Shugaba Bola Tinubu ya yi alƙawarin ƙwato dazuzzuka da sauran yankuna a Arewa-Maso-Yamma da sauran sassan Nijeriya, yayin da yake jawabi a wata liyafa da tsofaffin shugabannin Katsina suka shirya. Ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta ƙara amfani da fasahar sa ido don yaƙar ta’addanci da ƴan fashi.

A cewar sanarwar kakakin shugaban ƙasa, Tinubu ya ce: “Za mu zuba hannun jari a fasaha domin kwato dazuzzuka.

Tsaro batu ne na ƙasa baki ɗaya, ba na yanki ko gunduma kawai ba.” Shugaban ya kuma yi alƙawarin inganta filin jirgin sama na Katsina domin samar da ayyukan yi.

Gidauniyar TY Buratai Ta Yi Kira Ga Tinubu Ya Ƙarawa Ma’aikata Albashi Kasar Sin Ta Goyi Bayan Rawar Da Hukumar IAEA Ke Takawa Wajen Warware Batun Nukiliyar Iran Ta Hanyar Diflomasiyya

Gwamna Dikko Radda na Katsina ya bayyana cewa jihar ta kafa wani tsarin tsaro na musamman don tattara bayanan sirri, yana mai cewa inganta filin jirgin saman zai samar da ayyukan yi ga mutane 2,700. Tsohon gwamna Aminu Masari ya yaba wa shugaban saboda naɗa ‘yan asalin jihar a muƙamai mabambanta a gwamnatin tarayya.

Tinubu ya kuma yi godiya ga gwamnonin jihohin Kaduna, Jigawa, Borno, Benue, Yobe, Sokoto da Kwara da suka halarci bikin auren ‘yarsa da ƙaddamar da ayyukan gwamnati a Katsina. Ya kuma yaba wa tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari a matsayin mutum mai gaskiya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Radda Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

HOTUNA: Yadda aka tarbi Shugaba Tinubu a Katsina

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya isa Jihar Katsina domin ziyarar aiki ta kwana biyu, inda zai ƙaddamar da wasu ayyuka da gwamnatin jihar ta yi.

Gwamnan Jihar Katsina Dikko Radda, da tsohon Gwamna jihar Bello Masari na cikin manyan mutanen da suka tarɓe shi tun daga filin jirgin Umaru Musa.

Tinubu zai yi shekara takwas yana mulki – Afenifere Yadda aka yi bikin yaye sabbin matuƙa jiragen Rundunar Sojin Saman Najeriya

Bayan isarsa ne kuma ya yi wa rundunar sojin ƙasar jawabi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shettima zai halarci bikin rantsar da sabon shugaban ƙasar Gabon
  • Shettima zai tafi Gabon bikin rantsar da sabon shugaban ƙasar
  • Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon
  • Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
  • HOTUNA: Yadda aka tarbi Shugaba Tinubu a Katsina
  • Tinubu zai yi shekara takwas yana mulki – Afenifere
  • Seyi Tinubu Ya Musunta Zargin Kamawa Da Bayar Da Cin Hanci Ga Shugaban NANS
  • Ra’ayin Jama’a kan ziyarar Tinubu Katsina
  • Tinubu Ba Ya Tsoma Baki A Ayyukan EFCC – Olukoyede