Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-02@16:53:29 GMT

Sojojin Sun Kakkabe Wasu Manyan ‘Yan Bindiga A Zamfara

Published: 4th, May 2025 GMT

Sojojin Sun Kakkabe Wasu Manyan ‘Yan Bindiga A Zamfara

Rundunar sojojin Najeriya ta 1 karkashin jagorancin Birgediya Janar Timothy Opurum ta samu gagarumar nasara a yakin da take yi da ta’addanci da ‘yan bindiga a jihar Zamfara, musamman a kananan hukumomin Talata Mafara da Kaura Namoda.

 

A wata sanarwa da mukaddashin mataimakin daraktan hulda da jama’a na rundunar soji, Kyaftin Sulaiman Omale ya fitar tace a farkon farkon watan Mayun 2025, dakarun su da ke sintiri na yaki sun ci karo da dimbin ‘yan ta’adda da suka kutsa kai kauyen Mai Kwanugga a karamar hukumar Talata Mafara.

 

Ya yi bayanin cewa, ‘yan ta’addan sun rika kai hari kan mutanen yankin tare da kona gidaje kafin isowar sojojin, inda ya ce, bayan tuntubar rundunar, sojojin sun yi nasarar fatattakar ‘yan ta’addan bayan barin wuta, inda suka yi nasarar kashe ‘yan ta’adda da dama, ciki har da fitattun ‘yan ta’addan guda biyar da suka hada da Auta Jijji, Dankali, Sagidi, Kachallah Rijaji, da Kachallah Suza.

 

Sanarwar ta kuma ce, dakarun rundunar 1 sun bi sahun ‘yan ta’addan da suka tsere, inda aka samu nasarar kwato wasu tarin makamai da suka hada da bindigogi kirar AK-47 guda 4, Bindigan PKT 1, bututun RPG guda 2, bama-baman RPG guda 6, harsasai 28 na 7.62mm harsashi na musamman na PKT 3 da harsasai na musamman na PKT 3.

 

 

Birgediya Janar Timothy Opurum ya yabawa kwazon sojojin tare da tabbatar wa ‘yan kasar tabbacin da rundunar ta yi ba tare da bata lokaci ba na maido da zaman lafiya da tsaro a fadin jihar.

 

Rundunar sojin Najeriya ta karfafa gwiwar jama’a da su ci gaba da bayar da sahihin bayanai ga hukumomin tsaro tare da kaucewa daukar doka a hannunsu.

 

 

REL/AMINU DALHATU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Tsaro Zamfara yan ta addan

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare

A ranar 30 ga wata ne shugabannin kasashen Sin da Amurka suka gana da juna a birnin Busan na kasar Koriya ta Kudu, lamarin da ya jawo hankulan kasa da kasa, inda shugabannin 2 suka yi musayar ra’ayoyi dangane da huldar da ke tsakanin kasashen 2 da al’amuran da suka jawo hankulansu. Sun amince da inganta hadin gwiwar kasashen 2 a fannonin tattalin arziki da cinikayya da makamashi da kyautata mu’amalar al’adu.

A yayin ganawar, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya jaddada cewa, yana son hada kai da shugaba Donald Trump na Amurka wajen aza harsashi mai kyau na raya huldar da ke tsakanin kasashen 2, tare da samar wa juna kyakkyawan yanayin samun ci gaba. A nasa bangaren, shugaba Trump ya ce, kasar Sin, abokiyar Amurka ce mafi girma. Kasashen 2 za su hada kansu wajen samun nasarar gudanar da manyan ayyuka da dama a duniya. Nan gaba Amurka da Sin za su kara samun nasara a hadin gwiwarsu. Shugabannin 2 sun amince su rika yin mu’amala da juna. Shugaba Trump yana sa ran kai ziyara a kasar Sin a farkon shekara mai zuwa, ya kuma gayyaci shugaba Xi ya ziyarci Amurka.

Masharhanta sun yi nuni da cewa, ganawar shugabannin 2 ta sanya tagomashi kan kyautatuwar huldar da ke tsakanin Sin da Amurka, ta kuma tsara manufar raya huldar kasashen 2 a nan gaba, tare da kwantar da hankulan kasashen duniya.

Abubuwan tarihi da kuma hakikanin abubuwa sun nuna cewa, wajibi ne Sin da Amurka su zama abokan juna. A wannan muhimmin lokaci, ganawar da shugabannin kasashen 2 suka yi ta sake tsara manufar kyautata da raya huldar da ke tsakanin kasashen 2. Muddin kasashen 2 suka aiwatar da muhimman daidaito da shugabannin 2 suka cimma, da mutunta ruhin adalci, tare da martaba juna da samun moriyar juna, to, za a raya huldar da ke tsakanin kasashen 2 ba tare da wata matsala ba, da kuma kara samar da kwanciyar hankali da tabbaci a duniya. (Tasallah Yuan)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi October 31, 2025 Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo October 30, 2025 Daga Birnin Sin Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma  October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari
  • Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
  • Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?
  • Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa