Gwamnatin jihar Kebbi, ta baiwa ma’aikatan jihar tabbacin ci gaba da jajircewa wajen kyautata jin dadin su da kuma kare hakkokinsu.

 

Gwamna Nasir Idris wanda ya ba da wannan tabbacin a lokacin da yake jawabi ga ma’aikata domin bikin ranar watan Mayu a Birnin Kebbi, ya jaddada cewa ma’aikata aminai ne masu kima wajen ci gaban jihar Kebbi, kuma su kasance masu ruwa da tsaki da ba za a yi watsi da su ba.

 

Gwamna Idris, wanda ya bayyana bikin ranar Mayu a matsayin wani muhimmin lokaci, ya yabawa ma’aikatan bisa jajircewarsu da irin gagarumar gudunmawar da suke bayarwa wajen ci gaban jihar.

 

“Kwazonku da jajircewarku sune kashin bayan tattalin arzikinmu. Ina yaba muku kan kokarinku na jajircewa”.

 

Gwamna Idris, ya kuma amince da kalubalen da ma’aikatan jihar ke fuskanta tare da ba su tabbacin gwamnatinsa ta kudiri aniyar magance wadannan matsalolin.

 

A yayin da yake taya kungiyar kwadago ta Najeriya NLC da TUC murnar zagayowar ranar ma’aikata, Gwamna Idris ya nuna jin dadinsa ga kungiyar ‘yan kasuwa bisa jajircewar da suke yi na kyautata jin dadin ma’aikata sannan ya bukaci ma’aikata da su ci gaba da jajircewa wajen gudanar da ayyukansu tare da ci gaba da ciyar da jihar gaba.

 

Tun da farko a nasa jawabin, shugaban kungiyar kwadago ta kasa (NLC) na jihar, Kwamared Murtala Usman, ya bayyana jin dadinsa a madadin kungiyoyin NLC da TUC bisa yadda Gwamnan ya ba da kulawar da yake yi wajen kyautata jin dadin ma’aikata da ci gaban su.

 

Kwamared Usman ya yaba da irin goyon bayan da Gwamnan ke ci gaba da baiwa ma’aikata, inda ya bayyana halartan taron bikin ranar Mayun 2025 kamar yadda aka zata duba da tarihinsa a matsayinsa na tsohon dan kungiyar kwadago da kuma tsohon shugaban kwadago.

 

Muhimman abubuwan da suka wakana a wajen taron sun hada da fareti da ma’aikata suka yi, da bayar da lambar yabo ga gwamna Idris da kungiyar dalibai ta kasa (NANS) reshen jihar Kebbi da kungiyar ma’aikatan jinya ta kasa suka yi.

 

Shugabannin kungiyar NLC na jihar sun kuma mika kyautuka ga wasu fitattun mutane bisa gudunmawar da suka bayar wajen ci gaban jihar Kebbi.

 

COV/ Abdullahi Tukur

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Gwamna Idris jihar Kebbi

এছাড়াও পড়ুন:

’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina

An ceto dukkanin mutane 14 ba tare da wani ya ji rauni ba, amma abin baƙin ciki, wani matashi ɗan shekara 27 mai suna Abba daga garin Funtua ya rasa ransa kafin isowar ’yansanda.

A wani lamari da ya faru a ranar 28 ga watan Yuli da misalin ƙarfe 11:27 na dare, an sake kiran ’yansanda daga ƙauyen Zagaizagi, inda aka sanar da su cewa wasu ’yan bindiga sum hari tare da sace wasu mutane ƙauyen.

’Yansanda sun isa wajen suka gwabza da ’yan bindigar, kuma sun samu nasarar ceto wasu mutane 14 da kuma ƙwato shanun da aka sace guda biyu.

Amma, mutane biyu daga cikin mazauna ƙauyen sun rasa rayukansu a harin.

Rundunar ta ce har yanzu tana ci gaba da ƙoƙarin kamo ’yan bindigar da suka tsere.

Kwamishinan ’yansandan, CP Bello Shehu, ya yaba wa jami’ansa bisa jarumtaka da suka nuna.

Ya kuma buƙaci jama’a da su ci gaba da bai wa ’yansanda sahihan bayanai a kan lokaci.

Ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a faɗin jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato
  • Kassim: Duk Wanda Yake Neman Hizbullah Ta Ajiye Makamanta Yana Yi Wa Isra’ila Aiki
  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati
  • Shugabannin Arewa Sun Tattauna Sabon Hanyar Ci Gaba – Minista Uba Maigari Ya Yaba
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Na Da Kwamitoci 30 Da Ke Sa Ido Kan Ma’aikatun Gwamnati
  • Gwamnan Zamfara Ya Naɗa Abdulkadir Ibrahim A Matsayin Sabon Sarkin Katsinan Gusau Na 16