Iran : Araghchi zai ziyarci Pakistan da Indiya
Published: 4th, May 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi yana shirin kai ziyara a kasashen Pakistan da Indiya a wannan makon a wani bangare na tuntubar juna tsakanin Tehran da kasashen yankin.
Ministan harkokin wajen Iran din zai isa Pakistan a ranar Litinin 5 ga watan Mayu, domin tattaunawa da manyan jami’an kasar.
Tattaunawar za ta mayar da hankali ne kan karfafa dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu da sabbin ci gaban yanki da na kasa da kasa, in ji kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, kafin ya tabbatar da cewa Mr. Araghchi zai kai ziyarar aiki a Indiya nan gaba a cikin mako.
Ziyarar na zuwa ne yayin da ake ci gaba da samun takun saka tsakanin Indiya da Pakistan, kasashe biyu masu makamin nukiliya.
Wannan tashin hankalin dai ya ta’azzara ne sakamakon harin da aka kai a yankin Kashmir da ke karkashin ikon Indiya a ranar 22 ga watan Afrilu, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane 26.
Indiya dai na zargin Pakistan da hannu a harin, zargin da Pakistan din ta musanta.
A wata tattaunawa ta wayar tarho da firaministan Indiya Narendra Modi a ranar 26 ga watan Afrilu, shugaban kasar Iran Massoud Pezeshkian ya yi Allah wadai da harin, yana mai jaddada bukatar hadin gwiwa da yaki da ta’addanci.
A wata tattaunawa ta daban ta wayar tarho da firaministan Pakistan Shehbaz Sharif a wannan rana, Mr. Pezeshkian ya bayyana matukar damuwarsa kan yadda ake kara samun takun saka tsakanin Indiya da Pakistan.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede
“Iyakar kasa ba wai kawai yanki ne na tsaro ba. Yanki ne na al’adu; yanki ne na tarihi; haka nan ma yanki ne na tattalin arziki. Kula da shige da fice na da matukar amfani ga ci gabanmu. Wajibi ne Nijeriya ta zuba jari a kan kula da nau’in mutanen da take tacewa wajen shiga kasa da kuma irin mutanen da muke tacewa wajen fita daga kasa.
“Dole ne mu yi nazarin nau’in ayyukan da bakin-haure ke yi da kuma yadda suke shafar tattalin arzikinmu. Muna bukatar tsame mutanen da ke kawo cikas ga ci gabanmu”, in ji Babandede.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA