Aminiya:
2025-08-02@20:58:44 GMT

Sojoji sun kama jami’an tsaro da ke haɗa baki da ’yan ta’adda

Published: 4th, May 2025 GMT

Hedikwatar tsaro ta tabbatar da kama wasu jami’an tsaro huɗu da ke taimakawa ayyukan ta’addanci a yankin Arewa maso Gabas.

Waɗanda ake zargin sun haɗa da wasu jami’ai biyu na rundunar haɗin gwiwa da ke aiki tare da sojoji domin yaƙar ’yan ta’addar.

ISWAP sun kai wa sojoji hari a Yobe  An kama masu garkuwa da mutane 3 da kuɓutar da wasu

A cewar Darakta mai kula da harkokin yaɗa labarai na tsaro, Manjo Janar Markus Kangye, an kame sojojin ne a wani samame da aka yi tsakanin ranakun 26 zuwa 29 ga watan Afrilu a cikin ƙananan hukumomin Bama, Kukawa, da Madagali.

Ya ce, suna daga cikin waɗanda suke taimakawa ’yan ta’adda huɗu da sojojin suka kama.

Kangye ya nuna damuwarsa kan cin amanar da suke yi, ya kuma gargaɗi kwamandojin da su wayar da kan jami’ansu kan ayyukan da za su kawo cikas ga ƙoƙarin da sojoji ke yi.

“A wani samame da aka gudanar tsakanin ranakun 26-29 ga Afrilu, 2025 a ƙananan hukumomin Bama, Kukawa, da Madagali na Jihohin Borno da Adamawa, sojoji sun kama wasu ’yan ta’adda guda huɗu da ke kai kayan aikin ga mahara, abin baƙin ciki, an tabbatar da cewa biyu daga cikinsu na cikin rundunar haɗin gwiwa.”

Don haka dole ne kwamandoji su wayar da kan jami’an rundunar haɗin gwiwa da su daina haɗa kai da wasu ko ƙarfafa ayyukan ta’addanci da ke da ikon yi wa ayyukanmu zagon ƙasa,” in ji Kangye.

A wani samame kuma, Kangye ya ce sojoji tare da haɗin gwiwar dakarun haɗin gwiwa sun kai farmakin da suka haɗa da sintiri na yaƙi, samame, da aikin share fage a ƙananan hukumomin Gwoza da Dikwa da Bama da Chibok da Gujba da Geidam da kuma Yunusari.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Adamawa Kukawa rewa maso Gabas haɗin gwiwa

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

A wani samame kuma, ƴansanda sun kama wani da ake zargin barayin USB ne, tare da ƙwato kayayyakin da aka lalata, ciki har da wata mota da aka yi amfani da ita wajen gudanar da aikin ba bisa ƙa’ida ba, inda ya ƙara da cewa “an kama su ne biyo bayan bayanan sirri da aka samu a ranar 15 ga Yuli, 2025, da misalin ƙarfe 0300 na safe.”

Wanda ake zargin mai suna Abubakar Sadi mai shekaru 25 dan asalin Kofar Waika ta jihar Kano, an kama shi a wurin da lamarin ya faru, yayin da sauran wadanda ake zargin suka tsere cikin daji.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rahoton Majalisar Dinkin Duniya Ya Yi Gargadi Kan Barazanar Kungiyoyin ‘Yan Ta’adda A Afirka
  • An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo
  • Jami’ar Umaru Yar’adua ta kori ɗalibai 57 kan satar jarabawa
  • Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa
  • Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa
  • An ceto mutum uku da aka yi garkuwa da su a Kebbi
  • Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa
  • INEC Ta Gudanar da Taron Masu Ruwa da Tsaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi na Babura/Garki
  • Amurka Ta Kakabawa Jami’an Gwamnatin Falasdinawa Takunkuman Hana Shiga Amurka
  • ZAMFARA: APC Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Dauki Don Matsalar Tsaro Na Kara Tsananta