Aminiya:
2025-05-04@05:46:04 GMT

Hajjin Bana: Gwamnatin Jigawa ta aika wa NAHCON Naira biliyan 6 

Published: 4th, May 2025 GMT

Hukumar jin daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce ta miƙawa Hukumar Alhazai ta Ƙasa NAHCON kuɗi sama da Naira biliyan 6 a matsayin kuɗin jigilar maniyyatan jihar na 2025 na zuwa Saudiyya.

Bayanin hakan ya fito ne daga bakin Darakta Janar na Hukumar Alhaji Ahmed Labbo a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Dutse, ya ce hukumar ta raba tare da sayar da kason kujerun aikin Hajji sama da 1,000 na jihar ga ƙananan hukumomi 27 ga mahajjata.

Sojoji sun kama jami’an tsaro da ke haɗa baki da ’yan ta’adda ISWAP sun kai wa sojoji hari a Yobe 

Umar Labbo ya bayyana cewa, hukumar ta kammala shirye-shiryenta da suka haɗa da biza ga maniyyatan jihar, inda a yanzu ake jiran tashin jirgi na farko daga jihar da zarar lokacin ya yi.

Don haka ya shawarci maniyyatan jihar da su kasance wakilan ƙasar nagari ta hanyar gujewa abubuwan da za su ɓata sunan jihar da ƙasa baki ɗaya yayin da suke ƙasa mai tsarki.

Babban daraktan ya kuma shawarci alhazai da su yi amfani da ilimin da suka samu a aikin Hajji a kowane mataki, ya kuma shawarce su da su riƙa yin haƙuri a matsayin abokan aikinsu a duk tsawon wannan aiki, ya buƙace su da su bi ƙa’idojin da hukumar ta tanadar a duk lokacin gudanar da aikin.

Ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa yadda yake ci gaba da baiwa hukumar tallafi, wanda ya sa hukumar ta ɓullo da tsare-tsaren buƙatun alhazai daban-daban domin samun walwala da kariya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

Ya ci gaba da cewa, tuni aka fara gudanar da wasu manyan ayyukan a Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar, musamman a ta Lekki da ta Tin Can Island.

Shugaban ya bayyana cewa, an kuma samar da kafar sadarwa ta zamani ga masu ruwa da tsaki a daukacin Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar, domin a rinka yin musayar Data, har da lokacin da ya dace, a fara gudanar da aiki.

Ya sanar da cewa, idan an kammala wannan aikin, za su kara taimaka wa wajen kara inganta ayyukan Hukumar, na tsawon sa’oi 24.

Dantosho wanda Manajan Sashen Tashar da ke a jihar Legas Lawal Ibrahim ya wakilce shi a wajen taron ya bayyana cewa, Hukumar ta kuma yi hadaka da Rundunar Sojin Ruwa, Rundunar ‘Yansanda ta kasa da kuma Hukumar Kula da Tsaro da sufurin jiragen Ruwa ta Kasa NIMASA musamman domin a kara karfafa samar da tsaro da kuma bai wa ma’aikatan Hukumar kariya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Nijeriya Ta Goyi Bayan Amfani Da Ƙirƙirarrar Basira Cikin Ɗa’a A Aikin Jarida – Minista
  • Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja
  • Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026
  • Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
  • Zamfara Ta Biya Sama Da Naira Biliyan 13 A Matsayin Bashin Garatuti Da Aka Gada – Mataimakin Gwamna.
  • Gwamnan Jigawa Ya Halarci Taron Ranar Ma’aikata Ta Bana
  • Hamas Ta Yi Allah Wadai Da Matsayin Amurka Na Goyon Bayan Haramta Hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijiran Falasdinawa Ta UN
  • WHO, ta nuna kaduwa da abin da ke faruwa a Gaza
  • Gwamnatin Kano Zata Kashe Naira Miliyan Dubu 51 Don Aiwatar Da Ayukka