Gwamnaton kasar Kongo Democradiyya ta bada sanarwan haramta jam’iyyar Josept Kabila tsohon shugaban kasar.

Shafin yanar gizo na labarai, Africa News ya nakalto ma’aikatar harkokin cikin gida na kasar tana bada wannan sanarwan.

Labarin ya kara da cewa, Josept Kabila ya shugabanci kasar ta kwango har zuwa shekara ta 2019, karkashin Jam’iyyarsa ta ‘the People’s Party for Reconstruction and Democracy (PPRD).

Daga baya Kabila ya dorawa kansa gudun hijira zuwa kasashen waje a shekara ta 2023. Bai kuma sake dawowa ba sai ranar jummar da ta gabata.

Kabila dan shekara 53 a duniya, ya shigo kasar kongo daga kasar Rwanda, sannan ya je ya gana da shuwagabannin kungiyar M23 a birnin Goma, inda daga nan suke ikonsu a kan yankunan arewa da kudancin Kivu.

Gwamnatin tsetsekedi tana zargin Kabila da goyon bayan yan tawayen M23, haka ma ta bayyana cewa Jami’an tsaron kasar sun kai farmaki a kan gidan Kabila da ke kinsasa da wata gonarsa, iyalan Josepy Kabilan sun tabbatar da haka.

Makonni kafin dawowarsa gida, tsohon shugaban kasar ya bayyana cewa zai dawo kasarsa ne don ya taimaka wajen dawo da lafiya cikin kasar.

Daga karshe a wani bangare kuma ma’aikatar sharia ta kasar ta bayyana cewa ta fara shirin gabatar da Kabila a gaban kuliya saboda goyon bayan kungiyar M23.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta

A jiya Litinin ne dai gwamnatin kasar Holland ta sanar da hana wa minstocin tsaron kasa Itmir Bin Gafir, da na kudi, Bitsirael Smotrich shiga cikinta.

Kasar ta Holland ta zargi wadannan mutanen biyu da cewa suna ingiza sojojin HKI da yi wa Falasdinawa kisan kiyashi da kuma fadada yawan matsugunan ‘yan sahayoniya  a yankunan da aka ce nan ne za a kafa Daular Falasdinawa.

 Haka nan kuma gwamnatin kasar ta Holland ta kira yi jakadan HKI a birnin Hauge domin gargadinsa akan yanayin da ake ciki a Gaza, da cewa babu yadda za a iya ci gaba da jurewa akansa, ko kare dalilin jefa yankin cikin wannan halin.”

Wannan matakin na kasar Holland ya zo ne gabanin wani taro da tarayyar turai za ta yi a yau Talata domin jingine aikin tare da HKI a fagen nazari da bincike na ilimi, saboda ta ki tsagaita wutar yaki a Gaza.

Tun da fari, Fira ministan  kasar Holland Dick Schoof ya wallafa a sharin X cewa;  A yayin taron da kasashen turai za su yi, Kasarsa za ta  yi  matsin lamba akan ganin an dakatar da yarjejeniyar kasuwanci da HKI, haka nan kuma kakaba takunkumai akan shigar da kayanta na kasuwanci zuwa kasuwannin turai.

Fira ministan na kasar Holland ya ce, ya fada wa shugaban HKI Ishaq Herzog wannan matakin da suke son dauka ta hanyar tarayya turai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Bayyana Shirinsa Na Sake Tsayawa Takarar Shugabanci Karo Na Hudu
  •  Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta
  • Kasar Faransa Ta Yi Allah Wadai Da Harin Ta’addancin Da Aka Kai Birnin Zahedan Na Kasar Iran
  • Pezeshkiya: Iran A Shirye Take Don Mu’amala Amma Bazata Bar Hakkinta Ba
  • Iran Ta Ce Amurka Ce Bayan Hare-haren Da Aka Kai Zahidan
  • Shugaban Kasar Masar Ya Roki Trump Ya Kawo Karshen Yaki A Gaza
  • Mutanen Sweida Na Kasar Siriya Suna Fama da Rashin Abinci da Ruwa
  • Kungiyar Gwamnonin Jihohi Ta Jajintawa Jihar Adamawa Bisa Ambaliyar Ruwa A Yola
  • SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa
  • Dakarun Yemen Zasu Kara Daukan Matakai Kan Jiragen Ruwan Da Ke Hulda Da Isra’ila