Aminiya:
2025-05-03@19:23:11 GMT

Yadda sojoji suka kashe manyan ’yan bindiga 5 a Zamfara

Published: 3rd, May 2025 GMT

Sojoji sun hallaka wasu manyan ’yan ta’adda tare da yaransu masu yawan gaske a wata arangama a Ƙaramar Hukumar Talata Mafara da ke Jihar Zamfara.

Shugabannin ’yan bindiga da suka haɗa da Auta Jijji da Dankali da Sagidi da Kachallah Rijaji da kuma Kachallah Suza sun sheƙa lahira ne a yayin musayar wuta da sojojin a ranar Alhamis.

Kakakin Birget na 1 ta Sojin Ƙasa ta Najeriya, Kyaftin Suleiman Omale, ya ce sojojin sun ƙaddamar da aikin ne bayan samun rahoton cewa ’yan bindiga sun kai hari ƙauyen Mai Kwanugga inda suke ta ƙone gidajen al’umma.

Ya bayyana cewa, “dakarun da ke sintiri suka yi artabu da dandazon ’yan bindiga, inda a yayin musayar wuta suka kashe shugabannin ’yan bindiga biyar da wasu da dama.”

Yadda aka yi bikin yaye sabbin matuƙa jiragen Rundunar Sojin Saman Najeriya Ra’ayin Jama’a kan ziyarar Tinubu Katsina Sarki Sanusi II ya naɗa sabon Galadiman Kano da wasu 4

Ya ƙara da cewa sojojin sun bi sawun ’yan bindigar da suka tsere inda suka ƙwato manyan bindigogi guda shida da bama-bamai da kuma harsasai iri-iri.

Washegari kuma a yayin da sojojin ke ci gaba aiki, mazauna yankin sun mika musu wasu ƙarin makaman da ’yan bindigar suka tsere suka bari.

Kyaftin Omale ya bayyana cewa fararen hula biyu sun samu raunin harbi a yayin musayar wuta amma suna samun kulawa a asibiti, a yayin da ake ci gaba a aikin gamawa da ragowar ’yan ta’addan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Arangama jagororin yan bindiga musayar wuta Zamfara yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

An gano shanu 25 da suka ɓace a dajin Sakkwato

Hedikwatar ’yan sandan Gada da ke Jihar Sakkwato ta gano wasu shanu 25 da ake zargin an sace ko kuma sun ɓace daga hannun masu su.

An gano dabbobin ne a wani dajin da ke kan iyaka da ƙaramar hukumar Sabon Birni ta jihar a ranar Alhamis, bayan da hukumomin yankin suka samu labarin.

’Yan kungiyar asiri: Mutum 95 sun shiga hannu a Edo Shettima zai halarci bikin rantsar da sabon shugaban ƙasar Gabon

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar, Ahmad Rufa’i ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a, inda ya ce an gano dabbobin ne bayan da Alhaji Muhammad Kyari ya bayar da rahoton cewa akwai shanun da suka ɓace.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Hakimin Gada, Alhaji Idi ‘M, tsohon Hakimin garin Gidan Rabami da ke ƙaramar Hukumar Gada, a baya ya sanar da hukuma game da wasu baƙin shanu a wani dajin da ke kusa.

“An gano dabbobin ne a wani dajin da ke da iyaka da ƙaramar hukumar Sabon Birni, yankin da ya shahara da sarƙaƙiya da kuma ƙalubalen tsaro a wasu lokuta.

“Rundunar ’yan sanda ta Gada ta mayar da martani cikin gaggawa, inda ta tura jami’anta zuwa wurin da aka yi nasarar ƙwato shanu 25 ba tare da wata matsala ba.”

Sanarwar ta ci gaba da cewa, bayan kuɓutar da su an kai shanun zuwa hedikwatar Gada, inda ake tsare da su cikin ƙoshin lafiya.

Rundunar ’yan sandan ta yi kira ga masu dabbobin da suka rasa shanunsu da su ziyarci hedikwatar tare da ingantacciyar hujjar mallakar su domin tantancewa tare karɓarsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin: Adadin Tafiye-tafiye Yayin Ranakun Hutun Murnar Ranar ‘Yan Kwadago Ta Duniya Ya Kafa Tarihi 
  • An gano shanu 25 da suka ɓace a dajin Sakkwato
  • Tinubu Ya Yi Alƙawarin Kwato Dazuzzuka Daga Hannun Ƴan Bindiga
  • Sojojin Isra’ila sun kaddamar da sabbin hare-hare kan Siriya
  • Falasdinawa 40 Ne suka Yi Shahada A Zirin Gaza Sakamakon Ta’addancin Sojojin Mamayar Isra’ila A Jiya Juma’a
  • Wutar Lantarki Ta Kashe Mutum 112, Wasu 108 Sun Jikkata A 2024
  • Zamfara Ta Biya Sama Da Naira Biliyan 13 A Matsayin Bashin Garatuti Da Aka Gada – Mataimakin Gwamna.
  • Al’umma Sun Shiga Fargaba Yayin Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Sun Kashe Limamin Da Suka Sace A Zamfara
  • Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe