Shugaban Majalisar Neja Ya Mika Sakon Easter Ga Al’ummar Kirista.
Published: 19th, April 2025 GMT
Kakakin majalisar dokokin jihar Neja, Barr. Abdulmalik Sarkin-Daji, ya mika sakon taya murna ga al’ummar kiristoci a jihar da ma sauran sassan jihar bisa nasarar kammala azumin Easter na kwanaki 40.
A madadin shugabanni da membobin majalisar ta 10, shugaban majalisar ya yaba wa mabiya addinin kirista saboda sadaukarwar da suka yi da kuma ci gaban ruhaniya a wannan lokaci mai tsarki.
Duk da haka ya yaba musu bisa sadaukarwar da suka yi a wannan lokacin kuma fatan sabunta ruhi da aka samu a lokacin Azumi ya kawo zaman lafiya, farin ciki, da wadata ga kowa.
Barr AbdulMalik Sarkin Daji, ya amince da muhimmiyar rawar da shugabannin addinin Kirista ke takawa wajen jagorantar al’ummar Nijar cewa majalisar ta 10 za ta ci gaba da samar da dokokin da za su kawo wa al’ummar jihar tasiri kai tsaye kuma mai kyau.
.
Hakazalika ya ce majalisar dokokin jihar Neja ta ci gaba da jajircewa wajen ganin an samar da zaman lafiya a tsakanin dukkan mazauna yankin, ba tare da la’akari da addini ko al’ada ba.
Bikin Ista, ginshiƙin bangaskiyar Kirista, tashin Yesu Almasihu daga matattu, alamar nasara akan mutuwa da zunubi, taron tunatarwa ne na ikon canza bangaskiya da saƙon bege mai ɗorewa wanda ke bayyana a tsawon shekaru.
PR ALIYU LAWAL.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
Yayin ganawarsa da firaministan Thailand, Shugaba Xi Jinping ya ce a shirye kasarsa take ta karfafa hadin gwiwa da Thailand kan dabarun samun ci gaba, tare kuma da gabatar da gogewarta na samun ci gaba a sabon zamani, kuma ya yi kira da a gaggauta gina layin dogo tsakanin Sin da Thailand da bunkasa hadin gwiwa a bangaren cinikin amfanin gona da tattalin arziki mai kiyaye muhalli da kuma kirkire kirkiren fasaha. (Mai fassara: FMM)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA