wani mataki da Iran ta dauka na nauyin shiga tattaunawa da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA, domin tsara wani sabon daftarin aiki mai ma’ana kan yadda za a aiwatar da alkawuran da ta dauka na kare hakkokin da suka hau kanta, yanzu kuma ana jiran Turai ta cika nata alkawuran.
A wata tattaunawa ta wayar tarho tare da ministocin harkokin wajen Faransa, Jamus, da Birtaniya, da kuma jami’in kula da harkokin waje na EU, Araqchi ya ce: “Dole ne sauran bangarorin su yi amfani da wannan damar wajen ci gaba da gudanar da harkokin diflomasiyya don kaucewa rikicin da za a iya afkawa, da kuma nuna muhimmancinsu wajen neman hanyar diflomasiyya da kuma imanin da suke da shi na samar da mafita ta hanyar zaman lafiya.”
Araqchi ya yi nuni da cewa yunkurin da kungiyar kasashen Turai Troika ke yi na mayar da takunkumin da Majalisar Dinkin Duniya ta kakabawa Iran ba shi da wata ka’ida ta doka ko ta dabi’a, yana mai jaddada cewa kiyaye yanayin tattaunawa da diflomasiyya yana da matukar muhimmanci don kaucewa tabarbarewar lamarin.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Masu Goyon Bayan Isra’ila Suna Da Hannu A Laifukanta September 18, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Cika Kwanaki 713 Suna Kisan Kiyashi A Zirin Gaza September 18, 2025 Harin Makami Mai Linzami Yemen Ya Tilastawa Jirgin Fira Ministan Gwamnatin Isra’ila Saukar Gaggawa September 18, 2025 Eslami: Dole ne IAEA ta zama mai cikakken ‘yancin cin gashin kai September 18, 2025 Rahoto: An yi tattaunawa mai tsawo tsakanin Syria da Isra’ila a Landan September 18, 2025 Sheikh Qassem: Harin Pager jarabawa ce wadda ta kara wa masu gwagwarmaya kwarin gwiwa September 18, 2025 Pezeshkian: Iran da Masar suna da tsohon tarihi a duniya September 18, 2025 Iran ta samu Zinariya, Azurfa, da Tagulla a Gasar Kokawa ta Duniya September 18, 2025 Iran Ta Yi Nasarar Gwajin Tauraron Dan’adam Da Zai Samar Da “Internet” Ga Yankunan Karkara September 17, 2025 Za A Kada Kuri’ar Raba Gardama Akan Sabon Tsarin Mulki A Kasar Guinea September 17, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci