“Murkushe ‘yan adawa tare da musguna musu, musamman jam’iyyar PDP, wata alama ce karara da ke nuna cewa; zangon karshen mulki na karatowa; domin kuwa tarihi ya sha nuna hakan”, in ji Lamido a tattaunawarsa da BBC Hausa.

 

“Ya kamata Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ya kasance mai adalci, domin shi ne shugaban dukkanin ‘yan Nijeriya.

Dole ne ya bar ‘yan adawa su yi takara a siyasance da jam’iyyar APC, idan kuma bai yi taka-tsan-tsan ba, abin zai iya komawa kansa”, in ji shi.

 

A ranar Litinin ne, Gwamnan Jihar Delta Sheriff Oborebwori da da wanda ya gaji kujerar daga wajensa, Dakta Ifeanyi Okowa da daukacin tsarin ‘yan siyasar da ke jam’iyyar PDP a jihar, suka sauya sheka zuwa jam’iyyar APC.

 

Haka zalika, a makwannin da suka gabata ne, ‘yan majalisar wakilai daga jam’iyyun adawa irin su LP da NNPP, su ma suka sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki. Sannan kuma, ana samun rade-radin cewa, gwamnonin jihohi da dama na shirin yin koyi da shi,

 

A halin da ake ciki yanzu, bayan wani dogon zama da kwamitin gudanarwar PDP na kasa ya yi, jam’iyyar PDP ta kudiri aniyar kwato ragamar shugabancinta daga hannun wadanda suka sauya sheka.

 

Mukaddashin Shugaban Jam’iyyar na Kasa, Ambassador Illiya Umar Damagum, da yake jawabi bayan kammala taron nasu, ya ce; jam’iyyar ta umarci mai ba ta shawara kan harkokin shari’a na kasa, ya fara shiri don tunkarar wannan kara.

 

Damagum ya bayyana cewa, jam’iyyar ta amince da shawarwarin da gwamnonin PDP suka bayar a taron da suka gudanar a Ibadan kwanan nan, wanda ya hada da nadin sabon Sakatare na kasa da kuma tsara babban taron jam’iyyar na kasa nan gaba.

 

Da yake tsokaci kan sauya sheka na Delta, Damagum ya ce; ya ji dadin yadda gwamnan da tsohon dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, ba su soki jam’iyyar ba, ya kara da cewa; babu wani abu da jam’iyyar ta yi musu da ya sa suka bar ta.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: jam iyyar PDP sauya sheka a jam iyyar

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APC

Ƙungiyar matasan jam’iyyar APC reshen Jihar Kano ta ce guguwar sauyin sheƙa ta jiga-jigan ’yan siyasa da ke ficewa daga jam’iyyar NNPP alama ce da ke nuna cewa tasirin tsohon Gwamnan Kano, Rabi’u Musa Kwankwaso a siyasance na ƙara disashewa.

Cikin wata sanarwa da ƙungiyar matasan ta KASASCO ta fitar a ranar Talata, ta ce a halin yanzu jam’iyyar APC ba ta buƙatar dawowar Kwankwaso cikinta saboda tasirinsa a siyasance na ci gaba da gushewa.

DAGA LARABA: Asarar Da Hausawa Ke Tafkawa Sakamakon Bacewar Tatsuniya ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno

Darekta Janar na KASASCO, Kwamared Yahaya Usman Kabo, ya ce jam’iyyar APC a ƙarƙashin jagorancin Abdullahi Abbas ta yi tsayuwar daka da kafa tubalin samun nasara a Zaɓen 2027 da ke tafe, la’akari da cewa tana da Sanatoci biyu da kuma wakilci mai ƙarfi a matakin jiha da tarayya.

Ya bayyana cewa guguwar sauyin sheƙa da ke kaɗawa a jam’iyyar NNPP na da nasaba da tasirin jiga-jigan jam’iyyar da suka tsaya kai da fata wajen tabbatar da nasararta a Zaɓen 2023.

Sai dai ya ce a yanzu jiga-jigan jam’iyyar ta NNPP na ficewa daga cikinta zuwa APC saboda zargin rashin adalci da mayar da su saniyar ware da ’yan Kwankwasiyya suka yi.

Aminiya ta ruwaito cewa daga cikin jiga-jigan NNPP da suka sauya sheƙa zuwa APC a bayan nan akwai Sanata Abdurrahman Kawu Sumaila da Kabiru Alhassan Rurum da Abdullahi Sani Rogo da Zubairu Hamza Massu.

Akwai kuma Abbas Sani Abbas da Baffa Bichi da kuma Sha’aban Ibrahim Sharada.

Ya ce “sauyin sheƙar waɗannan jiga-jigan ’yan siyasa ta karya garkuwar jam’iyyar a Kano. Saboda haka yanzu APC ta warware duk wasu matsalolin cikin gida da take fuskanta domin tabbatar da nasarar a 2027.”

APC ta ce tana da yaƙinin samun nasara a zaɓen da take tafe wanda take fatan bai wa Shugaba Bola Tinubu ƙuri’u miliyan biyu a Jihar Kano.

Sai dai ta ce dawowar Kwankwaso jam’iyyar babu abin da zai haifar sai kawo ruɗani a cikinta.

“A yanzu Kwankwaso ba shi da wani tasiri a siyasance, shi ya sa yake neman mafaka da babu inda zai same ta face a jam’iyyar APC.

“Sai dai yana da kyau ya fahimci cewa APC ba wuri ba ne na samun mafaka kuma ba ta buƙatar irinsu [Kwankwaso] da babu abin da za su kawo wa jam’iyyar face ruɗani.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Ce Ba Zata Amince Da Barazana Da Kuma Takurawa A Lokaci Guda Da Tattaunawa ba
  • Atiku Ne Rikitacce Ba Tinubu Ba
  • Sabon Tsarin Ci Gaba Na Sin Ya Kawo Sauyi Daga Samar Da Takalma Miliyan 100 Zuwa Kera Mattarar Bayanai Ta Microchip
  • Ministan Tsaron Iran Ya Bayyana Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya A Matsayar Alamar Yan Ta’adda
  • Kasar Sin Ta Yi Kiran Kawar Da Makaman Nukiliya Bisa Tsarin Tsaro Na Bai Daya
  • Iran Tace Samar Da Kasar Falasdinu Mai Cikekken Yenci Ba Abin Tattaunawa Bane
  • An Bukaci Masu Yiwa Kasa Hidima Su Yi Amfani Da Kafofin Sadarwa Na Zamani Don Inganta Hadin Kan Kasa.
  • Dubban Mutanen Burkina Faso Sun Yi  Gangamin Nuna Goyon Bayan Shugaban Kasa Ibrahim Traore
  • Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APC