Aminiya:
2025-06-18@18:20:18 GMT

Rashin tsaro: Ba za mu miƙa wuya ga ’yan ta’adda ba — Tinubu

Published: 3rd, May 2025 GMT

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya buƙaci sojoji da su ƙara ƙaimi wajen kawo ƙarshen matsalar tsaro da ke addabar Najeriya yana mai jaddada alkawarin cewa ƙasar ba za ta miƙa wuya ga ’yan ta’adda ba.

Da yake jawabi ga sojojin a lokacin ziyararsa a Katsina, Shugaba Tinubu ya nuna damuwa game da ƙalubalen tsaron da ake fuskanta a ƙasar a halin yanzu, inda ya bayyana su a matsayin wani lokaci mai muhimmanci a tarihin Najeriya.

Tinubu ya yi kira da a nuna jajircewa wajen kare ikon Najeriya da kuma dawo da zaman lafiya a faɗin ƙasar.

Ya tabbatar wa sojojin da kudirinsa na kula da jin daɗinsu, inda ya yi alƙawarin biyan alawus-alawus a kan lokaci, tabbatar da kula da lafiya, da kuma tallafa wa iyalansu.

2027: Mene ne mafita ga ’yan adawa? Yadda sojoji suka kashe manyan ’yan bindiga 5 a Zamfara

Ya jaddada jarumtaka da sadaukarwarsu, yana mai cewa su ne “garkuwar Najeriya.” Ya jaddada cewa yaƙin ba wai kawai na yankuna ba ne, har ma da yaƙin neman ran kasar.

Tinubu ya tabbatar da ƙudirin gwamnatinsa na tallafa wa sojoji da ayyuka da zuba jari, yana mai gargaɗin masu kawo cikas na cikin gida da na waje cewa Najeriya ba za ta miƙa wuya ba.

Ziyarar tasa ta kuma hada da ƙaddamar da titin mota mai hannu biyu mai tsawon kilomita 24 da cibiyar aikin gona ta zamani a Katsina.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Najeriya Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Damƙe Ɗan Fashi, Sun Kwato Makamai A Kaduna Da Filato

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun raunata shugaban ISWAP na Najeriya, Albarnawi
  • Litar fetur za ta iya komawa N1,000 a Najeriya saboda yakin Isra’ila-Iran – Masana
  • DAGA LARABA: Ko Kare Kai Daga Harin ‘Yan Ta’adda Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro?
  • Jirgin alhazai ya yi saukar gaggawa kan barazanar harin bom
  • Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Cin Ganyayyaki Ke Yi Wa ‘Yan Najeriya Wahala
  • Sojoji Sun Damƙe Ɗan Fashi, Sun Kwato Makamai A Kaduna Da Filato
  • Gwamnati ta kasa ɗaukar matakin da ya dace a kan kashe-kashen Benuwe — Atiku
  • FCCPC Ta Sammaci Air Peace Kan Rashin Maido Da Kuɗin Tikitin Jirgin Da Aka Soke Tafiyarsa
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Durƙushewar Sababbin Sana’o’i Tun Ba A Je Ko’ina Ba