Iran da Saudiyya sun jaddada bukatar kare hurimin kasar Siriya
Published: 5th, May 2025 GMT
Kasashen Iran da kuma Saudiyya sun jaddada kiran su na ganin an kare hurumin kasar Siriya tare kuma da yin tir da hare-haren da Isra’ila ke kai wa kasar.
Jami’an Iran da Saudiyya sun tabbatar da aniyarsu ta tabbatar da ‘yancin kai da kuma ‘yancin yankin Siriya, tare da yin Allah wadai da harin da sojojin Isra’ila suka kai kan al’ummar kasar Larabawar.
An bayyana hakan ne a wata ganawa da aka yi a ranar Lahadi a birnin Riyadh tsakanin Mohammad-Reza Raouf Sheibani, wakilin Iran na musamman kan Syria, da Saud al-Sati, mataimakin ministan harkokin wajen Saudiyya kan harkokin siyasa, a yayin da suke magana kan yadda ake samun sauyin yanayi a kasar Siriya, da kuma mafi girman tasirin hare-haren da Isra’ila ke kaiwa a yankin.
M. Sheibani ya sake jaddada goyon bayan Iran ga hadin kai da ‘yancin kai na Siriya, yana mai yin tir da hare-haren da gwamnatin Isra’ila ke kai wa a matsayin barna da kuma tada zaune tsaye.
Ya jaddada cewa irin wadannan ayyuka na kawo cikas ga zaman lafiyar yankin da kuma saba ka’idojin kasa da kasa.
A nasa bangaren, al-Sati ya yi na’am da wannan ra’ayi, yana mai tabbatar da daidaiton matsayin Saudiyya na goyon bayan tabbatar da yankin Siriya, zaman lafiya da kwanciyar hankali.
Ya yi Allah wadai da hare-haren da gwamnatin kasar ke kai wa a yankin na Syria, yana mai bayyana bukatar bin dokokin kasa da kasa da mutunta ikon kasa a duniya.
Bangarorin biyu sun amince da muhimmancin ci gaba da tuntubar juna dangane da ci gaban yankin, tare da jaddada bukatar yin hadin gwiwadon tinkarar kalubalen da ake fuskanta.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: hare haren da tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
Babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin CMG, ya gabatar da labarin ganawar da aka yi jiya Alhamis tsakanin shugabannin Sin da Amurka a Busan na Korea ta Kudu, cikin harsuna 85. Kuma zuwa yau Juma’a, mutanen da suka karanta rahotanni masu alaka da ganawar ta hanyoyin watsa labarai na dandalin CMG sun kai miliyan 712. Haka kuma, kafafen watsa labarai na kasa da kasa 1678, sun wallafa tare da tura rahotanni da bidiyon labaran CMG na harsuna daban daban game da ganawar, har sau 4431.
Har ila yau a wannan rana, an gudanar taron tattaunawa na kasa da kasa kan bude kofa da kirkire kirkire da ci gaba na bai daya a kasar Uruguay, wanda CMG da hadin gwiwar ofishin jakadancin Sin dake kasar suka shirya a Montevideo babban birnin Uruguay. (Mai fassara: FMM)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA