Sojoji sun kama jami’an tsaro da ke haɗa baki da ’yan ta’adda
Published: 4th, May 2025 GMT
Hedikwatar tsaro ta tabbatar da kama wasu jami’an tsaro huɗu da ke taimakawa ayyukan ta’addanci a yankin Arewa maso Gabas.
Waɗanda ake zargin sun haɗa da wasu jami’ai biyu na rundunar haɗin gwiwa da ke aiki tare da sojoji domin yaƙar ’yan ta’addar.
ISWAP sun kai wa sojoji hari a Yobe An kama masu garkuwa da mutane 3 da kuɓutar da wasuA cewar Darakta mai kula da harkokin yaɗa labarai na tsaro, Manjo Janar Markus Kangye, an kame sojojin ne a wani samame da aka yi tsakanin ranakun 26 zuwa 29 ga watan Afrilu a cikin ƙananan hukumomin Bama, Kukawa, da Madagali.
Ya ce, suna daga cikin waɗanda suke taimakawa ’yan ta’adda huɗu da sojojin suka kama.
Kangye ya nuna damuwarsa kan cin amanar da suke yi, ya kuma gargaɗi kwamandojin da su wayar da kan jami’ansu kan ayyukan da za su kawo cikas ga ƙoƙarin da sojoji ke yi.
“A wani samame da aka gudanar tsakanin ranakun 26-29 ga Afrilu, 2025 a ƙananan hukumomin Bama, Kukawa, da Madagali na Jihohin Borno da Adamawa, sojoji sun kama wasu ’yan ta’adda guda huɗu da ke kai kayan aikin ga mahara, abin baƙin ciki, an tabbatar da cewa biyu daga cikinsu na cikin rundunar haɗin gwiwa.”
Don haka dole ne kwamandoji su wayar da kan jami’an rundunar haɗin gwiwa da su daina haɗa kai da wasu ko ƙarfafa ayyukan ta’addanci da ke da ikon yi wa ayyukanmu zagon ƙasa,” in ji Kangye.
A wani samame kuma, Kangye ya ce sojoji tare da haɗin gwiwar dakarun haɗin gwiwa sun kai farmakin da suka haɗa da sintiri na yaƙi, samame, da aikin share fage a ƙananan hukumomin Gwoza da Dikwa da Bama da Chibok da Gujba da Geidam da kuma Yunusari.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Adamawa Kukawa rewa maso Gabas haɗin gwiwa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai
A jawabinsa yayin taron, Gwamna Sani ya gabatar da kasida mai taken: “Gina Haɗin Gwiwa Domin Ci Gaban Kowa”, inda ya bayyana yadda Jihar Kaduna ke ci gaba da samun nasara a fannoni da dama kamar gyaran birane, bunƙasa noma, da tsarin tallafiwa jama’a.
Gwamnan Ya ce tsarin ci gaban jihar yana dogara ne kan faɗaɗa damar tattalin arziki da kare marasa ƙarfi, da ƙarfafa jama’a su samu nasara a rayuwarsu.
Gwamna Uba Sani, ya kuma halarci shirin baje koli na birnin Dubai mai taken : “Sauya Arewa a Nijeriya: Jagoranci, Ƙirƙira, da Tasirin Zamantakewa”, inda nan ma ya jaddada cewa jagoranci mai nagarta da amfani da fasaha a mulki suna da matuƙar muhimmanci wajen buɗe damarmaki ga mutane da birane.
A yayin taron, Gwamnan ya gudanar da wata ganawa ta musamman da Marwan Bin Galita, Darakta Janar na birnin Dubai inda suka tattauna batutuwan haɗin gwiwa a fannin kirkirar makamashin sharar gida da kula da sharar gida ta zamani, da kuma tsare-tsaren gine-ginen birane na zamani.
A ganawar, duk Bangarorin biyu sun amince da zurfafa haɗin kai a fannin fasaha da musayar ƙwarewa domin tallafawa sauyin jihar Kaduna zuwa tattalin arzikin mai ɗorewa.
Gwamna Sani ya bayyana cewa halartar Jihar Kaduna a taron (APCS 2025) na nuna shirin jihar na shiga sahun ƙasashen duniya wajen yin haɗin kai, ƙirƙira, da zama abin koyi a fannin ci gaba mai ɗorewa da ci gaban kowa da kowa a fadin Nijeriya da ma duniya baki ɗaya
ShareTweetSendShare MASU ALAKA