NLC Kano Ta Yabawa Gwamnati Na Kokarin Kyautata Jin Dadin Ma’aikata
Published: 2nd, May 2025 GMT
Kungiyar kwadago ta Nijeriya NLC reshen jihar Kano ta yabawa gwamnatin jihar Kano kan kudirin ta na daidaita bashin da ake bin ‘yan fansho da ya haura naira biliyan 16.
Da yake jawabi yayin bikin ranar ma’aikata da aka gudanar a filin wasa na Sani Abacha da ke kofar Mata a Kano, shugaban kungiyar kwadago ta NLC, Kwamared Kabiru Inuwa, ya bukaci ma’aikatan Nijeriya da su jajirce wajen tabbatar da adalci da walwala.
Kwamared Inuwa ya bayyana cewa duk da nasarorin da gwamnatin ta samu wajen horas da ma’aikata, har yanzu akwai bukatar karin ma’aikata masu tallafawa a ma’aikatun gwamnati da na kananan hukumomi.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jaddada kudirin gwamnatin sa na samar da yanayi mai kyau ga ma’aikatan gwamnati.
“Duk da kalubalen tattalin arziki, gwamnatin jihar na tabbatar da biyan albashin ma’aikata a kan lokaci domin kara kwarin gwiwar ma’aikata don samar da ingantaccen aiki.”
Gwamnan ya bayyana cewa gwamnatinsa ta farfado da ma’aikatan jihar Kano ta hanyar bin ka’idojinta da tsarin aiki.
Gwamna Yusuf ya jadadda cewa, bisa fifikon da aka ba wa garambawul na fansho a jihar, shaida ce karara na jajircewar gwamnatin na ganin cewa kokarin da sadaukarwar da manyan ‘yan kasa ke yi ba a bar su a banza ba.
Ya bukaci ma’aikata da su mayar da biki ga kokarin gwamnati ta hanyar sadaukar da kai da jajircewa wajen gudanar da ayyukan da aka dora musu.
A yayin bikin wakilan kungiyoyin kwadago daban-daban sun gudanar da fareti mai ban sha’awa don murnar zagayowar ranar ma’aikata.
Taron ya samu halartar gwamna Abba Kabir Yusuf, mataimakinsa, yan majalisar zartarwa na Kano, shugaban kungiyar da sauran masu ruwa da tsaki.
Cover /Abdullahi jalaluddeen/Kano
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
Haka kuma, wannan na faruwa ne makonni biyu bayan yin garkuwa da Pastor Friday Adehi na Christian Evangelical Fellowship of Nigeria (CEFN) tare da wani abokin cocinsa bayan kammala wa’azi. Wannan ya kara nuna yadda matsalar garkuwa ke ta’azzara a yankin Kogi East.
A gefe guda, kungiyar lauyoyi ta Najeriya (NBA), reshen Idah, ta bukaci gwamnati a matakai daban-daban da ta dauki matakan gaggawa don kawo karshen satar mutane a jihar. Shugaban kungiyar, Barr. James Michael, ya ce yawaitar garkuwa a kan titunan yankin ya jefa rayukan jama’a cikin hatsari, don haka gwamnati ya kamata ta dauki tsauraran matakai domin kare lafiyar al’umma.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp