Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026
Published: 3rd, May 2025 GMT
Cibiyar samar da kyakyawan yanayin yin kasuwanci na Fadar Shugaban Kasa da hadaka da NPA ne, suka shirya taron kaddamarwar,
“Ana sa ran a zangon farko na 2026, aikin na NSWP zai fara fara aiki wanda tuni, Fadar Shugaban Kasa ta amince da kwangilar domin a wanzar da aikin,” Inji Dantsoho.
Ya kuma bayar da tabbacin cewa, za a rinka gudanar da ganawa akai-akai da masu ruwa da tsaki domin gudanar da hada-hadar kasuwanci a cikin Tashoshin Jiragen Ruwan kasar a cikin nasara.
Ya sanar da cewa, zuba hannun jari a kayan aiki Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar, samar da kayan aiki na fasahar zamani da sauransu, za su taimaka wajen kara habaka kasa da kuma gudanar da ayyuka, a Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar.
Dantsoho ya kara da cewa, kayan aikin da ke a musamman Tashoshin Jiragen Ruwa na Apapa da Tin Can Island, sun jima ana yin amfani da su a kasar nan, wadanda kuma akwai bukatar a yi masu garanbawul.
“Yau kimanin shekaru 48 ke nan, da kafa Tashar Jirgin Ruwa ta Tin Can Island, inda kuma ta Apapa ta kai kimanin shekaru 100, amma har yanzu, ba a yi masu wani garanbawul ba,” A cewar Dantsoho.
Sai dai, ya sanar da cewa, amincewar kwanan baya da Gwamnatin Tarayya ta yi na a yiwa daukacin Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar garanbawul, hakan zai kara taimakawa wajen gudanar da ayyuka a Tashoshin.
A bangaren kimiyya Shugaban ya bayyana cewa, Hukumar na ci gaba da aiki kafada da kafada da kungiyar kula da harkokin teku ta kasa da kasa wato IMO, domin yin amfani da tsarin PCS, duba da cewa, inda ya alakanta aikin na NSWP, a matsayin wani banban ginshiki.
Dantsoho ya jadda cewa, tsarin na PCS, zai kawar da yin amfani da takardu, da kuma yin shisshigi, wanda hakan zai kuma kara tabbatar da kawar da duk wata badakala da za ta iya kunno kai da rage tsada da kuma kara samar da kudaden shiga.
“Hukumar ta NPA kadai, ba za ta yi cimma burin da ta sanya a gaba sai ba, sai an hada karfi da karfe kuma kara tabbatar da inganci, abu ne da ya karade kowanne fanni, matukar muna son kara samar da karin kudaden shiga wadanda za su yi daidai da na fadin duniya ,” , A cewar Dantsoho.
A na ta jawabin, Darakta Janar ta Kwamitin Gudanar da Muhalli na Kasuwanci na Shugaban kasa (PEBEC) Princess Zahrah Mustapha Audu ta bayyana cewa, inganganta ayyukan, za su taimaka wajen rage cunkson Jiragen Ruwa a Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar.
A cewarta, an kaddmar da Kwamitin ne, domin a samar da sauye-sauye rashin damar da ba a samu a fannin ayyukan Tashihin da kuma kara bunkasa tattalin arzikin kasar nan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar
এছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaidai Dake Kasar Yamen
Majiyar sojojin kasar Yamen sun sanar cewa a ci gaba da hare-haren wuce gona da iri da HKi ke yi, Jiragen yakin HKI sun kai hari kan tashar jirgin ruwan hudaidai dake kasar kuma sun samu nasarar kakkabo makaman.
Kakakin sojin kasar yamen yahya Saree ya fadi a cikin shafinsa na x cewa makaman kariya da muke dasu sun kalubalanci hare haren da Isra’ial ta kai a tashar jirgin ruwa na Hudaida, Isra’ila ta harba makamai masu linzami 12 a tashoshin jiragen ruwanta guda 3.
Gidan rediyo isra’ila ya sanar cewa babban dalilin kai harin shi ne don a hana gudanar da ayyuka na tsawon makwanni, bayan gyara wuraren da suka lalace a hare-haren baya bayan nan da aka kai,
Da Saniya safiye ne sojojin Isra’ila suka sanar da a kawashe tashar jirgin ruwa ta Hudaida inda suka yi barazanar kai hari a tashar a yau.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki Guda 5 A Wajen Taron Kolin kere-kere . September 16, 2025 Iran Ta Bukaci IAEA Tayi Tir Da Harin Da Isra’ila Ta Kai A Tashoshin Nukiyarta. September 16, 2025 Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana September 16, 2025 Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi September 16, 2025 Pezeshkian: Ta’addancin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Kan Kasar Qatar Zalunci Ne Ga Diflomasiyya September 16, 2025 Baqa’i: Kowace Kasa A Duniya Tana Da Hakkin Mallakar Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya September 16, 2025 Kungiyar Human Rights Watch; Isra’ila Ta Kashe ‘Yan Jarida Fiye Da 30 A Kasar Yemen Ne Da Gangan September 16, 2025 Kungiyar Kare Hakkokin Bil’Adama Ta Siriya Ta Bankado Karin Fararen Hula Da Aka Kashe A Rikicin Suweida September 16, 2025 Tawagar Yan Wasan Damben Gargajiya Ta Iran Ta Zama Zakara A Damben Ta Duniya September 16, 2025 An Fara Taron Hukumar Makamashin Nukliya Ta Duniya IAEA Karo Na 69 A Birnin Vienna September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci