Ta ce, sakamakon dukan da ta sha, ta samu karaya a kafa da kuma raunin da ya shafi kunnenta.

 

Sai dai Shu’aibu ya musanta wannan ikirarin, inda ya tabbatar da cewa, an kama dan uwanta ne a yayin wani samame da aka gudanar a wurin wani shagali a birnin Katsina.

 

A cewarsa, an kama wanda ake zargin ne da laifin yin sojan gona da kuma yunkurin dakatar da jami’an Hisbah a lokacin da suke bakin aiki.

 

Da yake karin haske game da gaskiyar lamarin abinda ya faru, Shuaibu ya ce, an hana Hauwa shiga cikin ofishin Hisbah ne saboda irin tufafin da take sanye da su na rashin da’a, kuma ta yi yunkurin marin daya daga cikin jami’an Hisbah a lokacin da suka hana ta shiga.

 

Dangane da ikirarin da Hauwa ta yi na karaya a kafa, Shu’aibu ya ce hukumar ta bukaci iyalanta da su kawo mata shaidar na’urar haska kashi amma har zuwa lokacin taron manema labarai ba su samu wani takarda da ke tabbatar da raunin da ta samu ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a Filato

Aƙalla mutum huɗu ciki har da jaririn wata tara aka kashe a wani hari da aka kai ƙauyen Nkiendowro da ke Ƙaramar Hukumar Bassa a Jihar Filato.

Mutanen da suka rasu sun haɗa da mata biyu da namiji ɗaya, wanda aka ce suna aikin jigilar kwashe tumatir daga ƙauyen zuwa kasuwar Farin-Gada da ke Jos lokacin da aka kai musu hari.

Rashin wutar lantarki ya durƙusar da kasuwanci a Arewa Maso Gabas An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a Filato 

Wasu mutum biyu kuma sun jikkata a harin, wanda yanzu haka suna karɓar magani a wani asibiti da ba a bayyana sunansa ba.

Shugaban tsaron al’ummar Miango, Josiah Zongo, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa an ajiye gawarwakin, yayin da waɗanda suka jikkata ke karɓar kulawa.

Rundunar ’yan sandan Jihar Filato ba ta fitar da wata sanarwa ba kan harin.

A wani lamari makamancin haka, an kai hari ƙauyen Murish da ke Ƙaramar Hukumar Mangu a daren ranar Laraba, amma matasa da mazauna ƙauyen sun yi nasarar kare kansu daga maharan.

Wani matashi daga ƙauyen ya bayyana cewa maharan sun shigo suna harbi, amma mutanen ƙauyen sun kare kansu.

Shohotden Mathias Ibrahim, Daraktan Al’adu na ƙungiyar Mwaghavul Development Association kuma shugaban sansanin ‘yan gudun hijira a Mangu, ya roƙi al’umma da su kwantar da hankali su ci gaba da harkokinsu cikin lumana.

Ƙananan hukumomin Mangu da Bassa sun fuskanci hare-hare da dama a ‘yan kwanakin nan, lamarin da ke ƙara tayar da hankalin al’umma game da tsaro a Jihar Filato.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe
  • Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India
  • Adadin Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Kashe A AfirkaTa Kudu Ya Karu Zuwa 49
  • An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a Filato
  • Gobara Ta Ƙone Wani Gidan Mai A Legas
  • Ministan Tsaro Na Kasar Iran ya bada Labarin Gwajin Wani Sabom Makami Mai Limzami Mai Daukar abubuwan Fashewa Har Ton Biyu