Gwamnatin Tarayya Ta Raba Rigunan Kariya Ga Wasu Jihohin Najeriya.
Published: 1st, May 2025 GMT
Gwamnatin tarayya ta kaddamar da wayar da kan al’umma kan kare lafiyar ruwa tare da raba riguna a wasu zababbun Jihohin Najeriya.
Ministan Tattalin Arzikin Ruwa, Adegboyega Oyetola wanda ya kaddamar da taron a gidan gwamnati, Minna ya ce wannan ra’ayin ya yi daidai da jajircewar Gwamnatin Tarayya na kare rayuka da dukiyoyin al’umma da rayuwar ’yan Najeriya da ke dogaro a kullum kan hanyoyin ruwa na cikin kasa wajen sufuri da kasuwanci.
Ya amince da dimbin karfin tattalin arzikin magudanan ruwa a kasar nan da ke fama da tashe-tashen hankula sakamakon yawaitar hadurra na kwale-kwalen da ke bukatar hada kai, da kuma daukar matakai bisa dabaru don haka aka fara raba riguna 3,500 a matakin farko ga jihohi 12 ciki hadda jihar Neja.
Ministan wanda ya yabawa Gwamna Umar Bago bisa ga kokarin da yake yi na ganin ya inganta harkokin sufurin koguna a cikin Jihar tare da sayo da rarraba jiragen ruwa guda biyar ya yi kira ga sauran gwamnonin Jihohi da shugabannin al’umma da su yi koyi dashi.
A nasa jawabin gwamnan jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya ce gwamnati tare da hadin gwiwar hukumar kula da hanyoyin ruwa ta kasa NIWA da sauran masu ruwa da tsaki za su aiwatar da aikin da aka wajaba na amfani da rigar kariya da kuma bin dukkan ka’idojin kiyaye hanyoyin ruwa a jihar.
Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Neja, Abdulmalik Sarkin Daji ya wakilce shi ya yi tir da yadda ake tafka ta’asa a cikin kwale-kwale a jihar inda ya ce gwamnatin jihar ta gano musabbabin hatsarin kwale-kwale a jihar kuma ta kuduri aniyar magance ta ta hanyar tabbatar da doka da oda da kuma zuba jari a hanyoyin ruwa.
Manajan Darakta kuma babban jami’in gudanarwa na hukumar kula da hanyoyin ruwa ta kasa NIWA, Bola Oyebamiji wanda shi ma ya amince da kudurin Gwamna Bago na magance matsalolin da suka shafi harkar sufurin ruwa, ya bayyana bukatar kara karfafa hadin gwiwa da abokan hulda wajen dakile bala’in da jiragen ruwa ke tafkawa a hanyoyin ruwa.
Kwamishiniyar Sufuri, Hajiya Hadiza Idris Kuta ta yabawa ma’aikatar harkokin ruwa da tattalin arzikin kasa bisa tallafin da take baiwa jihar Neja da samar da motocin daukar marasa lafiya da kwale-kwalen fasinja da suka hada da samar da jami’an kula da ruwa da aka jibge a yankunan gabar tekun jihar yayin da ta kuma yarda cewa rigunan ceton da aka raba wa jihar zai taimaka matuka.
Etsu Nupe kuma Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Jihar Neja Alh, Yahaya Abubakar wanda Wambai Nupe, Injiniya Ndagi Aliyu ya wakilta ya sake jaddada bukatar cibiyoyi na gargajiya a matsayinsu na masu ruwa da tsaki a matakin kasa da su kara kaimi wajen wayar da kan al’ummarsu kan bukatar kiyaye hanyoyin ruwa.
KARSHEN ALIYU LAWAL.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: a hanyoyin ruwa kwale kwale
এছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila da Iran su daidaita rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
Gwamnatin Tarayya ta roƙi ƙasashen Isra’ila da Iran da su daina rikici, su zauna lafiya su sasanta tsakaninsu.
A wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Waje ta fitar, ta bayyana damuwa kan yadda rikicin ke ƙara ta’azzara, inda ta nemi ɓangarorin biyu da su kai zuciya nesa don samar da zaman lafiya a duniya baki ɗaya.
Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — DalungSanarwar ta ce faɗa da ramuwar gayya na jefa rayukan fararen hula cikin hatsari, kuma yana iya haddasa rikici mai muni a yankin Gabas ta Tsakiya, wanda hakan zai iya barazana ga tsaron duniya da kuma ci gaban tattalin arziƙi dunuya.
“Mu a matsayimmu na ƙasa mai son zaman lafiya, muna roƙon ƙasashen da ke rikici da su zauna su tattauna maimakon su ci gaba da faɗa.”
Gwamnatin Tarayya ta kuma yi kira ga ƙasashen duniya, musamman Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya, da su ɗauki matakai don hana yaɗuwar rikicin da kuma samo hanyar warware matsalar.
Sanarwar ta ƙara da cewa amfani da ƙarfin soji ba shi da amfani matuƙa, domin faɗa ba zai kawo sauƙi ba.
Najeriya ta ce a shirye ta ke ta bayar da taimako domin hana yaɗuwar rikicin da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin.