Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026
Published: 3rd, May 2025 GMT
Cibiyar samar da kyakyawan yanayin yin kasuwanci na Fadar Shugaban Kasa da hadaka da NPA ne, suka shirya taron kaddamarwar,
“Ana sa ran a zangon farko na 2026, aikin na NSWP zai fara fara aiki wanda tuni, Fadar Shugaban Kasa ta amince da kwangilar domin a wanzar da aikin,” Inji Dantsoho.
Ya kuma bayar da tabbacin cewa, za a rinka gudanar da ganawa akai-akai da masu ruwa da tsaki domin gudanar da hada-hadar kasuwanci a cikin Tashoshin Jiragen Ruwan kasar a cikin nasara.
Ya sanar da cewa, zuba hannun jari a kayan aiki Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar, samar da kayan aiki na fasahar zamani da sauransu, za su taimaka wajen kara habaka kasa da kuma gudanar da ayyuka, a Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar.
Dantsoho ya kara da cewa, kayan aikin da ke a musamman Tashoshin Jiragen Ruwa na Apapa da Tin Can Island, sun jima ana yin amfani da su a kasar nan, wadanda kuma akwai bukatar a yi masu garanbawul.
“Yau kimanin shekaru 48 ke nan, da kafa Tashar Jirgin Ruwa ta Tin Can Island, inda kuma ta Apapa ta kai kimanin shekaru 100, amma har yanzu, ba a yi masu wani garanbawul ba,” A cewar Dantsoho.
Sai dai, ya sanar da cewa, amincewar kwanan baya da Gwamnatin Tarayya ta yi na a yiwa daukacin Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar garanbawul, hakan zai kara taimakawa wajen gudanar da ayyuka a Tashoshin.
A bangaren kimiyya Shugaban ya bayyana cewa, Hukumar na ci gaba da aiki kafada da kafada da kungiyar kula da harkokin teku ta kasa da kasa wato IMO, domin yin amfani da tsarin PCS, duba da cewa, inda ya alakanta aikin na NSWP, a matsayin wani banban ginshiki.
Dantsoho ya jadda cewa, tsarin na PCS, zai kawar da yin amfani da takardu, da kuma yin shisshigi, wanda hakan zai kuma kara tabbatar da kawar da duk wata badakala da za ta iya kunno kai da rage tsada da kuma kara samar da kudaden shiga.
“Hukumar ta NPA kadai, ba za ta yi cimma burin da ta sanya a gaba sai ba, sai an hada karfi da karfe kuma kara tabbatar da inganci, abu ne da ya karade kowanne fanni, matukar muna son kara samar da karin kudaden shiga wadanda za su yi daidai da na fadin duniya ,” , A cewar Dantsoho.
A na ta jawabin, Darakta Janar ta Kwamitin Gudanar da Muhalli na Kasuwanci na Shugaban kasa (PEBEC) Princess Zahrah Mustapha Audu ta bayyana cewa, inganganta ayyukan, za su taimaka wajen rage cunkson Jiragen Ruwa a Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar.
A cewarta, an kaddmar da Kwamitin ne, domin a samar da sauye-sauye rashin damar da ba a samu a fannin ayyukan Tashihin da kuma kara bunkasa tattalin arzikin kasar nan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar
এছাড়াও পড়ুন:
An Yaba Da Kwazon Shugaba Bola Ahmad Tinubu
Masu ruwa da tsakin Arewa sun yaba da kwazon Tinubu, inda suka bukaci a kara karfafa gwiwar ‘yan kasa a taron Kaduna.
Masu ruwa da tsaki a Arewacin Najeriya sun yaba wa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa irin ci gaban da ta samu wajen cika alkawuran zabe, musamman a muhimman batutuwan da suka shafi tsaron kasa, samar da ababen more rayuwa, da sake fasalin tattalin arziki.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun babban darakta na gidauniyar tunawa da Sardaunan Sakkwato Sir Ahmadu Bello, Engr. Abubakar Gambo Umar, kuma ya rabawa manema labarai a karshen taron tattaunawa na kwanaki biyu da aka gudanar a Arewa House, Kaduna.
Ya yaba wa gwamnatin Shugaba Tinubu saboda nuna gaskiya da kuma kyakkyawan aiki, yayin da ta bukaci ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da daidaito, adalci, da hadin gwiwar yanki.
Mahalarta taron sun kuma yaba da irin ci gaban da gwamnatin ta samu kan manyan ayyuka irin su bututun iskar gas na AKK, da aikin hako mai na Kolmani, da kuma ayyukan noman rani na karkara wadanda ke amfana da al’ummar Arewa kai tsaye.
Ya tabbatar da cewa, kawancen ’yan kasa da na gwamnati na da matukar muhimmanci wajen dorewar dimokuradiyya, da hadin kan kasa, da kuma ci gaba mai dorewa.
Har ila yau, ya haifar da damuwa game da matsalolin da ke addabar yara da ba sa zuwa makaranta a Arewa da kuma gaggawar karfafa sarkar darajar noma don samar da ayyukan yi da samar da abinci.
Daga cikin muhimman kudurori, taron ya yi kira da a samar da tsare-tsare na yau da kullum na gwamnati da ‘yan kasa, a matakin kasa da na jihohi.
Har ila yau, ta ba da shawarar inganta harkokin zuba jari a fannin ilimi, musamman don magance tsarin Almajirai da kuma matsalar rashin makaranta da ke addabar Arewacin Nijeriya.
Mahalarta taron sun bayar da shawarar kara hadin gwiwa tsakanin gwamnatocin tarayya da na jihohi, da goyon bayan kishin kasa, dabarun da suka shafi al’umma don sauye-sauyen tattalin arziki da tsaro, tare da karfafa gwiwar kungiyoyin farar hula, na gargajiya, da shugabannin addinai da su kara taka rawa wajen bayar da shawarwarin manufofin jama’a.
Shugaban kungiyar gwamnonin Najeriya kuma gwamnan jihar Kwara Abdulrahman Abdulrazaq ne ya wakilci shugaba Bola Tinubu a wajen taron.
Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya wakilci Dakta Aliyu Modibbo Umar, mai ba da shawara na musamman kan ayyuka na musamman, yayin da gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya kasance babban mai masaukin baki.
Gwamnan jihar Gombe kuma shugaban kungiyar gwamnonin jihohin Arewa, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya halarta a matsayin babban bako na musamman.
Manyan jami’an gwamnatin tarayya sun hada da Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Sanata George Akume, wanda ya jagoranci tawagar. Sauran manyan wadanda suka halarci taron sun hada da mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, mambobin majalisar ministocin tarayya, shugabannin hukumomin tsaro, da manyan jami’an tsaro daga Arewacin Najeriya.
A jawabin da ya gabatar, Farfesa Tijjani Mohammed Bande, ya bayyana yadda Najeriya ke da karfin gwiwa a cikin kalubale kamar rashin tsaro, talauci, da gibin ilimi.
Ya bukaci shugabannin Arewa da su tabbatar da muradun su a cikin tsarin kasa ta hanyar daidaitawa da ingantattun manufofin ci gaba masu amfani ga gamayya.
Babban zaman taron ya tattauna batutuwan da suka shafi kasa baki daya da suka hada da tsaro, shugabanci, farfado da tattalin arziki, noma, samar da ababen more rayuwa, da ci gaban bil Adama.
Adamu Yusuf