Aminiya:
2025-06-18@11:50:50 GMT

Yadda sojoji suka kashe manyan ’yan bindiga 5 a Zamfara

Published: 3rd, May 2025 GMT

Sojoji sun hallaka wasu manyan ’yan ta’adda tare da yaransu masu yawan gaske a wata arangama a Ƙaramar Hukumar Talata Mafara da ke Jihar Zamfara.

Shugabannin ’yan bindiga da suka haɗa da Auta Jijji da Dankali da Sagidi da Kachallah Rijaji da kuma Kachallah Suza sun sheƙa lahira ne a yayin musayar wuta da sojojin a ranar Alhamis.

Kakakin Birget na 1 ta Sojin Ƙasa ta Najeriya, Kyaftin Suleiman Omale, ya ce sojojin sun ƙaddamar da aikin ne bayan samun rahoton cewa ’yan bindiga sun kai hari ƙauyen Mai Kwanugga inda suke ta ƙone gidajen al’umma.

Ya bayyana cewa, “dakarun da ke sintiri suka yi artabu da dandazon ’yan bindiga, inda a yayin musayar wuta suka kashe shugabannin ’yan bindiga biyar da wasu da dama.”

Yadda aka yi bikin yaye sabbin matuƙa jiragen Rundunar Sojin Saman Najeriya Ra’ayin Jama’a kan ziyarar Tinubu Katsina Sarki Sanusi II ya naɗa sabon Galadiman Kano da wasu 4

Ya ƙara da cewa sojojin sun bi sawun ’yan bindigar da suka tsere inda suka ƙwato manyan bindigogi guda shida da bama-bamai da kuma harsasai iri-iri.

Washegari kuma a yayin da sojojin ke ci gaba aiki, mazauna yankin sun mika musu wasu ƙarin makaman da ’yan bindigar suka tsere suka bari.

Kyaftin Omale ya bayyana cewa fararen hula biyu sun samu raunin harbi a yayin musayar wuta amma suna samun kulawa a asibiti, a yayin da ake ci gaba a aikin gamawa da ragowar ’yan ta’addan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Arangama jagororin yan bindiga musayar wuta Zamfara yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Hafsan Soji Ya Ƙalubalanci Sabbin Sojoji Da Su Shirya Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda

“Yayin da kuka fita a yau kuma kuka samu matsayinku a wannan ma’aikata mai daraja, ku sani cewa za ku zama wani bangare na hanyoyin magance kalubalen ta’addanci da ‘yan tada kayar baya acikin al’ummarmu, don haka duk inda aka tura ku, tilas ne ku aiwatar da abinda aka horar da ku, kuma ku nuna jajircewa wajen fuskantar matsaloli.

 

“Tafiyar mil dubu tana farawa ne da taku daya, don haka, tafiyarku ta fara ne a ranar 13 ga watan Janairun 2025, lokacin da kuka fara amsar horo na aikin soji, an shirya muku duk wani abu da za ku iya fuskanta na kalubale, kuma ina mai tabbatar muku da cewa, za ku fuskanci kalubalen da da farko zaku ga kamar ba za a iya shawo kansu ba. Amma kuna jajircewa, sai su zama tarihi”. In ji shi

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama
  • Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina
  • Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas
  • Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga
  • Dan shekara 10 ya kashe mahaifinsa ɗan sanda da bindiga
  • An Daddale Tarin Yarjejeniyoyi Yayin Taron Baje Kolin Harkokin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Sojojin Isra’ila Sun Kashe Kananan Yara Masu Yawa A Iran
  • Iran Ta Cilla Makamai Kan HKI Da Rana A Karon Farko A Yau Lahadi
  • Babban Hafsan Soji Ya Ƙalubalanci Sabbin Sojoji Da Su Shirya Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda