Sojoji sun kama jami’an tsaro da ke haɗa baki da ’yan ta’adda
Published: 4th, May 2025 GMT
Hedikwatar tsaro ta tabbatar da kama wasu jami’an tsaro huɗu da ke taimakawa ayyukan ta’addanci a yankin Arewa maso Gabas.
Waɗanda ake zargin sun haɗa da wasu jami’ai biyu na rundunar haɗin gwiwa da ke aiki tare da sojoji domin yaƙar ’yan ta’addar.
ISWAP sun kai wa sojoji hari a Yobe An kama masu garkuwa da mutane 3 da kuɓutar da wasuA cewar Darakta mai kula da harkokin yaɗa labarai na tsaro, Manjo Janar Markus Kangye, an kame sojojin ne a wani samame da aka yi tsakanin ranakun 26 zuwa 29 ga watan Afrilu a cikin ƙananan hukumomin Bama, Kukawa, da Madagali.
Ya ce, suna daga cikin waɗanda suke taimakawa ’yan ta’adda huɗu da sojojin suka kama.
Kangye ya nuna damuwarsa kan cin amanar da suke yi, ya kuma gargaɗi kwamandojin da su wayar da kan jami’ansu kan ayyukan da za su kawo cikas ga ƙoƙarin da sojoji ke yi.
“A wani samame da aka gudanar tsakanin ranakun 26-29 ga Afrilu, 2025 a ƙananan hukumomin Bama, Kukawa, da Madagali na Jihohin Borno da Adamawa, sojoji sun kama wasu ’yan ta’adda guda huɗu da ke kai kayan aikin ga mahara, abin baƙin ciki, an tabbatar da cewa biyu daga cikinsu na cikin rundunar haɗin gwiwa.”
Don haka dole ne kwamandoji su wayar da kan jami’an rundunar haɗin gwiwa da su daina haɗa kai da wasu ko ƙarfafa ayyukan ta’addanci da ke da ikon yi wa ayyukanmu zagon ƙasa,” in ji Kangye.
A wani samame kuma, Kangye ya ce sojoji tare da haɗin gwiwar dakarun haɗin gwiwa sun kai farmakin da suka haɗa da sintiri na yaƙi, samame, da aikin share fage a ƙananan hukumomin Gwoza da Dikwa da Bama da Chibok da Gujba da Geidam da kuma Yunusari.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Adamawa Kukawa rewa maso Gabas haɗin gwiwa
এছাড়াও পড়ুন:
An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
Antoni Janar na Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke birnin Yamai a Nijar, ya bayyana cewa an kama tsohon Ministan Harkokin Waje, Ibrahim Yacoubou, bisa zargin hannunsa a cikin wata aika-aika ta kisan kai domin yin tsafi.
A cewar Maazou Oumarou, lamarin ya samo asali ne daga wani binciken ’yan sanda da aka fara gudanarwa tun a ranar 29 ga Yuli, 2025.
KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan NejaYa bayyana cewa, an soma gudanar da binciken ne dangane da yunƙurin kisa a wani yanki da ke wajen birnin Yamai, lamarin da ya kai ga cafke ababen zargin a garin Dosso.
Wani mutum mai suna Mahamadou Noura ne ya bayyana cewa shi ne ya yi yunƙurin kisan, tare da wasu kashe-kashe guda shida da ya aiwatar a baya, bisa umarnin wasu mutane, ciki har da tsohon ministan Ibrahim Yacoubou.
Mutumin ya shaida wa mahukunta cewa ya aikata hakan ne domin yin tsafi da gawarwakin, a madadin wasu mutane da suka haɗa da: Issa Ali Maiga da Ismael Morou Karama da Elhadji Bilya da kuma Issa Seybou Hama.
TRT ya ruwaito cewa tuni dai an cafke duk ababen zargin, yayin da Kotun Ɗaukaka Ƙarar ta umurci ’yan sanda da su ci gaba da bincike tare da ɗaukar ƙarin matakan da za su tabbatar da gaskiya.
Sanarwar ta ce: “Manufar wannan mataki na shari’a ita ce a tattara cikakken rahoto da ke ƙunshe da dukkan abubuwan da suka faru, sannan a miƙa shi ga ɓangaren gurfanarwa.”
Mai shigar da ƙara a ɓangaren gwamnati ya ce, la’akari da girman wannan lamari, wajibi ne a gudanar da bincike cikin gaggawa.
Haka kuma ya buƙaci al’umma da su mutunta ’yancin kotu tare da bayar da cikakken goyon baya domin fayyace gaskiya.
Ana iya tuna cewa, Ibrahim Yacoubou na daga cikin manyan jami’an da aka kama bayan juyin mulkin Nijar na ranar 26 ga Yuli, 2023, sai dai daga bisani an ba shi beli na wucin gadi a cikin watannin baya.