Bai wa ’yan bindiga kuɗin fansa na dagula sha’anin tsaro — Ribadu
Published: 9th, April 2025 GMT
Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Sha’anin Tsaro, Nuhu Ribadu, ya roƙi ’yan Najeriya da su daina biyan ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane kuɗin fansa.
Ribadu, ya ce biyan kuɗin fansa ba ya sa ana sakin waɗanda aka sace, kuma hakan na ƙara dagula al’amuran tsaro.
Harajin China da Amurka: Mece ce makomar tattalin arziƙin duniya? Za a ci gaba da sayar da ɗanyen mai a farashin Naira — GwamnatiRibadu ya bayyana haka ne a ranar Talata a Abuja, yayin da yake karɓar mutane 64 da dakarun tsaro suka ceto daga hannun masu garkuwa da su a Zangon Kataf da ke Kudancin Kaduna.
“Don Allah ku daina bai wa waɗannan mutane (masu garkuwa) kuɗi, wannan shi ne babban ƙalubalen da muke fuskanta,” in ji Ribadu.
“Da yawa daga cikin iyalan waɗannan mutanen sun riga sun biya kuɗin fansa, amma hakan bai sa an sako su ba. Mu ne jami’an tsaro muka kuɓutar da su.”
Ya ƙara da cewa: “Ba kuɗin da ake ba su ne ke kawo sakamakon da ake so ba.
“Waɗannan mutanen, duk lokacin da kuka ba su kuɗi, sai su ƙara inganta aikinsu.
“Ba mu taɓa bai wa kowa ko sisin kwabo ba, kuma ba ma son mutane su ci gaba da yin hakan.”
Ribadu, ya ce ci gaban da aka samu wajen ceto waɗanda aka sace ya samu ne sakamakon jajircewar dakarun soji da sauran hukumomin tsaro.
“Ina matuƙar yaba wa dakarunmu da hukumomin tsaro. Jajircewarsu wajen bin diddigin waɗannan miyagu shi ne dalilin da ya sa muke a nan yau,” in ji Ribadu.
“Saboda jajircewar Shugaban Ƙasa, kullum muna samun ci gaba. Amma sako waɗanda aka kama ba shi ne ƙarshen wannan abu ba.
“Za mu ci gaba da bin diddigin waɗannan ’yan ta’adda har sai sun fuskanci hukunci.”
Mutum 64 da aka ceto sun kwashe sama da wata guda a hannun waɗanda suka sace su.
Daga cikinsu akwai mataimakin darakta a ma’aikatar gwamnati da kuma wani ɗan uwan Bishop Matthew Hassan Kukah na cocin Katolika da ke Jihar Sakkwato.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu
Rundunar ‘yan sandan jihar Neja ta saki tare da hada wadanda aka yi garkuwa da su talatin da biyar tare da iyalansu.
Sun kunshi mata goma sha shida da yara goma sha tara daga Kagara, Tegina da Agwara, bayan sun shafe makonni a hannun ‘yan sanda da ke tsare da kuma kawar da hankalinsu daga barayin da ke Minna.
Kwamishinan ‘yan sanda mai kula da jihar Neja Adamu Abdullahi Elleman ya bayyana haka a lokacin wani takaitaccen bayani da ya mikawa shugaban karamar hukumar gidan rediyon Ayuba Usman Katako a Minna.
Kwamishinan ‘yan sandan wanda mataimakin kwamishinan ‘yan sanda Ibrahim Adamu ya wakilta, ya bayyana cewa za’a sake haduwa da wadanda abin ya shafa da iyalansu domin sun kasance karkashin kulawar ‘yan sanda tare da tallafi da kulawar da suka dace daga gwamnatin jihar Neja.
A cewarsa, hakan ya fara ne a ranar 3 ga watan Yulin 2025 lokacin da aka samu labari daga wata majiya mai tushe da ke nuna cewa wadanda abin ya shafa na kaura daga Birnin-Gwari a jihar Kaduna zuwa wasu yankuna.
Jami’an ‘yan sanda sun yi kaca-kaca da rukunin farko na st Agwara a kokarin da suke na tsallakawa kogin zuwa wasu kauyukan New-Bussa na jihar Neja tare da ceto mata biyar da kananan yara shida.
A yayin da ake gudanar da tambayoyi, an bayyana cewa ‘yan bindigar na yin kaura daga Birnin-Gwari zuwa wasu unguwanni kuma rundunar ‘yan sandan da ke aiki a hanyar Mekujeri zuwa Tegina ta cafke kashi na biyu tare da mata hudu da kananan yara bakwai, yayin da kuma aka kama wani rukunin tare da direban da ya tafi da su.
Bincike ya nuna cewa direban, Yusuf Abdullahi na Birnin-Gwari ya je sansaninsu ne domin kai mutanen da abin ya shafa, kuma yana kan bincike don tabbatar da hadin gwiwarsa a ayyukansu.
Kwamishinan ‘yan sandan, Adamu Abdullahi Elleman, ya tabbatar da cewa tun da aka tsare wadanda abin ya shafa, an ba su wasu shawarwari da nasiha, da abinci da kuma kayan kwanciya.
Ya kara da cewa, bayan samun takardar izinin da ya kamata, ana mika wadanda abin ya shafa ga shugaban karamar hukumar da ‘yan uwansu tare da yin kira ga jama’a da su baiwa ‘yan sanda bayanan da suka dace a duk lokacin da aka lura da al’amura domin gaggauta shiga tsakani.
PR ALIYU LAWAL.