Kungiyar kwadago ta Nijeriya NLC reshen jihar Kano ta yabawa gwamnatin jihar Kano kan kudirin ta na daidaita bashin da ake bin ‘yan fansho da ya haura naira biliyan 16.

 

 

 

Da yake jawabi yayin bikin ranar ma’aikata da aka gudanar a filin wasa na Sani Abacha da ke kofar Mata a Kano, shugaban kungiyar kwadago ta NLC, Kwamared Kabiru Inuwa, ya bukaci ma’aikatan Nijeriya da su jajirce wajen tabbatar da adalci da walwala.

 

 

Kwamared Inuwa ya bayyana cewa duk da nasarorin da gwamnatin ta samu wajen horas da ma’aikata, har yanzu akwai bukatar karin ma’aikata masu tallafawa a ma’aikatun gwamnati da na kananan hukumomi.

 

 

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jaddada kudirin gwamnatin sa na samar da yanayi mai kyau ga ma’aikatan gwamnati.

 

 

“Duk da kalubalen tattalin arziki, gwamnatin jihar na tabbatar da biyan albashin ma’aikata a kan lokaci domin kara kwarin gwiwar ma’aikata don samar da ingantaccen aiki.”

 

Gwamnan ya bayyana cewa gwamnatinsa ta farfado da ma’aikatan jihar Kano ta hanyar bin ka’idojinta da tsarin aiki.

 

 

Gwamna Yusuf ya jadadda cewa, bisa fifikon da aka ba wa garambawul na fansho a jihar, shaida ce karara na jajircewar gwamnatin na ganin cewa kokarin da sadaukarwar da manyan ‘yan kasa ke yi ba a bar su a banza ba.

 

 

Ya bukaci ma’aikata da su mayar da biki ga kokarin gwamnati ta hanyar sadaukar da kai da jajircewa wajen gudanar da ayyukan da aka dora musu.

 

A yayin bikin wakilan kungiyoyin kwadago daban-daban sun gudanar da fareti mai ban sha’awa don murnar zagayowar ranar ma’aikata.

 

Taron ya samu halartar gwamna Abba Kabir Yusuf, mataimakinsa, yan majalisar zartarwa na Kano, shugaban kungiyar da sauran masu ruwa da tsaki.

 

 

Cover /Abdullahi jalaluddeen/Kano

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu zai je jaje bayan kisan fiye da mutum 100 a Benuwe

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya soke ziyarar aiki da ya shirya zuwa Kaduna, a maimakon haka zai ziyarci Jihar Benuwe domin jajanta wa al’umma sakamakon kashe-kashen da aka samu a jihar a baya-bayan nan.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasar, Bayo Onanuga ya fitar a ranar Litinin.

Gwamnati ta kasa ɗaukar matakin da ya dace a kan kashe-kashen Benuwe — Atiku Tinubu ya bayar da umarnin binciken hare-haren Benuwe

Kakakin ya ce Shugaba Tinubu zai kai ziyarar ce a ranar Laraba domin duba halin da jihar ke ciki bayan kashe-kashen da aka samu a ’yan kwanakin nan a jihar.

Haka kuma, a yayin ziyarar, shugaba Tinubu zai gana da masu ruwa da tsaki da suka haɗa da sarakuan gargajiya da ’yan siyasa da jagororin addini da shugabannin al’umma da kungiyoyin matasa, da nufin lalubo hanyoyin magance rikicin jihar.

Tuni dai shugaban ya aike da tawagar wakilan Gwamnatin Tarayya a yau da ta ƙunshi Sakataren Gwamnatin Tarayya da Babban Sufeton ’yan sanda da shugabannin hukumomin tattara bayanan sirri ta ƙasa da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro da shugabannin kwamitsocin tsaro a majalisun dokokin ƙasar.

Fadar shugaban kasar ta ce wata babbar tawagar manyan jami’an tsaron Nijeriya ta isa Jihar Benuwe domin bayar umarnin yadda za a tunkari matsalar rashin tsaron da jihar ke fuskanta da kuma mai do da kwanciyar hankali.

A ƙarshen mako ne dai aka samu munanan hare-haren da suka yi sanadin kashe fiye da mutum 100 a Jihar Benuwe.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu Garkuwa Da Mutane Sun Dira Jihar Kogi, Sun Sace Wani Basarake
  • Sin Ta Fatattaki Laifukan Zamba Ta Shafin Intanet 294,000 A Bara
  • Masu Garkuwa Da Mutane Sun Dira Jihar Kogi, Sun Sace Mutane 1
  • Tinubu zai je jaje bayan kisan fiye da mutum 100 a Benuwe
  • Gwamnati ta kasa ɗaukar matakin da ya dace a kan kashe-kashen Benuwe — Atiku
  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • Oman ta tabbatar da soke tattaunawar Iran da Amurka zagaye na shida
  • Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
  • Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba