Shugaba Bola Tinubu ya yi alƙawarin ƙwato dazuzzuka da sauran yankuna a Arewa-Maso-Yamma da sauran sassan Nijeriya, yayin da yake jawabi a wata liyafa da tsofaffin shugabannin Katsina suka shirya. Ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta ƙara amfani da fasahar sa ido don yaƙar ta’addanci da ƴan fashi.

A cewar sanarwar kakakin shugaban ƙasa, Tinubu ya ce: “Za mu zuba hannun jari a fasaha domin kwato dazuzzuka.

Tsaro batu ne na ƙasa baki ɗaya, ba na yanki ko gunduma kawai ba.” Shugaban ya kuma yi alƙawarin inganta filin jirgin sama na Katsina domin samar da ayyukan yi.

Gidauniyar TY Buratai Ta Yi Kira Ga Tinubu Ya Ƙarawa Ma’aikata Albashi Kasar Sin Ta Goyi Bayan Rawar Da Hukumar IAEA Ke Takawa Wajen Warware Batun Nukiliyar Iran Ta Hanyar Diflomasiyya

Gwamna Dikko Radda na Katsina ya bayyana cewa jihar ta kafa wani tsarin tsaro na musamman don tattara bayanan sirri, yana mai cewa inganta filin jirgin saman zai samar da ayyukan yi ga mutane 2,700. Tsohon gwamna Aminu Masari ya yaba wa shugaban saboda naɗa ‘yan asalin jihar a muƙamai mabambanta a gwamnatin tarayya.

Tinubu ya kuma yi godiya ga gwamnonin jihohin Kaduna, Jigawa, Borno, Benue, Yobe, Sokoto da Kwara da suka halarci bikin auren ‘yarsa da ƙaddamar da ayyukan gwamnati a Katsina. Ya kuma yaba wa tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari a matsayin mutum mai gaskiya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Radda Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu zai je jaje bayan kisan fiye da mutum 100 a Benuwe

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya soke ziyarar aiki da ya shirya zuwa Kaduna, a maimakon haka zai ziyarci Jihar Benuwe domin jajanta wa al’umma sakamakon kashe-kashen da aka samu a jihar a baya-bayan nan.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasar, Bayo Onanuga ya fitar a ranar Litinin.

Gwamnati ta kasa ɗaukar matakin da ya dace a kan kashe-kashen Benuwe — Atiku Tinubu ya bayar da umarnin binciken hare-haren Benuwe

Kakakin ya ce Shugaba Tinubu zai kai ziyarar ce a ranar Laraba domin duba halin da jihar ke ciki bayan kashe-kashen da aka samu a ’yan kwanakin nan a jihar.

Haka kuma, a yayin ziyarar, shugaba Tinubu zai gana da masu ruwa da tsaki da suka haɗa da sarakuan gargajiya da ’yan siyasa da jagororin addini da shugabannin al’umma da kungiyoyin matasa, da nufin lalubo hanyoyin magance rikicin jihar.

Tuni dai shugaban ya aike da tawagar wakilan Gwamnatin Tarayya a yau da ta ƙunshi Sakataren Gwamnatin Tarayya da Babban Sufeton ’yan sanda da shugabannin hukumomin tattara bayanan sirri ta ƙasa da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro da shugabannin kwamitsocin tsaro a majalisun dokokin ƙasar.

Fadar shugaban kasar ta ce wata babbar tawagar manyan jami’an tsaron Nijeriya ta isa Jihar Benuwe domin bayar umarnin yadda za a tunkari matsalar rashin tsaron da jihar ke fuskanta da kuma mai do da kwanciyar hankali.

A ƙarshen mako ne dai aka samu munanan hare-haren da suka yi sanadin kashe fiye da mutum 100 a Jihar Benuwe.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mun shirya yin sulhu da ’yan bindiga — Gwamnatin Sakkwato
  • Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a
  • Majalisa ta aike wa Tinubu kudurorin dokar haraji domin ya rattaba musu hannu
  • Buni ya bai wa manoma 1,000 tallafin aikin gona
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina
  • Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas
  • Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga
  • Dan shekara 10 ya kashe mahaifinsa ɗan sanda da bindiga
  • Sojoji Sun Damƙe Ɗan Fashi, Sun Kwato Makamai A Kaduna Da Filato
  • Tinubu zai je jaje bayan kisan fiye da mutum 100 a Benuwe