“Murkushe ‘yan adawa tare da musguna musu, musamman jam’iyyar PDP, wata alama ce karara da ke nuna cewa; zangon karshen mulki na karatowa; domin kuwa tarihi ya sha nuna hakan”, in ji Lamido a tattaunawarsa da BBC Hausa.

 

“Ya kamata Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ya kasance mai adalci, domin shi ne shugaban dukkanin ‘yan Nijeriya.

Dole ne ya bar ‘yan adawa su yi takara a siyasance da jam’iyyar APC, idan kuma bai yi taka-tsan-tsan ba, abin zai iya komawa kansa”, in ji shi.

 

A ranar Litinin ne, Gwamnan Jihar Delta Sheriff Oborebwori da da wanda ya gaji kujerar daga wajensa, Dakta Ifeanyi Okowa da daukacin tsarin ‘yan siyasar da ke jam’iyyar PDP a jihar, suka sauya sheka zuwa jam’iyyar APC.

 

Haka zalika, a makwannin da suka gabata ne, ‘yan majalisar wakilai daga jam’iyyun adawa irin su LP da NNPP, su ma suka sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki. Sannan kuma, ana samun rade-radin cewa, gwamnonin jihohi da dama na shirin yin koyi da shi,

 

A halin da ake ciki yanzu, bayan wani dogon zama da kwamitin gudanarwar PDP na kasa ya yi, jam’iyyar PDP ta kudiri aniyar kwato ragamar shugabancinta daga hannun wadanda suka sauya sheka.

 

Mukaddashin Shugaban Jam’iyyar na Kasa, Ambassador Illiya Umar Damagum, da yake jawabi bayan kammala taron nasu, ya ce; jam’iyyar ta umarci mai ba ta shawara kan harkokin shari’a na kasa, ya fara shiri don tunkarar wannan kara.

 

Damagum ya bayyana cewa, jam’iyyar ta amince da shawarwarin da gwamnonin PDP suka bayar a taron da suka gudanar a Ibadan kwanan nan, wanda ya hada da nadin sabon Sakatare na kasa da kuma tsara babban taron jam’iyyar na kasa nan gaba.

 

Da yake tsokaci kan sauya sheka na Delta, Damagum ya ce; ya ji dadin yadda gwamnan da tsohon dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, ba su soki jam’iyyar ba, ya kara da cewa; babu wani abu da jam’iyyar ta yi musu da ya sa suka bar ta.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: jam iyyar PDP sauya sheka a jam iyyar

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi

 

Shugaba Xi ya kuma bayyana cewa, cikakken zama na 4 na kwamiti na 20 na JKS ya amince da shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 15. Sin za ta yi amfani da wannan damar don ci gaba da gyare-gyaren tattalin arzikinta, da kuma fadada bude kasuwancinta mai zurfi ga ketare, ta haka za ta ci gaba da ba da sabbin damammaki ga yankin Asiya da Pasifik da sauran kasashen duniya ta hanyar zamanantar da al’ummarta. (Amina Xu)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo October 30, 2025 Daga Birnin Sin Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma  October 30, 2025 Daga Birnin Sin Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
  • Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Iran Ta Sanya  Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
  • Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan
  • Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi
  • Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP