Kasar Iran Zata Mayar Da Martani Mai Tsanani Kan Duk Wani Hari Da Zata Fuskanta Daga Makiya
Published: 5th, May 2025 GMT
Ministan Tsaron kasar Iran ya jaddada cewa: Za su mayar da martani mai tsanani da karfi kan duk wani ta’addanci da kasarsu za ta fuskanta
Ministan tsaron kasar Iran Birgediya Janar Aziz Nasirzadeh, yayin da yake mayar da martani ga barazanar Amurka, ya tabbatar da cewa Iran za ta mayar da martani mai karfi tare da kai hare-hare kan dukkanin wasu muradun Amurka da sansanoninta da suke wannan yankin.
Birgediya Janar Nasirzadeh ya kara da cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana da tarin makamai masu linzami, kuma idan aka kakaba mata yaki, to za ta yi amfani da su ba tare da bata lokaci ba, ko kuma a duk kan muradun makiya.
Ministan ya jaddada cewa: “Ba su da wata kiyayya da kasashe makwabta, amma tabbas idan sansanonin Amurka suka kai hari kan Iran, to lallai muradintaa duk inda suke zasu fuskancin hare-haren daukan fansa,” yana mai cewa: Makami mai linzami na Qasem Basir yana da juriya a fagen yakin na’ura mai kwakwalwa kuma yana iya ketare tsarin makamai masu linzami.”
Ya bayyana cewa: “makamin na Qasem Basir yana da saukin sarrafawa tare da cimma wurin da aka harba shi a kowane yanayi saboda sabon tsarin ci gaban da ya samu da kuma yadda aka sarrafa jikin sa da sinadarin carbon fiber, wanda ke kubuta daga makamai masu linzami da na’urorin radar.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Firayim Ministan Senegal Ya Bayyana Sabon Shirin Farfado Da Tattalin Arzikin Kasar
Firayim Ministan Senegal Ousmane Sonko ya sanar da wani sabon shirin farfado da tattalin arzikin kasar, inda ya yi alkawarin samar da kudi “90% na aiwatar da wanann shirin ta hanyar albarkatun cikin gida da kuma kauce wa karbar bashi.
Sonko ya bayyana haka ne a lokacin da ake gabatar da wannan shiri a Dakar babban birnin kasar, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito. Ya ce: “Za mu nemi haɗin kan abokan hulɗa na waje ne kawai a ɓangaren sake amfani da kadarorinmu na cikin gida.”
Ya kara da cewa “dole ne a yi amfani da kuma tattara albarkatun cikin gida don samar da mafi yawan kudaden da kasa take bukata.”
Shirin wanda ke da nufin daidaita harkokin kudi na kasar da ke yammacin Afirka, wadda ta fara hako mai da iskar gas a bara, ya zo ne a daidai lokacin da Senegal ke fuskantar kalubalen kudi da kuma tarin basusuka.
Kasar Senegal dai na fama da boyayyen bashi na biliyoyin daloli daga gwamnatin da ta shude, lamarin da ya sanya hukumar lamuni ta duniya IMF ta dakatar da shirinta na lamuni ga Senegal.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Gaza: Witfkoff ya yi rangadi a wuraren da Amurka ta kafa domin tallafi August 2, 2025 ‘Yan Sudan dama na komawa gida bayan gudun hijira na tsawon shekaru a Masar August 2, 2025 Iran Ta Ce Batun Neman Dakatar Da Tace Uranium Zai Rusa Duk Wata Jarjejeniya Da Ake Son Cimmawa August 1, 2025 Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Yi Watsi Da Duk Wani Zarge-Zargen Neman Bata Mata Suna August 1, 2025 Limamin Sallar Juma’a Ya Ce; Iran Zata Mayar Da Isra’ila Kufai Idan Ta Sake Kai Hari Kan Kasarta August 1, 2025 Kasar Slovenia Da Haramta Tura Makamai Zuwa Haramtacciyar Kasar Isra’ila August 1, 2025 Kasar Spain Ta Bayyana Abin Da Ke Faruwa A Gaza A Matsayin Abin Kunya Ga Bil’Adama August 1, 2025 Iran ta yi watsi da zargin gwamnatocin turai na yunkurin kashe wasu mutane a kasashensu August 1, 2025 Mali da Rasha sun tattauna kan hadin gwiwar makamashi August 1, 2025 Afirka ta Kudu na shirin daukar matakan kauce wa tasirin harajin Amurka August 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci