HausaTv:
2025-11-03@08:51:06 GMT

Kissoshin Rayuwa Imam Alhassan (a) 118

Published: 4th, May 2025 GMT

118-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na Kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshi wadanda suka zo cikin Alkur’ani mai girma ko kuma cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin Dastane Rastan na Aya. Shahid Murtadha Mutahhari ko cikin littafin Mathnawa na maulana jalaluddin Romi ko kuma cikin wasu littafan, da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu a wannan shirin.

//… Masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin kissa ko sirar Imam Al-Hassan Al-mujtaba limami na biyu daga cikin limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All…(s) kuma da na farko ga Fatimah (S) diyar manzon All..(s) kuma jakansa(s) na farko da muke kawo maku, a cikin shirimmu da ya gabata mun tsaya inda muka fara  bayyana yadda aka yi wa Amirulmuminina Aliyu dan Abu Talib(a) bai’a bayan na kashe Khalifa na 3 wato Uthman dan Affan.

Mun yadda mutane suka yi tururuwa zuwa gidansa, suna neman ya fito suyi masa bai’a a matsayin Khalifa, amma ya amincewa da haka. Yana fada masu cewa ya zabi ya zama daya daga cikin wadanda mabiya a kan wanda ake biyu, su zabi duk wanda suka ga dama, zai amince da shi kuma zai yi biyayya a gareshi, amma sai suke ki yin hakan duk da cewa akwai ragowar mambobi na shura wanda khalifa Umar ya kafa, banda shi, akwai Talha da zubair da kuma sa’ad dana bin wakkas amma haibarsa ta rufe ko wa,(a).

Hatta Talha da Zubair suna cikin ribibin mutane wadanda suke tururuwa zuwa gidansa don neman a yi masa bai’a. Amma a lokacinda mutanen madina suka ji tsoron kasa kissan Khalifa Uthman ya zama musiba a garesu, don kada makiya su ji labarin mutuwar Khalifa amma basu ji labarin wanda aka nada ba, sai su tsammanin an sami matsalace a cikin harkokin shugabanci a farwa musulmi da yaki.

Wannan ya sa shurda wato yansanda suka gudanar da taro na musamman sannan daga karshe suka yi barazana ga ma’abuta shura na mutum 6 su fiyar da shugaba a tsakaninsu cikin kwana guda ko kuma su kashesu.

A wannan halin ne sai mutane suka sake komawa wajen Imam Ali (a) suna neman bai’a kawai.

Daga karshe dai ya ce su bashi lokaci zuwa gobe don yayi tunani. Zai fada masu matsayinsa. Amma a lokacinda gari yaw aye sai ya maw mimbarin manzon All..(s) ya yi wata Khuduba wacce a cu=ikinta ne ya bayyana masu sharuddansa na karban shugabanci, suka amince aka yi masa bai’a, kuma mun bayyana cewa Talha dan Ubaidullahi ne ya fara yi masa bai’a, sannan Zubair . sannan mun ji cewa wasu sahabban sun ki yi masa bai’a, Sa’ad dan Abiwakkas da kuma Abdullahi dan Umar. Wadan suka bada uzuri na cewa an sabani a kan Imam Ali(a) don haka ba zasu yi masa bai’a  ba.

Don haka ne ma babu wabi labara da ya nuna cewa Sa’adu dan Abiwakkasa ya taimakwa Imam (s) a yake-yaken da yayi bayan ya zama khalifa ba. Sannan kamar yadda zamu gani nan gaba Abdullahi dan umar wanda yaki ko yiwa Imam Ali bai’a yayi nadama a karshen rayuwarsa, yana cewa yakar rundunar masu kwace bai’a da azzalumai da kuma masu ficewa daga addinin wadanda manzon All..(s) yayi Magana a kansu ya kubuce masa.

Sannan a lokacinda banu Umayya suka kwace iko da daular musulunci, Abdullahi dan Umar ya je yayiwa Khalifan umayyawa Bai’a a wajen Hajjadu dan Yusuf Athaqafi walin Abdulmalik dan marwa a Kufa, sai ya mika masa kafa. Wanda bayan ya ruwaito hadisi mai cewa ‘ duk wanda ya mutu bai ba bai’a a wuyarsa ya mutu mutuwar Jahiliya.

Ko ta yadda al-amura suka kasance dai daga karshen Aliyu dan abitalib (a) ya zama Khalifa na hudu bayan kissan da aka yiwa Khalifa na uku uthman dan Affan.

Sai dai a nan yakamata mu san cewa wani al-amari mai muhimmanci ya auke a tarihin addinin musulunci wanda tasirinsa yana har yanzun yana tafiya a cikin musulmi.

Da farko, Imam Ali (a) yaki yiwa Khalifa na farko bai kan cewa khalifanci hakkinsa ne kamar yadda zamu gani a cikin kisidun wadanda suka tsara kasidu bayan an zabe shi a matsayin khalifa na 4. Kuma bai gushe ba a tsawon tarihin khalifofi uku da suka gabace ya na kan bakansa kan cewa hakkinsa ne aka kwace.

A lokacinda khalifa ya kafa shura na mutane 6 ya kuma sanya shi a cikinsu, a lokacinda suka zauna don fara zaben sai da ya tunatar da su kan cewa Khalifanci hakkinsa ne, don haka su bashi hakkinsa tunda al-amura sun dawo jannunsu. Amma ba wanda ya amsa masa sai Zubair dan awwam, amma suka zabi Utham bayan ta tabbatar da hujjar All.. a kansu Khalifanci hakkinsa ne wanda All.. ya bashi.

Don haka a karo na uku yayi hakuri dan masalahar addinin musulunci. Amma a wannan karon mutanene suka zabeshi don sunga kura-kuran suka bayyana a wajen khalifa na uku har saida ya rasa yardar kowa a cikin al-ummar musulmi sai danginsa. Sannan danginsa din suka kyale aka kasha shi saboda laifukansa.

To a yanzon da mutane sun dawo masa da hakkinsa na khalifanci, da kuma hujjar All..a bayan kasa, to ya bar fada cewa khalifanci hakkinsa ne?

Kamar yadda zamu gani bai bar fad aba, sai dai zamansa khalifa na hudu ya bashi dama ne na ya kara bayyana cewa dukkan khalifofin da suka gabace shi hakkinsa ne suka kwace, kuma sakamakon kwace mata hakkinsa ne al-ummar musulmi suka shiga mummunan halin da suka shiga.

Sannan bugu da kari, Banu Umayya wadanda Khalifa Uthman ya arzutasu da dukiyar al-umma, musamman mu’awiya dan Abusufyan, wanda ya dauki shekaru kimani 20 a kan kujerar waki ko gwamnan sham, ya zama sarki wanda yake ganin ba wanda ya isa ya tabashi, idan ba ku manta ba Khalifa Umar ya fadawa shura na mutum 6 kafin ya rasu kan cewa idan sun yi hasada wa juna sun ki zaben daya daga cikinsu a matsayin Khjalifa to mu’awiya yana nan yana dakonsu.

Wannan ya nuna mana a cikin shekaru 25 da aka yi khalifofi uku suke shugabancin, sun kuma yi wani shiri na yadda shugabancin al-ummar musulmi zata koma hannun Banu Umayya, wato daga kan Mu’awiya dana bi sufyan zuwa sawran yayansa da jikokinsa.

Sun shirya ta yadda wata rana Mu’awiya ko banu umayya danginsa zasu kwace ikon khalifanci daga madina, saboda karfin da zai yi a bayansu. Dana nan addinin musulunci kam, sai dai a yi bankwana da shi.

Don a lokacinda Imam Ali (a) ya kama ragamar khalifansa ya sauke dukkan gwamnonin Uthman daga manya manyan garuruwa kamar Kufa da Basra da Masar, ya sauya su da wadanda ya tabbatar da cewa masu tsoron All..ne, sai Mu’awiya a matsayin gwamna karkashin khalifa a Madina yaki sauka, ba tare da bayyana cewa ai an nada shi wani fiye da shekaru 20  da suka gabata ne don wata rana ya kwace Khalifancin ba, sai dai ya fake da cewa an kasha Khalifa na hudu, don haka suna neman khalifa na hudu ya daukan masu jinin khalifa na uku idan ba haka ba, ba zai yi biyya a gareshi ba.

Kunga ta inda ya fito, kuma shiri ne wanda aka kulla shit un shekaru kimani 25 da suka gabata.

Sannan a bangaren Imam Ali (s) bai bar fahintar da mutane kan yadda al-amura suka kance bayan wafatin manzon All..(s) ba. Daga cikin khuduba mafi muhimmanci wanda ya fada dangane da wannan shi, khudubar shakshakiyya wanda ita ce ta 3 a likin littafin Nahjul Balaga.

Inda yake cewa:

{Amma na rantse da All.., Hakika dan Abukuhafa (wato Abubakar) ko Kahalifa na farko, ya sanyata (khalifancin) kuma hakika ya san cewa matsayi na da ita kamar matsayin dutsen-nika da majuyarsa, ilmi na kwarar daga gareni, kuma ko tsuntsu ba zata riskeni a daukaka ba,  sai na sake labule tsakanina da ita, n araba kaina da ita, sai na yi ta tunani tsakanin in yunkura in tashi a kansu da yankekken hanu ko kuma in yi hakuri cikin makantaccen duhun musibu, wanda babban mutum zai tsufa a cikinsa, sannan yaro kuma yayi furfura a cikinsa, sannan mumini ya rayu cikin kunci har sai ya hadu da ubangijinsa, sai na ga cewa yin hakuri a kan wadannan ya fi, sai na yi hakuri, al-hali  idanu suna kwalla, sanan makokoro a sheke yake, ina ganin an kwace gadona, sai da na farkon ya yi gabansa ya mika khalifancin da na biyu, (sai ya bada misali da kasidar As;ash, Sun bambanta wadanan kwanaki na masu wahala da lokacinda nake jindadi da kamar dan Uwan Jabir,

Abin mamaki da shi! An yi lokacinda yake son a dauke masa ita, (bayan ya karbeta) sai gashi ya kullawa wani ita khalifancin a lokacin mutuwars. Lalle wadannan biyu sun raba al-amarin a tsakaninsu… har zuwa inda yak e cewa- na yi hakuri a duk tsawannan lokaci, da kuma tsananin jarrabawam sai da zai tafi sai ya sanya ta a cikin wata jama’a ya riya cewa ni daya daga cikinsu ne, Abin al-ajabi da shura, me ya hadani da shuri, a ina ne na farkonsu ma ya fi ne, ballanta na a hadani da wadannan mutane, amma sai in yi kasa tare da su, idan sun tashi kuma in tashi tare da su, sai daya daga cikinsu ya karkata ga wani na don kiyayyar da yake da ni, sannan daya kuma ya karkata zuwa ga surukinsa, suna ta tuntuni a kan al-amarin, har sai da na ukkunsu

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: daya daga cikin

এছাড়াও পড়ুন:

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

A 2022, kasashe shida ne suka daina yanke hukuncin kisa, ko dai gaba daya ko kuma wani bangare.

Hudu daga cikinsu; Kazakhstan, Papua New Guinea, Saliyo, Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, sun jingine shi kwatakwata.

Ekuatorial Guinea da Zambia sun ce za a rika amfani da shi ne kawai kan laifuka mafiya kololuwar muni.

A watan Afrilun 2023, majalisar dokokin Malaysia ta kada kuri’ar daina amfani da shi a matsayin tilas kan laifuka 11, ciki har da kisa da kuma ta’addanci.

Majalisar dokokin Ghana ma ta kada kuri’ar soke hukuncin kisa a watan Yulin 2023.

 

Wadanne kasashe ne suka fi yanke hukuncin kisa?

Kasashe 20 ne suka zartar da hukunbcin kisa a 2022, idan aka kwatanta da 18 da suka yi hakan a 2021.

Kungiyar kare hakki ta Amnesty International ta ce jimillar mutum 1,518 aka zartar wa hukuncin kisa a duniya, inda aka samu karin kashi 32 cikin 100. Sai dai ta ce hakikanin adadin ya zarta haka sosai saboda yadda kasashe ke boye batun.

Bayan China, Amnesty ta ce kasashen da suka fi kashe mutane a 2024 su ne Iran (972), da Saudiyya (345), da kuma Iraki (63). Su ne suka zartar da kashi 91 cikin 100 na duka kasashen duniya.

Ana yi wa China kallon kasar da ta zarta kowacce aiwatar da hukuncin kisa a duniya, amma ba a sanin hakikanin adadin mutanen, saboda gwamnati ba ta bayyana su.

Kasashen Koriya ta Arewa da Bietnam ma na amfani da hukuncin kisa sosai amma ba su bayyanawa a hukumance.

Amnesty ta ce ta samu rahoton zartar da hukuncin kisa a bainar jama’a akalla sau uku a 2022 a Iran.

Ta ce Iran din ta kashe akalla mutum biyar saboda laifukan da suka aikata a lokacin da suke kasa da shekara 18 da haihuwa.

Saudiyya ta kashe mutane mafiya yawa a duniya a 2022 cikin shekara 30.

Kasashe biyar; Bahrain, Comoros, Laos, Nijar, Koriya ta Kudu – su ne suka yanke wa mutane hukuncin kisa a 2022 bayan sun shafe tsawon lokaci ba su yi amfani da shi ba.

Duk da cewa adadin na raguwa a Amurka, amma ya karu a 2021, amma duk da haka ya yi kasa sosai idan aka kwatanta da shekarar 1999.

 

Mutum nawa aka kashe saboda safarar miyagun kwayoyi?

Amnesty International ta ce sama da kashi 40 cikin 100 na mutanen da aka zartar wa hukuncin kisa a 2024 saboda laifukan ta’ammali da miyagun kwayoyi ne.

A 2022, an kashe mutum 325 saboda laifukan da suka shafi miyagun kwayoyi. Kasashen da suka aikata hakan su ne:Iran 255 Saudiyya – 57 – Singapore – 11

A 2023, Singapore ta zartar da hukuncin kisa kan mace ta farko cikin shekara 20. A 2018 aka kama Saridewi Djaman da laifin safarar hodar ibilis.

 

Ta yaya kasashe ke zartar da hukuncin kisa?

Saudiyya ce kadai ta zayyana fille kai a matsayin hanyar aiwatar da hukuncin kisa a 2022.

Sauran hanyoyin sun hada da rataya, da allura mai guba, da kuma harbi da bindiga.

A watan Janairun 2024 jihar Alabama ta Amurka ta zartar wa wani mai laifin kisa Kenneth Smith hukuncin kisa ta hanyar amfani da iskar nitrogen gas.

Ya zama mutum na farko a duniya da aka zartar wa hukuncin ta irin wannan hanyar, a cewar cibiyar Death Penalty Information Center da ke Amurka.

Lauyoyin Mista Smiths sun ce salon da ba a taba gwadawa ba kafinsa “rashin imani ne”.

Alabama da wasu jihohin Amurka biyu ne suka amince da amfani da iskar gas din saboda kwayoyin da ake amfani da su wajen yi wa mutum allura mai guba ba sa samuwa cikin sauki.

 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su November 2, 2025 Manyan Labarai Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya November 2, 2025 Manyan Labarai Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka November 2, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai