HausaTv:
2025-05-04@23:19:16 GMT

Sharhin Bayan Labarai: Ranar Malami A Kasar Iran

Published: 4th, May 2025 GMT

Assalamu alaikum masu sauraro, sharhin bayan labarammu zai yi magana ne a kan Aya. Shahid Mttahari, shahidi na farko daga cikin malamai jagororin juyin juya halin musulunci a nan kasar Iran a shekara 1979.

A jiya Jumma ce 2 ga watan Mayu na wannan shekara ta 2025 aka yi juyayin shahadar malami na fadrko wanda ya kai ga shahada bayan nasaral juyin juya halin musulunci a nan iran.

Aya. Murtadha Muttahari, malami marubuci sannan jagora mai farkar da mutane a Iran da sauran kasashen duniya ta hanyar alkalaminsa da kuma jawabansa na shekaru masu yawa.

Kafin juyin juya halin musulunci a nan Iran shekaru 46 da suka gabata, Aya, Muttahari ya zama fitilla ga mutane da dama a nan kasar Iran, musamman daliban Jami’I’oo a nan Iran kuma musamman daliban Jami’ar Tehran wadanda ya dauki shekari kimani 23 yana karantar da ilmin addinai da kuma falsafa.

Shaida Muttahari ya rubuta littafai a fannoniun ilmi da dama , kama daga Fikihu, akidu, falsafatarihi da sauransu kuma ya karantar da su. Banda haka shi jagora ne na fada da azzaluman shugabannni a karni na 20 da ya gabata.

Sanaiyyar wadannan al-amura da Shahid Muttahari aka sanya ranar 2 ga watan Mayu na ko wace shekara tun bayan shahadarsa a matsayin ranar Malami.

Aya. Mutahhari ya barman littafan da ya rubuta fiye da 100 kuma an tarjama wasunsu zuwa harsuna da dama a duniya. Wadannan littafan sun zama fitila wadanda suka farkar da mutanen da dama a ko ina a duniya.

Wani mai tarjamar Littafai a kasar Malasiya Seyyed Sheikh ibn Seyyed Mostafa, ya ce shi kadai ya tarjama littafan Shahid Mutahhari har guda 70, amma har yanzin ana bukatar littafan sa, a kasuwan. A bangaren ikida wasu malaman addini sun bayyana cewa ba wanda masana a kasahen yamma suka fahinci falsafan addinin musulunci kamar yadda suka fahinta a littgafan shaida muttahari.

Wata kungiyar batacciya a lokacin a nan Iran wacce ake kira Furkan ne ta sa daya daga cikin mabiyanta ya zo ya bindige shahid Muttahiri a kusa da gidansa a nan Tehran kwanaki 80 kacal da samun nasarar juyin juya halin musulunci a nan kasar Iran a shekara 1979. Da wani dalili wannan kungiyar ta kasheshi, Al..ya sani. Da fatan All..ya hasakak kabarinsa ya sa mu kara fahintar ilmin da ya bara mana.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: juyin juya halin musulunci a nan

এছাড়াও পড়ুন:

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Ce Kasar Oman Ce Ta Bukaci Dage Zaman Tattaunawan Iran Da Amurka

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: An dage zaman tattaunawan Iran da Amurka ne bisa shawarar kasar Oman

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya yi nuni da cewa: Ministan harkokin wajen kasar Oman ne ya sanar da sauyin lokacin zaman tattaunawan ba na kai tsaye ba tsakanin Iran da Amurka, yana mai bayanin cewa, dage shawarwarin ya zo ne bisa shawarar ministan harkokin wajen kasar, kuma za a sanar da wata sabuwar rana daga baya.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya sanar da manema labarai cewa: An canja ranar da za a gudanar da zaman shawarwarin ba na kai tsaye ba na gaba tsakanin Iran da Amurka, wanda aka shirya gudanarwa a ranar Asabar 3 ga watan Mayu a birnin Roma na kasar Italiya.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen na Iran ya yi nuni da cewa: Ministan harkokin wajen kasar Oman ne ya sanar da wannan sauyi, yana mai bayanin cewa, dage shawarwarin ya zo ne bisa shawarar ministan harkokin wajen kasar, kuma za a sanar da wata sabuwar rana daga baya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Yaba Da Sadaukarwar Da ‘Yan Jarida Suka Bayar Kan Watsa Wahalhalun Falasdinawa
  • Kasar Yemen Ta Kakaba Takunkumi Kan Amurka A harkokin Fitar Da Man Fetur Din Kasarta
  • Gwamnatin Nijeriya Ta Goyi Bayan Amfani Da Ƙirƙirarrar Basira Cikin Ɗa’a A Aikin Jarida – Minista
  •  Iran Ta Yi Allawadai Da Hare-haren HKI Akan Syria Da Nufin Rusa Kasar
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Sokin Kasar Faransa Kan Mummunar Rawar Da Take Son Takawa Kan Iran
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Yi Kakkausar Suka Kan Hare-Haren Jiragen Saman Amurka Kan Kasar Yemen
  • Layukan Dogo Na Kasar Sin Sun Gudanar Da Sufurin Miliyoyin Fasinjoji A Ranar Farko Ta Hutun ‘Yan Kwadago
  • Bukatar Inganta Rayuwar Daurarru A Gidajen Yarin Kasar Nan
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Ce Kasar Oman Ce Ta Bukaci Dage Zaman Tattaunawan Iran Da Amurka