Leadership News Hausa:
2025-11-02@21:16:46 GMT

Mene Ne Shirin Nukiliya Na Iran Kuma Me Amurka Ke So Ta Yi?

Published: 19th, April 2025 GMT

Mene Ne Shirin Nukiliya Na Iran Kuma Me Amurka Ke So Ta Yi?

Ta nanata cewa ba neman hada bam din nukiliya take yi ba, amma wasu kasashe – da kuma hukumar kula da makaman nukiliya ta duniya International Atomic Energy Agency (IAEA) – ba su yarda ba.

An fara zargin Iran ne game da shirin nata bayan an gano wasu boyayyun wuraren binciken nukiliya a 2002.

Hakan ya jawo karyewar wata yarjejeniya da ake kira Nuclear Non-Proliferation Treaty (NPT), wadda Iran ta kulla da wasu kasashe, wadda ta ke hana yaduwar makaman nukiliya a duniya.

NPT kan bai wa kasashe damar yin amfani da fasahar nukiliya wajen ayyukan lafiya, da noma ban da hada makamin nukiliya.

 

Yaya ci gaban shirin nukiliyar Iran yake?

Tun bayan ficewar Amurka daga yarjejeniyar da aka kira Joint Comprehensibe Plan of Action or JCPOA a 2018, Iran ta karya ka’idojinta a matsayin martani, wanda ya sa aka sake kakaba mata takunkumai.

Ta kara zuba dubban na’urorin tace ma’adanin Uranium wanda yarjejeniyar JPCOA ta haramta.

Hada makamin nukiliya na bukatar a inganta ma’adanin uranium zuwa kashi 90 cikin 100. A karkashin yarjejeniyar, an bai wa Iran damar inganta kashi 3.67 ne kawai ko kuma zuwa nauyin kilogiram 300 – wanda zai iya ba da damar ayyukan bincike amma bai kai na hada makami ba.

Amma zuwa watan Maris na 2024, hukumar IAEA ta ce Iran na da uranium kusan kilogiram 275 da ta inganta zuwa kashi 60 cikin 100. Hakan zai iya ba ta damar hada bam kamar shida idan ta kara inganta shi.

Jami’ai a Amurka sun ce sun yi imanin Iran za ta iya mayar da shi zuwa makami daya a cikin mako daya. Amma kuma sun ce Iran sai ta yi kamar shekara daya zuwa wata 18 kafin ta iya samar da cikakken makamin nukiliya.

Amma wasu kwararru na cewa za a iya gina karamin makamin cikin wata shida ko kasa da haka.

 

Me ya sa Trump ya cire Amurka daga yarjejeniyar?

Amurka da Majalisar Dinkin Duniya da Tarayyar Turai sun saka wa Iran takunkuman tattalin arziki daga 2010 saboda zargin cewa tana shrin hada nukiliya.

Sun hana Iran sayar da man fetur dinta a kasuwar duniya da kuma hana ta taba kudinta Dala biliyan 100 da ke kasashen waje. Tattalin arzikinta ya karye, kuma darajar kudinta ya yi ta karyewa, wanda ya jawo hauhawar farashi.

A 2015, Iran da manyan kasashen duniya shida – Amurka, Faransa, Rasha, Jamus, Birtaniya – suka kulla yarjejeniyar JCPOA.

Kasashen sun amince su dage wa Iran takunkumai bisa sharuddan yarjejeniyar.

An tsara yarjejeniyar za ta yi aiki tsawon shekara 15.

Lokacin da Donald Trump ya kama mulki ya fitar da Amurka daga yarjejeniyar a 2018, wadda babbar dirka ce a cikinta.

Ya ce yarjejeniyar ba ta da kyau saboda ba mai dorewa ba ce kuma ba ta yi magana kan shirin Iran na makamai masu linzami ba. Ya kara wa Iran takunkumai saboda ta dawo kan teburin tattaunawa.

Isra’ila ta yi ikirarin cewa Iran ta ci gaba da neman hada nukiliya a boye kuma za ta yi amfani da kudin da ta samu bayan cire tukunkumi wajen karfafa rundunar sojinta.

 

Me Amurka da Isra’ila ke so yanzu?

Da alama sanarwar da Trump ya bayar ta neman fara tattaunawa da Iran ta bai wa Isra’ila mamaki. Ya dade yana cewa zai iya kulla yarjejeniya mafi kyawu sama da JCPOA, amma har yanzu Iran ta yi watsi da bukatar.

Trump ya yi gargadi cewa idan Iran ba ta yarda da sabuwar yarjejeniya ba “zai kai musu hari”.

Mai bai shi shawara kan harkokin tsaro Mike Waltz ya ce Trump na son Iran ta “lalata baki dayan” shirin nukilyar tata, yana cewa: “Kamar ingantawa, ko hada makami, wato shirinta na makamai masu linzami.”

Duk da cewa Trump ya ce tattaunawar ta gaba da gaba ce, ministan harkokin Iran Abbas Araghchi ya ce tattaunawar da za a yi a Oman ba ta gaba da gaba ba ce. Ya ce a shirye suke su tattauna amma dole sai Trump ya amince cewa “babu maganar hari”.

Bayan sanarwar da Trump ya yi, Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce yarjejeniya daya da za su amince da ita ita ce wadda Iran za ta yarda da hakura da shirin nukiliya gaba daya.

Ya ce hakan na nufin: “Mu shiga mu tarwatsa masana’antun, mu lalata komai bisa sa ido da jagorancin Amurka.”

Abin da Isra’ila ke fargaba shi ne Trump zai iya yarda da wani abu kasa da lalata shirin na Iran gaba daya da zai yi kurin cim mawa a matsayin nasarar difilomasiyya.

Isra’ila da ba ta shiga yarjejeniyar NPT ba, ana ganin tana da makaman nukiliya, abin da ba ta taba amsawa ko karyatawa ba.

Isra’ila na ganin idan Iran ta samu nukiliya barazana ce a gare ta saboda har yanzu ba ta amince da ‘yancin Isra’ilar ba a matsayin kasa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Iran Nukiliya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza

Gwamnatin mamayar Isra’ila ta yanke hukuncin kisa kan masu fama da cutar kansa da kuma waɗanda suke fama da matsalar koda na mutuwa a Gaza domin hana fitar da su wata kasa don neman magani

Cibiyar Kare Hakkin Dan Adam ta Gaza ta bayyana matukar damuwarta game da tabarbarewar lafiyar marasa lafiya da ke fama da cutar kansa da kuma cutar koda a Zirin Gaza. Wadannan cututtuka sun kara ta’azzara ne sakamakon hare-haren sojojin mamayar Isra’ila kan Gaza da kuma ci gaba da killace yankin bayan tsagaita bude wuta, gami da hana shigar dq magunguna da kayayyakin ayyukan likitanci masu muhimmanci cikin yankin. Cibiyar ta kuma yi nuni da tsauraran matakan fitar da marasa lafiya zuwa ƙasashen waje don neman magani.

A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Lahadi, Cibiyar ta tabbatar da cewa, wannan yanayin ba shi da wata shakka cewa Isra’ila na aiwatar da manufar kisan gilla a kan dubban marasa lafiya ta hanyar hana su ‘yancinsu na rayuwa da magani da gangan, da kuma canza wahalarsu zuwa wani nau’in hukunci na gama gari.

Cibiyar ta ambaci majiyoyin lafiya da ke tabbatar da cewa, akwai marasa lafiya 12,500 da ke fama da cutar kansa a Zirin Gaza, ciki har da ƙananan yara. Ta lura cewa mata sun kai kusan kashi 52% na dukkan masu cutar kansa a Gaza.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher November 2, 2025 IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya November 2, 2025 Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci November 2, 2025 Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza November 2, 2025 Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran November 2, 2025 Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari November 2, 2025 Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon November 2, 2025 Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya November 2, 2025 Shugaban AmurkaTrump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya November 2, 2025 Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar November 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya yanke hulɗa da Amurka kawai — Sheikh Gumi
  • Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka
  • IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya
  • Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya
  • Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
  • HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa
  • M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi
  • Araqchi: Gwajin Makaman Nukiliya Na Amurka Babbar Barazana Ce Ga Duniya