HausaTv:
2025-06-19@07:00:48 GMT

HKI Ta Tabbatar Da Halakar Sojojinta 2 A Yankin Rafa Na Zirin Gaza

Published: 4th, May 2025 GMT

Gwamnatin HKI ta bada sanarwan halakar sojojinta biyu da kuma jikatan wasu alokacinda suke bincike da kuma kokarin shiga wani rami na karkashin kasa a inda wani bom ya tashi ya kashe su ya kuma raunata wasu.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kakafen yana labaran yahudawan na fadar haka a safiyar yau kuma wadanda aka rutsa da su sun hada da  Captain Noam Ravid, dan shekara 23 a duniya da kuma Staff Sergeant Yaly Seror, dan shekara 20 a duniya.

Labarin ya kara da cewa hatsarin ya faru ne a jiya asabar, sannan wasu sojoji biyu daga rundunar Yahalom sun ji rauni.

Tun ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 ne aka fara yakin tufanul Aksa, inda sojojin yahudawan tare da taimakon kasashen yamma suka fara kisan kiyashi ga Falasdinawa a yankin, wanda ya kaiga shahadar mutane 52,495 ya zuwa yanzu. Sannan wasu 118,366 suka ji rauni.

An dan tsaida yaki daga ranar 19 ga watan Jenerun wannan shekara har aka kai wata marhala sai HKI ta tsaida aiwatarda yarjeniyar. Sannan ta sake komawa yaki.

An kashe sojojin yahudawa fiye da 850 daga ciki har da sojojin kasa 414 a yankin na Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’an Tsaron Kan Iyakar Iran Sun Harbo Jiragen Masara Matuka 44 Na Sojojin H.K.Isra’ila

Jami’an tsaron kan iyakokin Iran sun harbo jiragen saman yaki marasa matuki ciki guda 44 a cikin sa’o’i 48 da suka gabata

Kwamandan rundunar tsaron kan iyakokin kasar Iran Birgediya Janar Ahmad Ali Goudarzi ya bayyana cewa: An harbo jiragen sama marasa matuka ciki guda 44 da kananan jiragen saman yakin gwamnatin ‘yan sahayoniyya tare da lalata su a wasu kan iyakokin kasar.

Birgediya Janar Goudarzi ya bayyana a ranar Lahadi cewa: “Bayan harin da gwamnatin ‘yan Sahayoniyya ta kaddamar kan Iran, a cikin sa’o’i 48 da suka gabata, jami’an tsaron Iran sunsamu nasarar kakkabo jiragen sama marasa matuka ciki na gwamnatin ‘yan sahayoniyya guda 44 da kananan jiragen sama na wannan muguwar gwamnati, sakamakon Sanya ido kan shige da ficen kan iyaka ta sararin samaniyya.”

Haka nan kuma yayin da yake ishara da cikakken shirin da dakarun tsaron kan iyakokin kasar suka yi na sa ido da kuma kiyaye iyakokin kasar Iran, ya kara da cewa: Jajirtattun jami’an tsaron kan iyakokin kasar Iran, tare da cikakken shirinsu na kula da tsaron kan iyakokin, sun gargadi dukkan makiya, ‘yan ta’adda, kungiyoyin masu dauke da makamai, da masu fasa kwauri da cewa za su mayar da martani da karfi kan duk wani hari da aka kai kan tsaron kan iyakokin kasar.

Birgediya Janar Goudarzi ya tabbatar da cikakken goyon bayansa ga sauran sojojin kasar, inda ya jaddada sanya ido kan bayanan sirri don tabbatar da tsaron Jamhuriyar Musulunci ta Iran da kuma tunkarar duk wata barazana a kan iyakar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina
  • EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana
  • DAGA LARABA: Ko Kare Kai Daga Harin ‘Yan Ta’adda Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro?
  • Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
  • Tankokin Isra’ila sun kashe mutum 51 a wurin karbar abinci a Gaza
  • Dan shekara 10 ya harbe mahaifinsa ɗan sanda a Anambra
  • Dan shekara 10 ya kashe mahaifinsa ɗan sanda da bindiga
  • FCCPC Ta Sammaci Air Peace Kan Rashin Maido Da Kuɗin Tikitin Jirgin Da Aka Soke Tafiyarsa
  • Jami’an Tsaron Kan Iyakar Iran Sun Harbo Jiragen Masara Matuka 44 Na Sojojin H.K.Isra’ila
  • Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas