Ana sa alamar tambayar cewa: Shin gobarar da ta tashi a birnin Kudus… shin sako ne na ranar tunawa da kafuwar gwamnatin ‘yan sahayoniyya?

Gobarar da ta tashi a tsaunin Kudus da aka mamaye ta bazu zuwa manyan yankuna a cikin haramtacciyar kasar Isra’ila, inda ta kewaye wani sansanin soji tare da cinye filayen masu girma da tsayi.

Hakan ya sa hukumomin gwamnatin mamayar Isra’ila suka kafa dokar ta baci tare da neman taimakon kasashen duniya. Yayin da Ministan tsaron cikin gidan Isra’ila Itamar Ben-Gvir yake neman dora wa Falasdinawa, alhakin tashin gobarar.

Gobarar ta kunno kai ne a daidai lokacin da yahudawan sahayoniyya suka fara gudanar da bukukuwan cika shekaru 77 da kafuwar gwamnatinsu ta mamaya a kasar Falasdinawa, gobara mai karfin gaske ta barke a tsaunukan birnin Kudus ta kuma bazu zuwa manyan yankuna masu girma.

Gobarar ta tashi ne a kusa da babbar hanyar da ke tsakanin Kudus da Tel Aviv, lamarin da ya kawo yawaitar cunkoson ababen hawa a manyan tituna. Gobarar ta yi sanadin jikkatar mutane masu yawa, kuma ta tilastawa hukumomin gwamnatin mamaya fara kwashe yahudawan sahayoniyya ‘yan kaka gida daga gidajensu da ma marasa lafiya daga Asibitin Hadassah Ein Kerem da ke birnin Kudus saboda gobarar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Sun Kai Hare-Hare Kan Cibiyoyin Leken Asirin Isra’ila

Dakarun kare juyin juya halin Musulunci sun kai hare-hare har sau uku kan cibiyoyin leken asirin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila

Ma’aikatar hulda da jama’a ta dakarun kare juyin juya halin musulunci ta Iran ta fitar da sanarwa inda ta bayyana harin da aka kai kan cibiyoyin leken asirin haramtacciyar kasar Isra’ila a mataki na uku na hare-haren daukan fansa na “Alkawarin Gaskiya na Uku”.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa: Hare-haren wuce gona da iri da yahudawan sahayoniyya suke kaiwa kan kasar Iran da jijjifin safiyar yau sun nufi yankunan gidajen jama’a ne. Sannan maharan yahudawan sahayoniyyan sun kashe jami’an leken asirin dakarun kare juyin juya hali uku, shahid Mohammad Kazimi, Hassan Mohaqeq, da Mohsin Baqiri.

A ci gaba da mayar da martani kan laifuffukan ta’addancin yahudawan sahayoniyya, Dakarun kare sararin samaniyar kasar Iran na Dakarun kare juyin juya halin Musulunci sun kai wani sabon harin makami mai linzami kan cibiyoyin leken asiri na ‘yan sahayoniyya a mataki na uku hare-haren daukan fans ana “Alkawarin Gaskiya na Uku”.

Hakika Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta lashi takwabin ruguza duk wani  muhimman wuri da cibiyar aikata muggan manufofin yahudawan sahayoniyya kafin kawo karshen wannan yaki da gwamnatin haramtacciyar kasar kasar Isra’ila ta daura kan Iran.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Sun Kai Hare-Hare Kan Cibiyoyin Leken Asirin Isra’ila
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Sojojin Isra’ila Sun Kashe Kananan Yara Masu Yawa A Iran
  • An Zartar Da Hukuncin Kisa Kan Dan Leken Asirin Haramtacciyar Kasar Isra’ila A Iran
  • Amurka Ta Rufe Ofishin Jakadancinta Da Ke Tel-Aviv Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Martanin Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Kan Ta’addancin ‘Yan Sahayoniyya ya Shiga Rana Ta Biyu
  • Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila