Aminiya:
2025-06-18@13:41:36 GMT

Hajjin Bana: Gwamnatin Jigawa ta aika wa NAHCON Naira biliyan 6 

Published: 4th, May 2025 GMT

Hukumar jin daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce ta miƙawa Hukumar Alhazai ta Ƙasa NAHCON kuɗi sama da Naira biliyan 6 a matsayin kuɗin jigilar maniyyatan jihar na 2025 na zuwa Saudiyya.

Bayanin hakan ya fito ne daga bakin Darakta Janar na Hukumar Alhaji Ahmed Labbo a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Dutse, ya ce hukumar ta raba tare da sayar da kason kujerun aikin Hajji sama da 1,000 na jihar ga ƙananan hukumomi 27 ga mahajjata.

Sojoji sun kama jami’an tsaro da ke haɗa baki da ’yan ta’adda ISWAP sun kai wa sojoji hari a Yobe 

Umar Labbo ya bayyana cewa, hukumar ta kammala shirye-shiryenta da suka haɗa da biza ga maniyyatan jihar, inda a yanzu ake jiran tashin jirgi na farko daga jihar da zarar lokacin ya yi.

Don haka ya shawarci maniyyatan jihar da su kasance wakilan ƙasar nagari ta hanyar gujewa abubuwan da za su ɓata sunan jihar da ƙasa baki ɗaya yayin da suke ƙasa mai tsarki.

Babban daraktan ya kuma shawarci alhazai da su yi amfani da ilimin da suka samu a aikin Hajji a kowane mataki, ya kuma shawarce su da su riƙa yin haƙuri a matsayin abokan aikinsu a duk tsawon wannan aiki, ya buƙace su da su bi ƙa’idojin da hukumar ta tanadar a duk lokacin gudanar da aikin.

Ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa yadda yake ci gaba da baiwa hukumar tallafi, wanda ya sa hukumar ta ɓullo da tsare-tsaren buƙatun alhazai daban-daban domin samun walwala da kariya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Jirgin alhazai ya yi saukar gaggawa kan barazanar harin bom

Alhazai 442 sun tsallake rijiya da baya, bayan jirgin da ya ɗauko su bayan sun kammala aikin Hajjin bana ya samu sakon cewa an dasa bom a cikinsa a yayin da yake sararin samaniya a ƙasa Indonesiya.

A ranar Talata ne jirgin, mallakin kamfanin Saudia Air, ya yi saukar gaggawa a birnin Jakarta babban birnin ƙasar Indonesiya, bayan da ya ɗauko alhazan da daga birnin Jidda na ƙasar Saudiyya.

’Yan sanda ƙasar Indonesiya sun ce an yi nasarar fitar da ɗauƙacin fasinjojin jirgin su 442 a filin jirgi da ke lardin Sumatra ta Arewa.

Ma’aikatar Sufuri ta ƙasar Indonesiya ta ce jirgin ya yi saukar gaggawa ne bayan samun wani saƙon imel cewa an sanya bom a jirgi.

Sarki ya yi barazanar hana yin Musulunci a garinsa bayan dodanni sun kai wa Musulmi hari Matatar man Isra’ila ta daina aiki bayan sabon harin Iran

Ta bayyana cewa bayan kwashe mutanen,  ’yan sanda sun fara aikin bincike domin gano bom ɗin da kuma lalata shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mun shirya yin sulhu da ’yan bindiga — Gwamnatin Sakkwato
  • Ma’aikatan Kwalejin Ilimi ta jihar Kaduna za su tsunduma yajin aiki
  • Ambaliyar Mokwa – Har yanzu muna neman mutum 700 – Gwamnatin Neja
  • Buni ya bai wa manoma 1,000 tallafin aikin gona
  • Iran ta kai hari hedikwatar hukumar leƙen asirin Isra’ila
  • Jirgin alhazai ya yi saukar gaggawa kan barazanar harin bom
  • KADSEMA da IOM sun fara tantance ɓarnar da ambaliya ta yi a Kaduna
  • An Zartar Da Hukuncin Kisa Kan Dan Leken Asirin Haramtacciyar Kasar Isra’ila A Iran
  • Mataimakin Gwamnan Sakkwato bai karɓi shanun tallafin layya ba — Hukumar Zakka
  • Ƴansanda Sun Fara Tsananta Ɗaukar Mataki Kan Ƴan Daba A Kano