Aminiya:
2025-05-01@04:37:39 GMT

Yadda ma’aikatan gidan ruwa 4 suka mutu a Bauchi

Published: 21st, April 2025 GMT

Ma’aikatan Hukumar Samar da Ruwan Sha ta Jihar Bauchi guda huɗu sun rasu a yayin da suke aikin tsabtace madatsar ruwa ta Gubi.

Wasu jami’ai da ke aiki a Madatsar Ruwa ta Gubi, sun bayyana cewa daga cikin mamatan har da wani uba da dansa da kuma wani wanda ke shirye-shiryen ɗaurin aurensa.

“Abin ya faru ne a lokacin da suke aikin tsaftace ruwan da ake kula da ruwan da ake yi wa babban birnin Bauchi.

Na samu labarin suna cikin tafki, sai suka ga wasu kifaye a cikin ruwan datti, ɗaya daga cikinsu yana ƙoƙarin kama kifi, kifin ya yi zurfi, sai ya bi shi ya mutu.

“Ana cikin haka, wani abokin aikinsa da ya ga abin da ya faru ya yi ƙoƙarin ceto shi, shi ma ya mutu, kuma anyi musu jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ta tanada,” kamar yadda wani abokin aikinsu ya bayyana.

Ambaliya ta kashe mutum 3 ta lalata hekta 10,000 na shinkafa a Neja Ango ya tsere tare da surukarsa Gobara ta ƙone gidaje sama da 100 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno 

Kakakin Rundunar ’Yan Sanda a Jihar Bauchi, CSP Mohammed Ahmed Wakil ya ce ma’aikatam da suka rasu sun hada Shayibu Hamza mai shekaru 48 da Abdulmalik Yahya mai shekaru 29 da Jamilu Inusa mai shekaru 29 da kuma Ibrahim Musa mai shekaru 42.

Ya ci gaba da cewa lamari mai ban tausayi ya auku a madatsar ruwa ta Gubi, wanda ya yi sanadin asarar ma’aikatan da suka sadaukar da kansu a yayin wani aikin yashe shara da ke cikin ramuka a madatsar ruwan ta Gubi.

Ya ce A lokacin da waƙi’ar ta auku, an yi ƙoƙarin ceto su, aka fito da su a sume daga cikin ramin tara ruwan da suke aikin, daga nan aka garzaya da su Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Ɓalewa da ke Bauchi, amma duk da kulawar gaggawa da aka ba su, sai Allah Ya karɓe su, likitoci suka tabbatar da rasuwarsu.

Wakil ya ce, a lokacin da ’yan sanda suka samu labarin faruwar lamarin, sun tura jami’ai zuwa wurin, yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike don gano ainihin abin da ya faru.

Ya ce akwai buqatar qara daukan matakai a vangaren kula da ruwa, yana mai jaddada muhimmancin dukkan ma’aikatan su kula da bin ƙa’idojin aminci da aka kafa don rage haɗari nan gaba.

Duk ƙoƙarin da muka yi na jin ta bakin Kwamishinan Albarkatun Ruwa ma Jihar Bauchi, Abdulrazaq Nuhu Zaki, da Babban Manajan Kamfanin Samar da Ruwan Sha na Jihar Bauchi, Injiniya Aminu Aliyu Gital, a game da lamarin ya ci tura.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Madatsar Ruwa a Jihar Bauchi mai shekaru

এছাড়াও পড়ুন:

Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi

Wani wanda ake zargi da safarar sassan jikin ɗan Adam ya shaida wa jami’an tsaro cewa ya shafe sama da shekara 10 yana sayar da sassan jikin mutum don samun kuɗi.

Dubun mutumin sun cika ne a ranar Asabar din da ta gabata inda sojoji suka kama shi a yankin Kulanla Odomoola da ke Jihar Ogun.

A furucinsa da ya amsa laifin, wanda ake zargin ya amince da sayar da sassan jikin mutum ga masu buƙata don samun kuɗin shiga.

“Na dogara ne da sayar da sassan jikin mutum tsawon shekaru 10 da suka gabata. Yawancin sassan da nake sayarwa ina tono su ne daga sabbin kaburbura a makabartu, yayin da wasu kuma nake samun su daga gawarwakin da aka watsar a gefen hanyoyi,” in ji shi.

Aminu Bayero ya naɗa Sanusi a matsayin Galadiman Kano Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji laifi ne — Janar Chibuisi NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”

Wanda ake zargin, wanda ya amsa laifinsa ga wani taron jama’a da suka yi yunƙurin kashe shi kafin sojoji su cece shi, ana zargin yana kan hanyarsa ne na kai wani sassan jiki ga wani mai siye lokacin da aka kama shi.

Daga nan aka miƙa wanda ake zargin ga ’yan sanda a yankin Noforija don ƙarin bincike da kuma gurfanar da shi a gaban kotu.

Laftanar Kanar Olabisi Olalekan Ayeni, Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar Sojin Najeriya ta 81, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya bayan kama wanda ake zargin daga baya an miƙa shi tare da kayayyakin da aka samu a wurinsa, ga ’yan sandan Najeriya don ƙarin bincike da kuma gurfanar da shi a gaban kotu.

“Sojojin sun ceto wanda ake zargin daga wani taron jama’a da suka yi yunƙurin kashe shi,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu
  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • Riza’i: Babu Hannun  Waje A Cikin Hatsarin Da Ya Faru A Tashar Ruwa Ta Shahid Raja’i
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Shirya Fara Tantance ‘Yan Fansho
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno
  • Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi
  • Jagora Ya Bada Umurnin A Gudanar Bincike Mai Zurfi A Fashewar Tashar Jiragen Ruwa Na Shaheed Rajae