HKI Ta Tabbatar Da Halakar Sojojinta 2 A Yankin Rafa Na Zirin Gaza
Published: 4th, May 2025 GMT
Gwamnatin HKI ta bada sanarwan halakar sojojinta biyu da kuma jikatan wasu alokacinda suke bincike da kuma kokarin shiga wani rami na karkashin kasa a inda wani bom ya tashi ya kashe su ya kuma raunata wasu.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kakafen yana labaran yahudawan na fadar haka a safiyar yau kuma wadanda aka rutsa da su sun hada da Captain Noam Ravid, dan shekara 23 a duniya da kuma Staff Sergeant Yaly Seror, dan shekara 20 a duniya.
Labarin ya kara da cewa hatsarin ya faru ne a jiya asabar, sannan wasu sojoji biyu daga rundunar Yahalom sun ji rauni.
Tun ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 ne aka fara yakin tufanul Aksa, inda sojojin yahudawan tare da taimakon kasashen yamma suka fara kisan kiyashi ga Falasdinawa a yankin, wanda ya kaiga shahadar mutane 52,495 ya zuwa yanzu. Sannan wasu 118,366 suka ji rauni.
An dan tsaida yaki daga ranar 19 ga watan Jenerun wannan shekara har aka kai wata marhala sai HKI ta tsaida aiwatarda yarjeniyar. Sannan ta sake komawa yaki.
An kashe sojojin yahudawa fiye da 850 daga ciki har da sojojin kasa 414 a yankin na Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kotu Ta Daure Wasu Mutum Biyu Da Suka Yi Wa Yarinya ‘Yar Shekara 14 Fyade A Birnin Kebbi
Wadanda ake tuhumar dai sun tabbatar wa kansu aikata laifin ba tare da kara yin wata shaida ba.
Duk da haka, a kokarin janye ikirari nasu, sun yarda cewa abokai ne kuma suna zaune tare a wurin da suka aikata laifin, kuma aka kama su tare.
Tawagar masu gabatar da kara karkashin jagorancin Barista Zainab M. Jabbo, DDPP daga ma’aikatar shari’a ta Jihar Kebbi, ta gabatar da karar a gaban kotun. A halin da ake ciki, wadanda ake kara sun samu wakilcin Barista Alhassan wanda ya fara kare su, Barista Rilwan M. Mayalo wanda ya kammala da kuma Barista Faruk Dauran, Kodinetan Agaji na shari’a, wanda ya wakilce su a yayin yanke hukunci.
Lauyan wanda ake kara ya kalubalanci nauyin da ke tattare da ikirarin wadanda ake kara suka gabatar a gaban kotu wajen tabbatar da laifukan da ake tuhumarsu da su.
Sai dai bayan dukkan bangarorin biyu sun amince da rubutaccen adireshinsu na karshe, kotun ta yanke hukuncin.
Kotun ta yanke wa wadanda ake tuhumar hukuncin zaman gidan kaso a kan laifin hada baki na aikata fyade. Idan aka yi la’akari da laifin hada baki na cin zarafi, an umurci wadanda ake tuhumar da su biya tarar Naira Dubu Dari biyu da Hamsin (N250,000) ko kuma zaman gidan yari na shekara daya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp