Shugaban Majalisar Neja Ya Mika Sakon Easter Ga Al’ummar Kirista.
Published: 19th, April 2025 GMT
Kakakin majalisar dokokin jihar Neja, Barr. Abdulmalik Sarkin-Daji, ya mika sakon taya murna ga al’ummar kiristoci a jihar da ma sauran sassan jihar bisa nasarar kammala azumin Easter na kwanaki 40.
A madadin shugabanni da membobin majalisar ta 10, shugaban majalisar ya yaba wa mabiya addinin kirista saboda sadaukarwar da suka yi da kuma ci gaban ruhaniya a wannan lokaci mai tsarki.
Duk da haka ya yaba musu bisa sadaukarwar da suka yi a wannan lokacin kuma fatan sabunta ruhi da aka samu a lokacin Azumi ya kawo zaman lafiya, farin ciki, da wadata ga kowa.
Barr AbdulMalik Sarkin Daji, ya amince da muhimmiyar rawar da shugabannin addinin Kirista ke takawa wajen jagorantar al’ummar Nijar cewa majalisar ta 10 za ta ci gaba da samar da dokokin da za su kawo wa al’ummar jihar tasiri kai tsaye kuma mai kyau.
.
Hakazalika ya ce majalisar dokokin jihar Neja ta ci gaba da jajircewa wajen ganin an samar da zaman lafiya a tsakanin dukkan mazauna yankin, ba tare da la’akari da addini ko al’ada ba.
Bikin Ista, ginshiƙin bangaskiyar Kirista, tashin Yesu Almasihu daga matattu, alamar nasara akan mutuwa da zunubi, taron tunatarwa ne na ikon canza bangaskiya da saƙon bege mai ɗorewa wanda ke bayyana a tsawon shekaru.
PR ALIYU LAWAL.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Sarkin Gusau
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi alhinin rasuwar Sarkin Gusau, Dokta Ibrahim Bello na Jihar Zamfara.
Sarkin ya rasu da safiyar Juma’a yana da shekaru 71.
An yanke wa mutum 3 hukuncin kisa kan kisan kai a Gombe HOTUNA: Yadda Kwankwaso ya karɓi ’yan APC zuwa NNPP a KanoMai bai wa Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin watsa labarai, Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa.
Ya ce Sarkin mutum ne da ya sadaukar da rayuwarsa don hidimta wa al’ummarsa.
Shugaba Tinubu ya ce rasuwar Sarkin babban rashi ne, ba wai kawai ga mutanen masarautarsa ba, har da ƙasa baki ɗaya.
Ya yaba da jajircewarsa, kyakkyawan shugabancin da sadaukarwarsa ga jama’a.
Shugaban ƙasa ya miƙa ta’aziyyarsa ga gwamnatin Jihar Zamfara, mutanen jihar, da kuma iyalan marigayin.
Ya roƙi Allah Ya jiƙan Sarkin, Ya kuma yafe masa kurakuransa.