Iran : Araghchi zai ziyarci Pakistan da Indiya
Published: 4th, May 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi yana shirin kai ziyara a kasashen Pakistan da Indiya a wannan makon a wani bangare na tuntubar juna tsakanin Tehran da kasashen yankin.
Ministan harkokin wajen Iran din zai isa Pakistan a ranar Litinin 5 ga watan Mayu, domin tattaunawa da manyan jami’an kasar.
Tattaunawar za ta mayar da hankali ne kan karfafa dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu da sabbin ci gaban yanki da na kasa da kasa, in ji kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, kafin ya tabbatar da cewa Mr. Araghchi zai kai ziyarar aiki a Indiya nan gaba a cikin mako.
Ziyarar na zuwa ne yayin da ake ci gaba da samun takun saka tsakanin Indiya da Pakistan, kasashe biyu masu makamin nukiliya.
Wannan tashin hankalin dai ya ta’azzara ne sakamakon harin da aka kai a yankin Kashmir da ke karkashin ikon Indiya a ranar 22 ga watan Afrilu, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane 26.
Indiya dai na zargin Pakistan da hannu a harin, zargin da Pakistan din ta musanta.
A wata tattaunawa ta wayar tarho da firaministan Indiya Narendra Modi a ranar 26 ga watan Afrilu, shugaban kasar Iran Massoud Pezeshkian ya yi Allah wadai da harin, yana mai jaddada bukatar hadin gwiwa da yaki da ta’addanci.
A wata tattaunawa ta daban ta wayar tarho da firaministan Pakistan Shehbaz Sharif a wannan rana, Mr. Pezeshkian ya bayyana matukar damuwarsa kan yadda ake kara samun takun saka tsakanin Indiya da Pakistan.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sabon harin Iran ya hallaka mana mutum 8 – Isra’ila
Isra’ila ta ce mutum takwas sun mutu a daren ranar Litinin sakamakon sabon harin da Iran ta kai a biranen Tel Aviv da Haifa da wasu sassa na ƙasar.
Wannan na zuwa ne a matsayin ci gaba daga jerin hare-hare da Iran ke kai wa tun bayan da Isra’ila ta fara kai mata hari makonnin da suka wuce.
NAJERIYA A YAU: Dalilan Durƙushewar Sababbin Sana’o’i Tun Ba A Je Ko’ina Ba Iran ta kai sabbin hare-hare birnin Tel Aviv da HaifaYanzu haka, adadin mutanen da hare-haren Iran suka kashe a Isra’ila ya kai 24, yayin da mutane sa.a da 300 ke kwance a asibitoci saboda raunuka.
Isra’ila ta ce a martaninta, jiragen yaƙin ƙasar sun kai hari a birnin Tehran, babban birnin Iran, inda suka lalata wata hedikwatar dakarun juyin juya hali.
Haka kuma sun kai farmaki a wasu cibiyoyi da Iran ke adana makamai a tsakiyar ƙasar.
An fara wannan rikici ne bayan da Isra’ila ta kai hari da asubahin ranar Juma’a a Iran.
Iran ta ce a wannan harin, mutane sama da 200 ne suka mutu.
Wannan hari ya fusata gwamnatin Iran, inda ta fara mayar da martani da hare-hare a Isra’ila.
A baya ma, ana zargin Isra’ila da kai hare-hare da dama a Iran, musamman kan dakarun da ta ke zargi da taimaka wa ƙungiyoyin da ke barazana gare ta, kamar Hezbollah da Hamas.
Rikicin ya ci gaba da tsananta, yayin da kowane ɓangare ke kai farmaki ga ɗaya, al’ummar ƙasashen biyu na ci gaba da jikkata da mutuwa.