Gwamnatin Tarayya Ta Raba Rigunan Kariya Ga Wasu Jihohin Najeriya.
Published: 1st, May 2025 GMT
Gwamnatin tarayya ta kaddamar da wayar da kan al’umma kan kare lafiyar ruwa tare da raba riguna a wasu zababbun Jihohin Najeriya.
Ministan Tattalin Arzikin Ruwa, Adegboyega Oyetola wanda ya kaddamar da taron a gidan gwamnati, Minna ya ce wannan ra’ayin ya yi daidai da jajircewar Gwamnatin Tarayya na kare rayuka da dukiyoyin al’umma da rayuwar ’yan Najeriya da ke dogaro a kullum kan hanyoyin ruwa na cikin kasa wajen sufuri da kasuwanci.
Ya amince da dimbin karfin tattalin arzikin magudanan ruwa a kasar nan da ke fama da tashe-tashen hankula sakamakon yawaitar hadurra na kwale-kwalen da ke bukatar hada kai, da kuma daukar matakai bisa dabaru don haka aka fara raba riguna 3,500 a matakin farko ga jihohi 12 ciki hadda jihar Neja.
Ministan wanda ya yabawa Gwamna Umar Bago bisa ga kokarin da yake yi na ganin ya inganta harkokin sufurin koguna a cikin Jihar tare da sayo da rarraba jiragen ruwa guda biyar ya yi kira ga sauran gwamnonin Jihohi da shugabannin al’umma da su yi koyi dashi.
A nasa jawabin gwamnan jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya ce gwamnati tare da hadin gwiwar hukumar kula da hanyoyin ruwa ta kasa NIWA da sauran masu ruwa da tsaki za su aiwatar da aikin da aka wajaba na amfani da rigar kariya da kuma bin dukkan ka’idojin kiyaye hanyoyin ruwa a jihar.
Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Neja, Abdulmalik Sarkin Daji ya wakilce shi ya yi tir da yadda ake tafka ta’asa a cikin kwale-kwale a jihar inda ya ce gwamnatin jihar ta gano musabbabin hatsarin kwale-kwale a jihar kuma ta kuduri aniyar magance ta ta hanyar tabbatar da doka da oda da kuma zuba jari a hanyoyin ruwa.
Manajan Darakta kuma babban jami’in gudanarwa na hukumar kula da hanyoyin ruwa ta kasa NIWA, Bola Oyebamiji wanda shi ma ya amince da kudurin Gwamna Bago na magance matsalolin da suka shafi harkar sufurin ruwa, ya bayyana bukatar kara karfafa hadin gwiwa da abokan hulda wajen dakile bala’in da jiragen ruwa ke tafkawa a hanyoyin ruwa.
Kwamishiniyar Sufuri, Hajiya Hadiza Idris Kuta ta yabawa ma’aikatar harkokin ruwa da tattalin arzikin kasa bisa tallafin da take baiwa jihar Neja da samar da motocin daukar marasa lafiya da kwale-kwalen fasinja da suka hada da samar da jami’an kula da ruwa da aka jibge a yankunan gabar tekun jihar yayin da ta kuma yarda cewa rigunan ceton da aka raba wa jihar zai taimaka matuka.
Etsu Nupe kuma Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Jihar Neja Alh, Yahaya Abubakar wanda Wambai Nupe, Injiniya Ndagi Aliyu ya wakilta ya sake jaddada bukatar cibiyoyi na gargajiya a matsayinsu na masu ruwa da tsaki a matakin kasa da su kara kaimi wajen wayar da kan al’ummarsu kan bukatar kiyaye hanyoyin ruwa.
KARSHEN ALIYU LAWAL.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: a hanyoyin ruwa kwale kwale
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisa ta ba NNPCL mako uku ya yi mata bayanin inda tirilyan 210 ta shiga
Kwamitin Majalisar Dattawa na bin Diddigi ya ba Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL) wa’adin mako uku ya amsa tambayoyi kan rashin ba da ba’asi kan Naira tiriliyan 210 da ba a san inda suka shiga ba daga shekarar 2017 zuwa 2023.
An dai bayar da wa’adin ne ga shugaban kamfanin na kasa, Bayo Ojulari, wanda ya bayyana a gaban kwamitin ranar Talata, bayan ya bayar da hakuri kan rashin bayyanarsa yayin gayyatar da kwamitin ya yi masa a baya.
Yadda ’yan bindiga sun tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACFKwamitin, wanda ke karkashin jagorancin Ahmed Wadada Aliyu (Nasarawa), ya tsaya kai da fata cewa dole kamfanin ya bayyana inda kudaden suka shiga.
Ojulari dai ya ba kwamitin hakuri, inda ya ce yana bukatar karin lokaci kafin ya iya amsa tuhumar da aka yi masa har guda 19.
Ya kuma ce, “Da kadan na haura kwana 100 a matsayin shugaban wannan kamfanin. Ina bukatar karin lokaci kafin na iya zakulo bayanan da kuka bukata. Wannan kuma na zuwa ne a daidai lokacin da sauran tarin ayyuka ke jira na.
“Ni kaina ina bukatar fahimtar abubuwan da kaina kafin na iya bayar da amsa a kansu. Amma zan je na zauna da sauran ma’aikatana da suka dace mu tattauna domin bayar da abin da ake bukata,” in ji shugaban na NNPCL.
Kodayake mako hudu ya bukata, amma kwamitin ya ba shi mako uku ne domin ya gabatar da bayanan.
Da yake karin haske a kan kudaden, Sanata Wadada ya ce kudaden da ake magana a kan su rubi biyu ne, akwai Naira tiriliyan 103 da kuma Naira tiriliyan 107 da suke bukatar bayanan a kan su.
“Amma fa ba mu ce wadannan kudaden da ake magana a kan su sace su aka yi ko kuma sun bace ba. Abin da kwamitinmu kawai yake kokarin yi shi ne bincike domin gano yadda aka yi tusarrufi da su,” in ji Sanata Wadada.