HausaTv:
2025-05-04@17:15:38 GMT

Kissoshin Rayuwa Imam Alhassan (a) 118

Published: 4th, May 2025 GMT

118-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na Kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshi wadanda suka zo cikin Alkur’ani mai girma ko kuma cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin Dastane Rastan na Aya. Shahid Murtadha Mutahhari ko cikin littafin Mathnawa na maulana jalaluddin Romi ko kuma cikin wasu littafan, da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu a wannan shirin.

//… Masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin kissa ko sirar Imam Al-Hassan Al-mujtaba limami na biyu daga cikin limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All…(s) kuma da na farko ga Fatimah (S) diyar manzon All..(s) kuma jakansa(s) na farko da muke kawo maku, a cikin shirimmu da ya gabata mun tsaya inda muka fara  bayyana yadda aka yi wa Amirulmuminina Aliyu dan Abu Talib(a) bai’a bayan na kashe Khalifa na 3 wato Uthman dan Affan.

Mun yadda mutane suka yi tururuwa zuwa gidansa, suna neman ya fito suyi masa bai’a a matsayin Khalifa, amma ya amincewa da haka. Yana fada masu cewa ya zabi ya zama daya daga cikin wadanda mabiya a kan wanda ake biyu, su zabi duk wanda suka ga dama, zai amince da shi kuma zai yi biyayya a gareshi, amma sai suke ki yin hakan duk da cewa akwai ragowar mambobi na shura wanda khalifa Umar ya kafa, banda shi, akwai Talha da zubair da kuma sa’ad dana bin wakkas amma haibarsa ta rufe ko wa,(a).

Hatta Talha da Zubair suna cikin ribibin mutane wadanda suke tururuwa zuwa gidansa don neman a yi masa bai’a. Amma a lokacinda mutanen madina suka ji tsoron kasa kissan Khalifa Uthman ya zama musiba a garesu, don kada makiya su ji labarin mutuwar Khalifa amma basu ji labarin wanda aka nada ba, sai su tsammanin an sami matsalace a cikin harkokin shugabanci a farwa musulmi da yaki.

Wannan ya sa shurda wato yansanda suka gudanar da taro na musamman sannan daga karshe suka yi barazana ga ma’abuta shura na mutum 6 su fiyar da shugaba a tsakaninsu cikin kwana guda ko kuma su kashesu.

A wannan halin ne sai mutane suka sake komawa wajen Imam Ali (a) suna neman bai’a kawai.

Daga karshe dai ya ce su bashi lokaci zuwa gobe don yayi tunani. Zai fada masu matsayinsa. Amma a lokacinda gari yaw aye sai ya maw mimbarin manzon All..(s) ya yi wata Khuduba wacce a cu=ikinta ne ya bayyana masu sharuddansa na karban shugabanci, suka amince aka yi masa bai’a, kuma mun bayyana cewa Talha dan Ubaidullahi ne ya fara yi masa bai’a, sannan Zubair . sannan mun ji cewa wasu sahabban sun ki yi masa bai’a, Sa’ad dan Abiwakkas da kuma Abdullahi dan Umar. Wadan suka bada uzuri na cewa an sabani a kan Imam Ali(a) don haka ba zasu yi masa bai’a  ba.

Don haka ne ma babu wabi labara da ya nuna cewa Sa’adu dan Abiwakkasa ya taimakwa Imam (s) a yake-yaken da yayi bayan ya zama khalifa ba. Sannan kamar yadda zamu gani nan gaba Abdullahi dan umar wanda yaki ko yiwa Imam Ali bai’a yayi nadama a karshen rayuwarsa, yana cewa yakar rundunar masu kwace bai’a da azzalumai da kuma masu ficewa daga addinin wadanda manzon All..(s) yayi Magana a kansu ya kubuce masa.

Sannan a lokacinda banu Umayya suka kwace iko da daular musulunci, Abdullahi dan Umar ya je yayiwa Khalifan umayyawa Bai’a a wajen Hajjadu dan Yusuf Athaqafi walin Abdulmalik dan marwa a Kufa, sai ya mika masa kafa. Wanda bayan ya ruwaito hadisi mai cewa ‘ duk wanda ya mutu bai ba bai’a a wuyarsa ya mutu mutuwar Jahiliya.

Ko ta yadda al-amura suka kasance dai daga karshen Aliyu dan abitalib (a) ya zama Khalifa na hudu bayan kissan da aka yiwa Khalifa na uku uthman dan Affan.

Sai dai a nan yakamata mu san cewa wani al-amari mai muhimmanci ya auke a tarihin addinin musulunci wanda tasirinsa yana har yanzun yana tafiya a cikin musulmi.

Da farko, Imam Ali (a) yaki yiwa Khalifa na farko bai kan cewa khalifanci hakkinsa ne kamar yadda zamu gani a cikin kisidun wadanda suka tsara kasidu bayan an zabe shi a matsayin khalifa na 4. Kuma bai gushe ba a tsawon tarihin khalifofi uku da suka gabace ya na kan bakansa kan cewa hakkinsa ne aka kwace.

A lokacinda khalifa ya kafa shura na mutane 6 ya kuma sanya shi a cikinsu, a lokacinda suka zauna don fara zaben sai da ya tunatar da su kan cewa Khalifanci hakkinsa ne, don haka su bashi hakkinsa tunda al-amura sun dawo jannunsu. Amma ba wanda ya amsa masa sai Zubair dan awwam, amma suka zabi Utham bayan ta tabbatar da hujjar All.. a kansu Khalifanci hakkinsa ne wanda All.. ya bashi.

Don haka a karo na uku yayi hakuri dan masalahar addinin musulunci. Amma a wannan karon mutanene suka zabeshi don sunga kura-kuran suka bayyana a wajen khalifa na uku har saida ya rasa yardar kowa a cikin al-ummar musulmi sai danginsa. Sannan danginsa din suka kyale aka kasha shi saboda laifukansa.

To a yanzon da mutane sun dawo masa da hakkinsa na khalifanci, da kuma hujjar All..a bayan kasa, to ya bar fada cewa khalifanci hakkinsa ne?

Kamar yadda zamu gani bai bar fad aba, sai dai zamansa khalifa na hudu ya bashi dama ne na ya kara bayyana cewa dukkan khalifofin da suka gabace shi hakkinsa ne suka kwace, kuma sakamakon kwace mata hakkinsa ne al-ummar musulmi suka shiga mummunan halin da suka shiga.

Sannan bugu da kari, Banu Umayya wadanda Khalifa Uthman ya arzutasu da dukiyar al-umma, musamman mu’awiya dan Abusufyan, wanda ya dauki shekaru kimani 20 a kan kujerar waki ko gwamnan sham, ya zama sarki wanda yake ganin ba wanda ya isa ya tabashi, idan ba ku manta ba Khalifa Umar ya fadawa shura na mutum 6 kafin ya rasu kan cewa idan sun yi hasada wa juna sun ki zaben daya daga cikinsu a matsayin Khjalifa to mu’awiya yana nan yana dakonsu.

Wannan ya nuna mana a cikin shekaru 25 da aka yi khalifofi uku suke shugabancin, sun kuma yi wani shiri na yadda shugabancin al-ummar musulmi zata koma hannun Banu Umayya, wato daga kan Mu’awiya dana bi sufyan zuwa sawran yayansa da jikokinsa.

Sun shirya ta yadda wata rana Mu’awiya ko banu umayya danginsa zasu kwace ikon khalifanci daga madina, saboda karfin da zai yi a bayansu. Dana nan addinin musulunci kam, sai dai a yi bankwana da shi.

Don a lokacinda Imam Ali (a) ya kama ragamar khalifansa ya sauke dukkan gwamnonin Uthman daga manya manyan garuruwa kamar Kufa da Basra da Masar, ya sauya su da wadanda ya tabbatar da cewa masu tsoron All..ne, sai Mu’awiya a matsayin gwamna karkashin khalifa a Madina yaki sauka, ba tare da bayyana cewa ai an nada shi wani fiye da shekaru 20  da suka gabata ne don wata rana ya kwace Khalifancin ba, sai dai ya fake da cewa an kasha Khalifa na hudu, don haka suna neman khalifa na hudu ya daukan masu jinin khalifa na uku idan ba haka ba, ba zai yi biyya a gareshi ba.

Kunga ta inda ya fito, kuma shiri ne wanda aka kulla shit un shekaru kimani 25 da suka gabata.

Sannan a bangaren Imam Ali (s) bai bar fahintar da mutane kan yadda al-amura suka kance bayan wafatin manzon All..(s) ba. Daga cikin khuduba mafi muhimmanci wanda ya fada dangane da wannan shi, khudubar shakshakiyya wanda ita ce ta 3 a likin littafin Nahjul Balaga.

Inda yake cewa:

{Amma na rantse da All.., Hakika dan Abukuhafa (wato Abubakar) ko Kahalifa na farko, ya sanyata (khalifancin) kuma hakika ya san cewa matsayi na da ita kamar matsayin dutsen-nika da majuyarsa, ilmi na kwarar daga gareni, kuma ko tsuntsu ba zata riskeni a daukaka ba,  sai na sake labule tsakanina da ita, n araba kaina da ita, sai na yi ta tunani tsakanin in yunkura in tashi a kansu da yankekken hanu ko kuma in yi hakuri cikin makantaccen duhun musibu, wanda babban mutum zai tsufa a cikinsa, sannan yaro kuma yayi furfura a cikinsa, sannan mumini ya rayu cikin kunci har sai ya hadu da ubangijinsa, sai na ga cewa yin hakuri a kan wadannan ya fi, sai na yi hakuri, al-hali  idanu suna kwalla, sanan makokoro a sheke yake, ina ganin an kwace gadona, sai da na farkon ya yi gabansa ya mika khalifancin da na biyu, (sai ya bada misali da kasidar As;ash, Sun bambanta wadanan kwanaki na masu wahala da lokacinda nake jindadi da kamar dan Uwan Jabir,

Abin mamaki da shi! An yi lokacinda yake son a dauke masa ita, (bayan ya karbeta) sai gashi ya kullawa wani ita khalifancin a lokacin mutuwars. Lalle wadannan biyu sun raba al-amarin a tsakaninsu… har zuwa inda yak e cewa- na yi hakuri a duk tsawannan lokaci, da kuma tsananin jarrabawam sai da zai tafi sai ya sanya ta a cikin wata jama’a ya riya cewa ni daya daga cikinsu ne, Abin al-ajabi da shura, me ya hadani da shuri, a ina ne na farkonsu ma ya fi ne, ballanta na a hadani da wadannan mutane, amma sai in yi kasa tare da su, idan sun tashi kuma in tashi tare da su, sai daya daga cikinsu ya karkata ga wani na don kiyayyar da yake da ni, sannan daya kuma ya karkata zuwa ga surukinsa, suna ta tuntuni a kan al-amarin, har sai da na ukkunsu

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: daya daga cikin

এছাড়াও পড়ুন:

Maniyyata Daga Turai Akan Dawakai Sun Isa Kasar Saudiyya Domin Yin Aikin Hajjin 2025

Mahajjata hudu – daya daga Maroko sauran kuma daga Sifaniya – sun isa kasar Saudiyya a kan dawakai a wannan makon da ya fice don gudanar da aikin Hajjin 2025, wanda hakan ke tunatar da al’ummar Musulumi tsarin zuwa aikin hajji a shekaru da dama da suka gabata. Mahajjatan sun isa zuwa kasar Saudiyya ne ta kan iyakar Al Hadithah da ke Al Qurayyat, inda jami’an gwamnati suka tarbe su tare da duba lafiyarsu, da kuma basu abubuwan sha don jinjin irin tafiyar da suka yi ta tsawon makonni. Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe Nijeriya Ta Yi Asarar Naira Biliyan 118 Sakamakon Barnatar Da Iskar Gas A Watanni 2 Hotunan yadda suka yi kura amma cikin nasara sun bazu a yanar gizo, inda suka nuna aniyarsu ta isa Makka ta hanyar amfani da hanyoyin tafiye-tafiye irin na tarihi. “Wannan irin tafiya, tana nuna tsantsar ibada ga Ubangiji,” in ji Mamdouh Al Mutairi, shugaban ofishin kan iyakar Al Hadithah, wanda da kansa ya gaishe da mahayan. Zabin mahayan na ratsa hamada da tsaunuka ya nuna yadda mahajjata ke tafiye-tafiyen aikin Hajji kafin fara amfani da ababen jigilar kayayyaki na zamani. Jami’an Saudiyya sun dauki nauyin duk wata buƙatar mahayan ta musamman. Wannan tafiya ta haifar da muhawara a duk duniya game da daidaita al’ada da zamani a cikin ayyukan addini. Kamar yadda sama da mahajjata miliyan 1.8 ke shirin Hajjin 2025, wannan yunkuri ya fito fili a matsayin shaida na dawwama da imani da juriya akan mabiya addinin Musulunci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kissoshin Rayuwa : Imam Al-Hassan (a) 113
  • Kissoshin Rayuwa : Imam Al-Hassan (a)
  • Maniyyata Daga Turai Akan Dawakai Sun Isa Kasar Saudiyya Domin Yin Aikin Hajjin 2025
  • Babu Dalilin Da Zai Sanya Wasu Mambobin PDP Ficewa A Jam’iyyar A Bauchi
  • Dakataccen Gwamnan Ribas Ya Dawo Daga Hutun Makonni Biyu A Kasar Waje
  • Kotu Ta Daure Wasu Mutum Biyu Da Suka Yi Wa Yarinya ‘Yar Shekara 14 Fyade A Birnin Kebbi
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 116
  • Gobarar rumbum makamai Maiduguri da Matakan da ya kamata a ɗauka — Ƙwararru
  • Gobarar rumbum makamai a Borno: Abin da ya kamata a yi