Hajjin Bana: Gwamnatin Jigawa ta aika wa NAHCON Naira biliyan 6
Published: 4th, May 2025 GMT
Hukumar jin daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce ta miƙawa Hukumar Alhazai ta Ƙasa NAHCON kuɗi sama da Naira biliyan 6 a matsayin kuɗin jigilar maniyyatan jihar na 2025 na zuwa Saudiyya.
Bayanin hakan ya fito ne daga bakin Darakta Janar na Hukumar Alhaji Ahmed Labbo a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Dutse, ya ce hukumar ta raba tare da sayar da kason kujerun aikin Hajji sama da 1,000 na jihar ga ƙananan hukumomi 27 ga mahajjata.
Umar Labbo ya bayyana cewa, hukumar ta kammala shirye-shiryenta da suka haɗa da biza ga maniyyatan jihar, inda a yanzu ake jiran tashin jirgi na farko daga jihar da zarar lokacin ya yi.
Don haka ya shawarci maniyyatan jihar da su kasance wakilan ƙasar nagari ta hanyar gujewa abubuwan da za su ɓata sunan jihar da ƙasa baki ɗaya yayin da suke ƙasa mai tsarki.
Babban daraktan ya kuma shawarci alhazai da su yi amfani da ilimin da suka samu a aikin Hajji a kowane mataki, ya kuma shawarce su da su riƙa yin haƙuri a matsayin abokan aikinsu a duk tsawon wannan aiki, ya buƙace su da su bi ƙa’idojin da hukumar ta tanadar a duk lokacin gudanar da aikin.
Ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa yadda yake ci gaba da baiwa hukumar tallafi, wanda ya sa hukumar ta ɓullo da tsare-tsaren buƙatun alhazai daban-daban domin samun walwala da kariya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Jirgin alhazai ya yi saukar gaggawa kan barazanar harin bom
Alhazai 442 sun tsallake rijiya da baya, bayan jirgin da ya ɗauko su bayan sun kammala aikin Hajjin bana ya samu sakon cewa an dasa bom a cikinsa a yayin da yake sararin samaniya a ƙasa Indonesiya.
A ranar Talata ne jirgin, mallakin kamfanin Saudia Air, ya yi saukar gaggawa a birnin Jakarta babban birnin ƙasar Indonesiya, bayan da ya ɗauko alhazan da daga birnin Jidda na ƙasar Saudiyya.
’Yan sanda ƙasar Indonesiya sun ce an yi nasarar fitar da ɗauƙacin fasinjojin jirgin su 442 a filin jirgi da ke lardin Sumatra ta Arewa.
Ma’aikatar Sufuri ta ƙasar Indonesiya ta ce jirgin ya yi saukar gaggawa ne bayan samun wani saƙon imel cewa an sanya bom a jirgi.
Sarki ya yi barazanar hana yin Musulunci a garinsa bayan dodanni sun kai wa Musulmi hari Matatar man Isra’ila ta daina aiki bayan sabon harin IranTa bayyana cewa bayan kwashe mutanen, ’yan sanda sun fara aikin bincike domin gano bom ɗin da kuma lalata shi.