HausaTv:
2025-08-04@13:30:01 GMT

Iran da Saudiyya sun jaddada bukatar kare hurimin kasar Siriya

Published: 5th, May 2025 GMT

Kasashen Iran da kuma Saudiyya sun jaddada kiran su na ganin an kare hurumin kasar Siriya tare kuma da yin tir da hare-haren da Isra’ila ke kai wa kasar.

Jami’an Iran da Saudiyya sun tabbatar da aniyarsu ta tabbatar da ‘yancin kai da kuma ‘yancin yankin Siriya, tare da yin Allah wadai da harin da sojojin Isra’ila suka kai kan al’ummar kasar Larabawar.

An bayyana hakan ne a wata ganawa da aka yi a ranar Lahadi a birnin Riyadh tsakanin Mohammad-Reza Raouf Sheibani, wakilin Iran na musamman kan Syria, da Saud al-Sati, mataimakin ministan harkokin wajen Saudiyya kan harkokin siyasa, a yayin da suke magana kan yadda ake samun sauyin yanayi a kasar Siriya, da kuma mafi girman tasirin hare-haren da Isra’ila ke kaiwa a yankin.

M. Sheibani ya sake jaddada goyon bayan Iran ga hadin kai da ‘yancin kai na Siriya, yana mai yin tir da hare-haren da gwamnatin Isra’ila ke kai wa a matsayin barna da kuma tada zaune tsaye.

Ya jaddada cewa irin wadannan ayyuka na kawo cikas ga zaman lafiyar yankin da kuma saba ka’idojin kasa da kasa.

A nasa bangaren, al-Sati ya yi na’am da wannan ra’ayi, yana mai tabbatar da daidaiton matsayin Saudiyya na goyon bayan tabbatar da yankin Siriya, zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Ya yi Allah wadai da hare-haren da gwamnatin kasar ke kai wa a yankin na Syria, yana mai bayyana bukatar bin dokokin kasa da kasa da mutunta ikon kasa a duniya.

Bangarorin biyu sun amince da muhimmancin ci gaba da tuntubar juna dangane da ci gaban yankin, tare da jaddada bukatar yin hadin gwiwadon tinkarar kalubalen da ake fuskanta.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: hare haren da tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Har yanzu ana fama da cutar kwalara a Najeriya – UNICEF

Asusun kula da Ƙananan Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya, UNICEF, ya ce Najeriya ce ƙasa ta biyu da aka fi samun ɓullar cutar kwalara a yammacin Afirka da tsakiyar Afirka.

Darektan Hukumar UNICEF mai kula da yammacin Afirka da Afirka ta tsakiya, Gilles Fagninou  ne ya bayyana hakan tare da cewar annobar kwalara ta zama tamfar alaƙaƙai a Najeriya.

Haɗarin tirela ya yi sanadin asarar awaki sama da 100 a Zariya Martani: Har yanzu muna ci gaba da yajin aiki — Ma’aikatan jinya  

“A cewarsa cutar Kwalara na ci gaba da yaɗuwa a Najeriya, inda ƙasar ke fama da ɓarkewar cutar a ‘yan shekarun nan.”

“Ya zuwa ƙarshen watan Yuni, Najeriya ta samu adadin mutane 3,109 da ake zargin sun kamu da cutar kwalara da kuma mutuwar mutane 86 a cikin jihohi 34,” in ji Fagninou.

Jami’in na Majalisar Ɗinkin Duniya ya ƙara da cewa, wannan adadi ya sanya Najeriya ta zama ƙasa ta biyu da cutar ta fi ƙamari a yankin yammacin Afirka da Afirka ta tsakiya kamar yadda aka ambata a baya.

Ya yi nuni da cewa ɓarkewar cutar kwalara a yankin yammaci da Afirka ta Tsakiyar ta haifar da matsala ga yara.

Ya ce, an ƙiyasta kimanin yara 80,000 na fuskantar barazanar kamuwa da cutar kwalara a yammacin Afirka da Afirka ta Tsakiya yayin da aka fara damina a faɗin yankin.

A cewarsa, ruwan sama kamar da bakin kwarya da yawaitar ambaliya da kuma yawan matsugunan su na haifar da haɗarin kamuwa da cutar kwalara da kuma jefa rayuwar yara cikin haɗari.

Ya bayyana cewa cutar kwalara cuta ce mai saurin yaɗuwa ta hanyar abinci ko ruwan da ke gurɓata da ƙwayoyin cuta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wakilin Hukumar FAO A Iran Yace Sauyin Yanayi Ya shafi Dukkan Yankin
  • Iran Ta Ce Ba Wani Ma’aikacin Hukumar IAEA A Kasar A Halin Yanzu
  • Gwamnan Jihar Kwara Ya Hori Sabbin Matasa Masu Yiwa Kasa Hidima Akan Kishin Kasa
  • Iran Ta Jaddada Cewa: Karfin Makamai Masu Linzami Da Jiragen Sama Marasa Matuka Ciki Suna Nan Cikin  Shiri
  • Iran Da Japan Suna Iya Jagorantar Duniya Don Rabata Da Makamai Kare Dangi
  • Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki
  • Mutanen Kasar Siriya Sun Fito Zanga-Zanga Yin Allawadai Da Kissan Alawiyya A Kasar
  • Iran ta yi gargadi game da makirce-makircen Isra’ila na kawo cikas ga tsaron yankin
  • Har yanzu ana fama da cutar kwalara a Najeriya – UNICEF
  • Sin Ta Samarwa Sassan Kasa Da Kasa Damar Shigowa Ba Tare Da Bukatar Biza Ba