Aminiya:
2025-05-03@21:14:40 GMT

Shettima zai tafi Gabon bikin rantsar da sabon shugaban ƙasar

Published: 3rd, May 2025 GMT

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, zai bar Abuja yau zuwa Libreville, babban birnin ƙasa Gabon, domin ya wakilci Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a bikin rantsar da zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasa, Brice Clotaire Oligui Nguema.

A halin yanzu Shugaba Tinubu yana ziyara ta kwanaki biyu a Jihar Katsina.

A cewar Stanley Nkwocha, mai magana da yawun Mataimakin Shugaban Kasa, Najeriya na goyon bayan sauyin mulki na dimokuraɗiyya cikin lumana a ƙasar Gabon kuma ta sake tabbatar da ƙudirinta na inganta dimokuraɗiyya a Afirka.

Oligui Nguema, wanda ya kasance shugaban riƙon ƙwarya na Gabon tun watan Agustan 2023, ya lashe zaɓen shugaban ƙasar da aka gudanar a ranar 12 ga Afrilu, inda ya samu kashi 94.85% na ƙuri’un da aka kaɗa.

Rashin tsaro: ‘Ba za mu miƙa wuya ga ’yan ta’adda ba’ Yadda sojoji suka kashe manyan ’yan bindiga 5 a Zamfara

’Yan takara bakwai ne suka fafata, inda tsohon Firayim Minista Alain Claude Bilie-By-Nze ya zo na biyu da kashi 3%.

Ana sa ran Shettima zai dawo Najeriya bayan bikin rantsarwar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dimokuraɗiyya

এছাড়াও পড়ুন:

Seyi Tinubu Ya Musunta Zargin Kamawa Da Bayar Da Cin Hanci Ga Shugaban NANS

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Yi Alƙawarin Kwato Dazuzzuka Daga Hannun Ƴan Bindiga
  • Shettima zai halarci bikin rantsar da sabon shugaban ƙasar Gabon
  • Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon
  • Tinubu zai yi shekara takwas yana mulki – Afenifere
  • Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Gabon
  • Seyi Tinubu Ya Musunta Zargin Kamawa Da Bayar Da Cin Hanci Ga Shugaban NANS
  • An Bude Kashi Na Uku Na Canton Fair Karo Na 137 
  • Mataimakin Gwamnan Neja Ya Ki Halartar Bikin Ranar Ma’aikata, Ana Zargin Akwai Takun Saka
  • Arif: A Shirye Muke Mu Sabunta Sana’o’in Sudan