Hajjin Bana: Gwamnatin Jigawa ta aika wa NAHCON Naira biliyan 6
Published: 4th, May 2025 GMT
Hukumar jin daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce ta miƙawa Hukumar Alhazai ta Ƙasa NAHCON kuɗi sama da Naira biliyan 6 a matsayin kuɗin jigilar maniyyatan jihar na 2025 na zuwa Saudiyya.
Bayanin hakan ya fito ne daga bakin Darakta Janar na Hukumar Alhaji Ahmed Labbo a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Dutse, ya ce hukumar ta raba tare da sayar da kason kujerun aikin Hajji sama da 1,000 na jihar ga ƙananan hukumomi 27 ga mahajjata.
Umar Labbo ya bayyana cewa, hukumar ta kammala shirye-shiryenta da suka haɗa da biza ga maniyyatan jihar, inda a yanzu ake jiran tashin jirgi na farko daga jihar da zarar lokacin ya yi.
Don haka ya shawarci maniyyatan jihar da su kasance wakilan ƙasar nagari ta hanyar gujewa abubuwan da za su ɓata sunan jihar da ƙasa baki ɗaya yayin da suke ƙasa mai tsarki.
Babban daraktan ya kuma shawarci alhazai da su yi amfani da ilimin da suka samu a aikin Hajji a kowane mataki, ya kuma shawarce su da su riƙa yin haƙuri a matsayin abokan aikinsu a duk tsawon wannan aiki, ya buƙace su da su bi ƙa’idojin da hukumar ta tanadar a duk lokacin gudanar da aikin.
Ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa yadda yake ci gaba da baiwa hukumar tallafi, wanda ya sa hukumar ta ɓullo da tsare-tsaren buƙatun alhazai daban-daban domin samun walwala da kariya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
“Haka kuma an kama wata mata mai shekaru 34 da ake zargi da hannu a lamarin, tare da wasu masu gidan marayu guda biyu da ke Abuja da Jihar Nasarawa, inda aka gano wasu yaran da ake kyautata zaton an yi safarar su. Wasu daga cikin gidajen marayun da aka gano ana amfani da su ne a matsayin cibiyoyin ajiye yara, inda ake jiran ‘kwace’ ko sayar da su da sunan daukar nauyin marayu.”
Ya ce, “An gano gidajen marayu guda hudu da ke Kaigini, Kubwa Edpressway Abuja; Masaka Area 1, Mararaba kusa da Abaca Road; da kuma Mararaba bayan Kasuwar Duniya suna da alaka da wannan kungiya, kuma ana ci gaba da bincike a kansu.”
Ya kara da cewa, daya daga cikin masu korafin ya bayyana cewa ya biya Naira miliyan 2.8 a matsayin kudin daukar yaro, sannan ya biya Naira 100,000 a matsayin kudin shawara ga daya daga cikin ‘yan kungiyar.
Sanarwar ta kara da cewa, “Wani mai korafi ya ce shi ma ya biya Naira miliyan 2.8 kudin daukar yaro da Naira 100,000 kudin shawara ga wani dan kungiyar.
“An canza sunayen yawancin yaran da aka ceto, lamarin da ya kara wahalar da bincike da gano asalinsu,” in ji sanarwar.
Darakta Janar ta NAPTIP, Binta Adamu Bello, ta bayyana damuwarta kan wannan lamari, inda ta ce safarar yara ta zama babbar matsala a kasa.
Ta hanyar Adekoye, DG din ta nuna damuwa game da yadda wasu gidajen marayu ke amfani da raunin jama’a wajen aiwatar da safarar yara.
Ta ce, “Abin takaici ne yadda wasu masu mugunta da ke da sunayen kwararru da matsayi a cikin al’umma, suke amfani da matsayin su wajen yaudarar mutanen da ke cikin mawuyacin hali, su yi safarar ‘ya’yansu, da dama daga cikinsu ma sun tsira ne daga halaka a lokacin rikice-rikicen al’umma ko na manoma da makiyaya, sannan a sayar da su ga iyaye masu neman haihuwa a matsayin daukar yaro ba tare da sahihin izinin iyayensu ba.
“Wannan abin ba za a yarda da shi ba, kuma wadanda aka kama kan wannan mugun aiki za su fuskanci hukuncin doka yadda ya kamata.
“’Ya’yanmu ba kayayyaki ba ne da za a ajiye su a gidajen marayu a sayar ga mai biyan mafi tsada. Wannan dole ya tsaya,” in ji ta.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA