Aminiya:
2025-11-03@02:59:52 GMT

Ango ya tsere tare da surukarsa

Published: 21st, April 2025 GMT

Ana zargin wani ɗan kasar Indiya mai shekara 20 da tserewa da surukarsa mai shekara 40, kwanaki tara kacal kafin aurensa da ’yarta.

Ma’auratan Rahul da Shibani, matasa ne ’yan Aligarh, a Jihar Uttar Pradesh ta Indiya, wadanda suka shirya yin aure a ranar 16 ga Afrilu na watan da muke ciki.

Zaɓen 2027: Babu ɗan takarar da zai yi nasara ba tare da goyon bayan Arewa ba — Hakeem NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye cikin littafai ana shirin kaiwa Saudiyya

An aika wa dangi katin gayyata domin halartar taron bikin, amma kwanaki tara kafin ranar bikin, sai wani iftila’i ya afku.

Angon dan shekara 20 ya lallaba ya bace, amma bai tafi shi kadai ba; ya tsere da Anita, mahaifiyar amaryarsa mai shekara 40.

Domin munin lamarin, Angon da Anita sun kwashe kudaden ajiyar ma’auratan da kuma ajiyar dangin Anita, inda suka tatuke Shibani (amarya) da mahaifinta.

A ranar Lahadi 6 ga Afrilu, Rahul ya bar gidansu, yana mai cewa zai yi siyayya kayan biki.

Da daddare sai ya kira mahaifinsa ya shaida masa cewa, zai yi tafiya, amma kada ya damu da neman sa.

Kusan lokaci guda, Shibani ta lura cewa, mahaifiyarta da kudin ajiyarsu sun bace, sai dai ba ta bar wani sako ba.

Kodayake Shibani da mahaifinta mai suna Kumar sun lura da dangantakar da ba a saba ba gani ba a tsakanin Rahul da Anita, amma ba su ce komai ba, saboda ba sa son lalata auren.

“Ya kamata mu yi aure da Rahul a ranar 16 ga Afrilu, kuma mahaifiyata ta tafi tare da shi ranar Lahadi.

“Rahul da mahaifiyata sun kasance suna tattaunawa ta waya sosai a cikin wata uku zuwa huɗu,” kamar yadda Shibani ta shaida wa manema labarai na Indiya.

“Mahaifiyata ta kwashe duk kudinmu na shagalin bikin. Za ta iya yin dauk abin da take so yanzu, ba mu damu ba. Abin da muke so shi ne a mayar mana da kudinmu da kayan ado.”

Mijin Anita, Kumar yana sana’a ce a Bengaluru kuma yawanci ba ya zama, inda shi ma ya lura cewa Rahul ya fi yin magana da matarsa fiye da yadda yake yi da ‘yarsa.

Duk da haka, bai ce komai ba domin ranar biki ta kusa, kuma ba ya son bata abubuwa.

Ya shigar da karar wanda zai auri ’yarsa da matsarsa da suka bace da fatan ‘yan sanda za su iya gano su.

“Na kira Anita sau da yawa, amma ta kashe wayarta, na kuma kira mutumin da suke tare, amma ya ci gaba da musanta cewa ba ta tare da shi,” in ji Kumar.

Ya ce, “Wannan mutumin ba ya yin waya da ‘yata, said ai ya yi da matata,” in ji mahaifin Shibani.

“Ina zaune a Bengaluru don gudanar da kasuwancina, sai na ji cewa, tsawon wata uku da suka wuce, suna tattaunawa da juna na tsawon sa’o’i 22 a rana, na yi shakku, amma ban ce komai ba saboda an kusa daurin auren.

Anita ta tsare da mutumin a ranar 6 ga Afrilu kuma ta kwashe duk kudinmu da kayan ado.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Indiya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda

Daga Usman Muhammad Zaria

 

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi kira ga mazauna jihar Jigawa da su kasance masu bin doka da oda, tare da yin aiki kafada da kafada da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin jihar.

Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya karɓi sabbin motoci 10 kirar Toyota Hilux da Gwamna Umar Namadi ya bai wa rundunar a Dutse, babban birnin jihar.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, CP Dahiru Muhammad ya yaba da jajircewar Gwamna Umar Namadi wajen tallafa wa hukumomin tsaro domin sauke nauyin da ke kansu a jihar.

Ya bayyana cewa, wannan gudummawa ta nuna cikakken kudirin gwamnatin Gwamna Namadi na ƙara inganta harkokin tsaro da kuma tallafawa Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya wajen aiwatar da aikinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.

Kwamishinan ya nuna cewa, waɗannan sabbin motoci 10 za su taimaka matuƙa wajen rage lokacin da ake ɗauka kafin amsa kiran gaggawa, tare da ƙara inganta aikin rundunar a fadin jihar.

Ya ƙara da cewa, za a yi amfani da motocin yadda ya kamata, tare da kula da su don tabbatar da ingantaccen  tsaro.

CP Dahiru Muhammad ya kuma sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, doka da oda, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fursunan da aka yanke wa hukuncin kisa ya tsere daga gidan yari a Yobe
  • Larijani: Iran Ba Ta Tsoron Gudanar Da Tattaunawa, Amma Ta Zama Mai Amfani
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
  • Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi