Bai wa ’yan bindiga kuɗin fansa na dagula sha’anin tsaro — Ribadu
Published: 9th, April 2025 GMT
Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Sha’anin Tsaro, Nuhu Ribadu, ya roƙi ’yan Najeriya da su daina biyan ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane kuɗin fansa.
Ribadu, ya ce biyan kuɗin fansa ba ya sa ana sakin waɗanda aka sace, kuma hakan na ƙara dagula al’amuran tsaro.
Harajin China da Amurka: Mece ce makomar tattalin arziƙin duniya? Za a ci gaba da sayar da ɗanyen mai a farashin Naira — GwamnatiRibadu ya bayyana haka ne a ranar Talata a Abuja, yayin da yake karɓar mutane 64 da dakarun tsaro suka ceto daga hannun masu garkuwa da su a Zangon Kataf da ke Kudancin Kaduna.
“Don Allah ku daina bai wa waɗannan mutane (masu garkuwa) kuɗi, wannan shi ne babban ƙalubalen da muke fuskanta,” in ji Ribadu.
“Da yawa daga cikin iyalan waɗannan mutanen sun riga sun biya kuɗin fansa, amma hakan bai sa an sako su ba. Mu ne jami’an tsaro muka kuɓutar da su.”
Ya ƙara da cewa: “Ba kuɗin da ake ba su ne ke kawo sakamakon da ake so ba.
“Waɗannan mutanen, duk lokacin da kuka ba su kuɗi, sai su ƙara inganta aikinsu.
“Ba mu taɓa bai wa kowa ko sisin kwabo ba, kuma ba ma son mutane su ci gaba da yin hakan.”
Ribadu, ya ce ci gaban da aka samu wajen ceto waɗanda aka sace ya samu ne sakamakon jajircewar dakarun soji da sauran hukumomin tsaro.
“Ina matuƙar yaba wa dakarunmu da hukumomin tsaro. Jajircewarsu wajen bin diddigin waɗannan miyagu shi ne dalilin da ya sa muke a nan yau,” in ji Ribadu.
“Saboda jajircewar Shugaban Ƙasa, kullum muna samun ci gaba. Amma sako waɗanda aka kama ba shi ne ƙarshen wannan abu ba.
“Za mu ci gaba da bin diddigin waɗannan ’yan ta’adda har sai sun fuskanci hukunci.”
Mutum 64 da aka ceto sun kwashe sama da wata guda a hannun waɗanda suka sace su.
Daga cikinsu akwai mataimakin darakta a ma’aikatar gwamnati da kuma wani ɗan uwan Bishop Matthew Hassan Kukah na cocin Katolika da ke Jihar Sakkwato.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Birgediya Pakphur: Nan Gaba Kadan Za A Budewa “Isra’ila” Kofofin Jahannama
Sabon kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci na Iran Birgadiya Muhammad Pakphur ya aike wa da jagoran juyin musulunci na Iran wasika da a ciki ya bayyana cewa:
” Laifukan ta’addanci da HKI ta aikata, wanda ya yi sanadiyyar shahadar manyan kwamandojin da kuma malaman Nukiliya, haka nan mata da kananan yara da ba su ji ba su gani ba, ba zai wuce ba tare da mayar da martani ba.”
Bugu da kari sabon kwamandan dakarun kare juyin musuluncin ya ce; Ba da jimawa ba, Za a buwa wa wannan haramtacciyar kasa kofofin jahannama.”
Birgeriya Muhamad Pakphur ya kuma kaddamar da ta’aziyya da kuma taya murnar shahadar kwamandojin, ya kuma yi godiya ga jagora da ya gaskata dakarun juyin.
Har ila yau Birgediya Pakphur Muhammad ya ce; Abinda ‘yan sahayoniyar su ka yi, wuce gona da iri ne da keta hurumin tsaron kasar Iran da zaman lafiyar jamhuriyar ta Iran, don haka ba zai wuce ba tare da mayar da martani ba.
Haka nan kuma ya ce: Kamar yadda jagoran juyin musulunci na Iran ya yi alkawali, wannan haramtacciyar kasar za ta fuskanci bakar makomarta da kuma mummunan sakamako.”
Wani sashe na wasikar sabon kwamandan dakarun kare juyin musuluncin na Iran ya kunshi cewa; Bisa dogaro da Allah, da kuma cika alkawalin da jagora ya yi, sannan kuma da daukar fansar jinanen shahidai kwamandoji, da masana da ‘yan kasa da ba su ji ba su gani ba, za a buewa wannan haramtacciyar kasa kofofin jahannama ba da jimawa ba.”