NLC Kano Ta Yabawa Gwamnati Na Kokarin Kyautata Jin Dadin Ma’aikata
Published: 2nd, May 2025 GMT
Kungiyar kwadago ta Nijeriya NLC reshen jihar Kano ta yabawa gwamnatin jihar Kano kan kudirin ta na daidaita bashin da ake bin ‘yan fansho da ya haura naira biliyan 16.
Da yake jawabi yayin bikin ranar ma’aikata da aka gudanar a filin wasa na Sani Abacha da ke kofar Mata a Kano, shugaban kungiyar kwadago ta NLC, Kwamared Kabiru Inuwa, ya bukaci ma’aikatan Nijeriya da su jajirce wajen tabbatar da adalci da walwala.
Kwamared Inuwa ya bayyana cewa duk da nasarorin da gwamnatin ta samu wajen horas da ma’aikata, har yanzu akwai bukatar karin ma’aikata masu tallafawa a ma’aikatun gwamnati da na kananan hukumomi.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jaddada kudirin gwamnatin sa na samar da yanayi mai kyau ga ma’aikatan gwamnati.
“Duk da kalubalen tattalin arziki, gwamnatin jihar na tabbatar da biyan albashin ma’aikata a kan lokaci domin kara kwarin gwiwar ma’aikata don samar da ingantaccen aiki.”
Gwamnan ya bayyana cewa gwamnatinsa ta farfado da ma’aikatan jihar Kano ta hanyar bin ka’idojinta da tsarin aiki.
Gwamna Yusuf ya jadadda cewa, bisa fifikon da aka ba wa garambawul na fansho a jihar, shaida ce karara na jajircewar gwamnatin na ganin cewa kokarin da sadaukarwar da manyan ‘yan kasa ke yi ba a bar su a banza ba.
Ya bukaci ma’aikata da su mayar da biki ga kokarin gwamnati ta hanyar sadaukar da kai da jajircewa wajen gudanar da ayyukan da aka dora musu.
A yayin bikin wakilan kungiyoyin kwadago daban-daban sun gudanar da fareti mai ban sha’awa don murnar zagayowar ranar ma’aikata.
Taron ya samu halartar gwamna Abba Kabir Yusuf, mataimakinsa, yan majalisar zartarwa na Kano, shugaban kungiyar da sauran masu ruwa da tsaki.
Cover /Abdullahi jalaluddeen/Kano
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato
Yayin da yajin aikin gargadi na kasa baki daya da kungiyar ma’aikatan jinya da ungozoma ta kasa (NANNM) ta kira ya shiga rana ta biyu, iyalai sun fara kwashe ‘yan uwansu daga asibitocin gwamnati zuwa masu zaman kansu a jihar Filato. A Asibitin Kwararru na Jihar Filato, dogon layin masu amsar katin asibiti don neman kulawa da lafiyarsu ya yi batan dabo a lokacin da wakilinmu ya ziyarci asibitin. Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka Wata mata mai suna Misis Mary David, wacce ta yi rajista a asibitin duba lafiyar mata masu juna biyu, ta shaida wa wakilinmu cewa babu ma’aikatan jinya da za su duba ta da sauran wadanda aka shirya za a duba su a ranar Alhamis. Da aka tambaye ta game da matakin da za ta dauka na gaba, Misis David ta ce za ta koma gida har sai an dakatar da yajin aikin. Mista Nde Danladi John daga karamar hukumar Kanke wanda shi ma ya zo ya kwashe iyalinsa, ya ce babu wanda ya duba su a asibiti tun ranar Laraba. Haka kuma, a sashen kula da lafiya na matakin farko na Jos ta Arewa da Jos ta Kudu, ba a ga wata ma’aikaciyar jinya da ke kula da marasa lafiya ba yayin da likitan da ke bakin aiki ya halarci wasu tsirarun marasa lafiya, ya ce sauran su dawo ranar Juma’a. Wakilinmu ya ruwaito cewa, yajin aikin da aka fara da tsakar daren ranar 30 ga watan Yuli, 2025, ya janyo janyewar ma’aikatan jinya da ungozoma baki daya a dukkanin cibiyoyin lafiya na tarayya da ke fadin kasar nan.Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp