Aminiya:
2025-04-30@19:18:07 GMT

Kada Kanawa su bari rigingimun siyasa su hana su zaman lafiya — Shettima

Published: 19th, April 2025 GMT

Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima ya shawarci Kanawa kan kada su bari bambance-bambancen aƙidu na siyasa su zama silar hana su zaman lafiya da haɗin kai.

Ya faɗi hakan ne a jawabinsa lokacin da ya je yi wa Shugaban APC na Kano, Abdullahi Abbas, ta’aziyar rasuwar mahaifinsa — Galadiman Kano, Abbas Sunusi.

Shin Mataimakin Gwamnan Bauchi ya ‘mari’ Ministan Tinubu? An shiga ruɗani kan satar al’aurar maza a ƙasar Chadi

Shettima ya jaddada muhimmancin zaman lafiya da haɗin kai, yana mai bayyana Kano a matsayin madubin Arewacin Nijeriya.

Yayin da yake nanata muhimmancin zaman lafiya, ya bayyana cewa kada a yi sake da Kano, inda ya buga misali da yadda rashin zaman lafiya ya ɗaiɗaita Jihar Borno.

Shettima ya yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki a fannin siyasa da su ajiye banbancin aƙidu, su bai wa ci gaban Kano fifiko a kan komai.

Ya tunatar da cewa Jihar Kano wata cibiya da kusan duk jihohin Arewa suka kewaye kuma ta zama tamkar wata ƙofa da ta zama mahaɗar jihohin

“Idan za ka je Borno ko Bauchi ko Sakkwato, dole ne sai ka bi ta Kano. Saboda haka Kano jiha ce ta kowa.

Aminiya ta ruwaito cewa, Gwamna Abba Kabir Yusuf ne ya yi Mataimakin Shugaban Ƙasar rakiya a yayin ziyarar ta’aziyyar da ya kai gidan marigayi Galadiman Kano.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano Siyasa zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Arsenal Da PSG: Wa Zai Yi Nasara A Gasar Zakarun Turai A Yau?

Wannan ya sa wasan yau zai zama mai ɗaukar hankali, domin kowanne daga cikinsu na burin ɗaukar kofin a karo na farko, domin a dakatar da yawan dariyar da ‘yan adawa ke musu.

A zagayen rukuni da suka haɗu a farkon wannan kakar, Arsenal ta lallasa PSG da ci 2-0.

Kocin Arsenal yanzu, Mikel Arteta, ya taɓa buga wasa a duka ƙungiyoyin.

Yana fatan ya zama kocin farko da zai jagoranci Arsenal ta lashe kofin Zakarun Turai.

Wannan ya sa magoya bayan Arsenal ke fatan ganin ƙungiyarsu ta yi abin mamaki a wasan da za a fara da misalin ƙarfe 8 na dare agogon Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa Gabon
  • Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya
  • Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APC
  • Arsenal Da PSG: Wa Zai Yi Nasara A Gasar Zakarun Turai A Yau?
  • Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai
  • Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
  • Shin Amurka Na Iya Komawa Kan Kadaminta A Matsayin Cibiyar Masana’antun Duniya?
  • Tawagar Jami’ai Da ‘Yan Kasuwar Ta Tunusiya Ta Gana Da Mataimakin Shugaban kasar Iran
  • Falasdinu: Mahmud Abbas Ya Nada Magaji Da Kuma Mataimakasa
  • Iran Da Rasha Sun Jaddada Yin Aiki Tare A Fagen Kiwon Lafiya