Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-09-17@23:28:12 GMT

Sojojin Sun Kakkabe Wasu Manyan ‘Yan Bindiga A Zamfara

Published: 4th, May 2025 GMT

Sojojin Sun Kakkabe Wasu Manyan ‘Yan Bindiga A Zamfara

Rundunar sojojin Najeriya ta 1 karkashin jagorancin Birgediya Janar Timothy Opurum ta samu gagarumar nasara a yakin da take yi da ta’addanci da ‘yan bindiga a jihar Zamfara, musamman a kananan hukumomin Talata Mafara da Kaura Namoda.

 

A wata sanarwa da mukaddashin mataimakin daraktan hulda da jama’a na rundunar soji, Kyaftin Sulaiman Omale ya fitar tace a farkon farkon watan Mayun 2025, dakarun su da ke sintiri na yaki sun ci karo da dimbin ‘yan ta’adda da suka kutsa kai kauyen Mai Kwanugga a karamar hukumar Talata Mafara.

 

Ya yi bayanin cewa, ‘yan ta’addan sun rika kai hari kan mutanen yankin tare da kona gidaje kafin isowar sojojin, inda ya ce, bayan tuntubar rundunar, sojojin sun yi nasarar fatattakar ‘yan ta’addan bayan barin wuta, inda suka yi nasarar kashe ‘yan ta’adda da dama, ciki har da fitattun ‘yan ta’addan guda biyar da suka hada da Auta Jijji, Dankali, Sagidi, Kachallah Rijaji, da Kachallah Suza.

 

Sanarwar ta kuma ce, dakarun rundunar 1 sun bi sahun ‘yan ta’addan da suka tsere, inda aka samu nasarar kwato wasu tarin makamai da suka hada da bindigogi kirar AK-47 guda 4, Bindigan PKT 1, bututun RPG guda 2, bama-baman RPG guda 6, harsasai 28 na 7.62mm harsashi na musamman na PKT 3 da harsasai na musamman na PKT 3.

 

 

Birgediya Janar Timothy Opurum ya yabawa kwazon sojojin tare da tabbatar wa ‘yan kasar tabbacin da rundunar ta yi ba tare da bata lokaci ba na maido da zaman lafiya da tsaro a fadin jihar.

 

Rundunar sojin Najeriya ta karfafa gwiwar jama’a da su ci gaba da bayar da sahihin bayanai ga hukumomin tsaro tare da kaucewa daukar doka a hannunsu.

 

 

REL/AMINU DALHATU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Tsaro Zamfara yan ta addan

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Matakin hana malaman da ba su da rajista hawa mumbari a Neja yana ci gaba da yamutsa hazo a ciki da wajen jihar.

Yayin da wasu suke ganin wannan mataki bai dace ba, wasu kuwa gani suke faduwa ta zo daidai da zama, wato matakin ya zo a daidai lokacin da ake bukata.

NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau Uku

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kan tanadin Dokar Kasa game da wannan batu.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba
  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000
  • Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa