Fadar shugaban kasa ta musanta rahotannin da ke nuni da cewa an hana mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, GCON shiga fadar shugaban kasa, inda ta bayyana ikirarin a matsayin shirme, kage da kuma karya gaba daya.

 

Wata sanarwa da babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai da sadarwa na ofishin mataimakin shugaban kasa Stanley Nkwocha ya sanyawa hannu, ta ce rahoton da wasu shafukan da ba su da tushe suka yada shi, na cikin jerin labaran karya da aka kitsa domin haifar da rashin jituwa tsakanin shugaban kasa da mataimakinsa.

 

Sanarwar ta kara da cewa, “Wannan wani yunkuri ne mai rauni na cin mutuncin mutum da ofishin Mai Girma, Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima.

 

Nkwocha ya ce labarin da ake cewa sojoji dauke da makamai sun hana mataimakin shugaban kasa shiga fadar Shugaban kasa wato Villa ba wai kawai an yi ne ba haka kawai, a’a har ma ya nuna rashin fahimtar ayyukan gwamnati.

 

Sanarwar ta ce, wannan shi ne mafi girman furuci na fatar baka, kuma hakan yana nuni da cewa masu yin wannan tatsuniyoyi sun gaji da zargi da kuma hasashe, in ji sanarwar.

 

Wannan dai ba shi ne karon farko da fadar shugaban kasar ke yin watsi da irin wadannan rahotannin ba. Kwanaki kadan kafin hakan, ta karyata labaran karya da ke yawo a shafukan yakin neman zabe dauke da hoton shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu. Fadar shugaban kasar ta yi imanin cewa irin wannan karyar wani yunkuri ne na kawo cikas ga hadin kai da amincin shugabancin kasar.

 

Mataimakin shugaban kasar ya ci gaba da maida hankali kan ayyukan sa da kuma marawa shugaban kasar baya wajen cimma muradun ‘yan Najeriya. Sanarwar ta kara da cewa, ba shi da wani abin da zai raba hankali.

 

Nkwocha ya yabawa ‘yan Najeriya da ke ci gaba da nuna goyon bayansu ga gwamnatin Tinubu-Shettima, ya kuma bukaci kafafen yada labarai da su nemi bayanai daga majiyoyi masu inganci tare da yin taka-tsan-tsan wajen bayar da rahotanni masu ban sha’awa.

 

Sanarwar ta kara da cewa, “alkwarin da ke tsakanin wannan gwamnati da ‘yan Najeriya ya yiwu ne ta hanyar halaltaccen tsarin mulki.

 

Bello Wakili

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: shugaban kasar Sanarwar ta

এছাড়াও পড়ুন:

Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum

Rikicin jam’iyyar PDP ya ƙara tsananta bayan sakataren jam’iyyar na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, ya sanar da dakatar da shugaban jam’iyyar na ƙasa, Ambasada Illiya Damagum.

Yayin da yake yi wa manema labarai jawabi a Abuja, Anyanwu, wanda yake ɗan tsagin  Nyesom Wike, ya ce an dakatar da Damagum da wasu manyan jami’an jam’iyyar guda biyar saboda zargin rashin ƙwarewa, almundahana, da ƙin bin hukuncin kotu.

Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike

“Mun yanke shawarar dakatar da shugaban jam’iyyar na ƙasa, Ambasada Ilya Damagum, saboda rashin ƙwarewa, almundahana, da ƙin mutunta hukuncin kotu,” in ji Anyanwu.

“An dakatar da shi na tsawon wata guda, kuma dole ne ya gurfana gaban kwamitin ladabtarwa.”

Anyanwu, ya kuma yaba da hukuncin kotu wanda ya soke babban taron jam’iyyar na ƙasa, inda ya bayyana cewa wannan nasara ce ga mambobin PDP baki ɗaya.

“Muna jinjina wa ɓangaren shari’a bisa wannan hukunci da ya nuna adawa da zalunci da rashin bin doka. Wannan nasara ce ga kowane ɗan jam’iyyar PDP,” in ji shi.

Sauran da aka dakatar sun haɗa da mai magana da yawun jam’iyyar na ƙasa, Debo Ologunagba; mataimakin shugaban jam’iyyar na Kudu, Taofeek Arapaja.

Akwai kuma sakataren kuɗi na ƙasa, Daniel Woyenguikoro; jagoran matasan jam’iyyar, Sulaiman Kadade da mataimakin sakataren jam’iyyar na ƙasa, Setonji Koshoedo.

Sanarwar Anyanwu, na zuwa ne bayan ɓangaren Damagum ya dakatar da shi da wasu magoya bayan Wike, lamarin da ya ƙara ba tsananta rikicin shugabanci a jam’iyyar PDP.

Anyanwu, ya kuma sanar da naɗa Alhaji Abdulrahman Mohammed, mataimakin shugaban jam’iyyar na yankin Arewa ta Tsakiya, a matsayin sabon muƙaddashin shugaban jam’iyyar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
  • Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan
  • Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi
  • Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Duk Wani Kutse Na Isra’ila A Kudancin Kasar