Ana kashe ’yan Najeriya amma Tinubu ya fi damuwa da Zaɓen 2027 — SDP
Published: 19th, April 2025 GMT
Jam’iyyar adawa ta SDP buƙaci Shugaba Bola Tinubu da sauran shugabannin siyasa a Najeriya su dai shagala da batun zaɓen 2027, su mayar da hankalinsu wajen magance matsalar tsaro da ke ƙara mayar da ƙasar tamkar filin kisa.
SDP ta bayyana cewa kashe-kashe ɗaruruwan mutane da ke faruwa a faɗin ƙasar nan – Arewa da Kudu – musamman a makonnin da suka gabata, na da matuƙar tayar da hankali.
Sakataren Yaɗa Labarai na Ƙasa na SDP, Araba Rufus Aiyenigba, ya bayyana a wata sanarwa da ya fitar a daren Juma’a, cewa abubuwan takaicin sun hada da da kisan mafarautan Jihar Kano a jihar Delta, baya ga ayyukan ’yan ta’adda da hare-haren da a ka yi wa mutane sama da 100 a sassan jihar Filato.
Ya ce gwamnatin da ke kan mulki a yau ta rasa duk wata dabara mai ma’ana kuma ta kasa samar da wata mafita da za ta dakatar da wannan zubar da jini da ke gudana, yayin da ƙasar nan ke saurin zama filin kisa.
Makarantar Bare: Shekara 20 dalibai na karatu a matsanancin yanayi Masu garkuwa za su mutu ta hanyar rataya a Edo – Okepebolo“A wasu makonnin da suka gabata, an kai munanan hare-hare da kisan gilla da ƙona wasu maharba daga Jihar Kano a yankin Edo, a yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa arewa daga wani farauta a yankin Neja Delta.
“Haka kuma, a makon da ya gabata, an kashe sama da mutane ɗari ta hanyar kisan gilla tare da ƙona gidaje da yawa a Filato!
“An kuma ruwaito cewa wata sabuwar ƙungiyar ta’addanci mai suna ‘Makmuda’ ta kashe mutane da yawa, wanda ya ƙara dagula al’amuran ƙasarmu,” in ji Aiyenigba.
Ya yi zargin cewa jami’an tsaron ƙasar nan suna ƙara kasala da rashin ƙarfi, yayin da gwamnatin da ke kan mulki ta rasa duk wata dabara mai ma’ana kuma ta kasa samar da wata mafita.
Ya ce, “Abin damuwa ne yadda duk waɗannan kashe-kashe da ɓarna ke faruwa ba tare da an yi wani abu ba.
“’Yan siyasa a bayyane yake cewa, sun fi damuwa ne kawai da batun zaɓen 2027 da ke tafe. Muna buƙatar yin aiki don tabbatar da tsaron masu zaɓe kuma mu mallaki ƙasa kafin ma a fara maganar zaɓe,” in ji shi.
Kakakin jam’iyyar SDP na ƙasa ya ce yanzu ne lokacin da Tinubu zai nuna ƙarfin hali da ƙarfin zuciya a matsayinsa na shugaba, ya kuma yi abin da ya dace don tabbatar da tsaron al’ummar Najeriya.
“A matsayinsa na shugaban ƙasa, wajibi ne ya tabbatar da tsaron ’yan ƙasa, kamar yadda Kundin Tsarin Mulkin Najeriya ya tanada, cewa jin daɗin jama’a da tsaro su ne babban manufar gwamnati.”
Ya ci gaba da mika ta’aziyyar jam’iyyar bisa rashe-rashen da aka yi a sakamakon wadannan matsalolin tsaro.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Rashin Tsaro Siyasa Tsaro Zaɓen 2027
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
Mai kuɗin Afrika kuma Shugaban Matatar Mai ta Ɗangote, Alhaji Aliko Ɗangote, ya zargi wasu manyan masu harkar mai da shirya maƙarƙashiya domin kashe matatarsa.
Ɗangote ya yi zargin cewa miyagun ’yan kasuwan suna ƙoƙarin kashe matatar mansa mai darajar dala biliyan 20, kamar yadda aka kashe masana’antar tufafi ta ƙasar.
Ya bayyana haka ne a ranar Litinin a Legas yayin bikin cika shekara ɗaya da fara samar da fetur a matatar, inda ya ce tafiyar ta kasance cike da ƙalubale tun daga farko.
“A gaskiya tafiyar shekara ɗaya da ta wuce ta yi mana matuƙar wuya. Mun zo mu sauya tsarin kasuwancin man ƙasa. Amma wasu na ganin mun raba su da hanayar cin abinci bakinsu,” in ji shi.
’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati BaYa ci gaba da cewa, “Amma abin da muka yi shi ne mun sa Najeriya da nahiyar Afirka gaba ɗaya su yi alfahari.”
Ɗangote ya ce matatar ta riga ta fitar da lita biliyan 1.8 na man fetur zuwa ƙasashen waje cikin watanni uku da suka gabata, sannan tana da isasshen ƙarfi wajen cika buƙatar cikin gida.
Ya ce tun daga fara aikin matatar a watan Satumbar 2024, dogayen layukan man fetur da suka fi shekaru 50 ana fama da su a Najeriya sun zama tarihi.
Ɗangote ya ƙara da cewa farashin fetur ya sauka daga kusan Naira 1,100 zuwa N841 a wasu jihohi, kuma da zarar sabbin motocin gas (CNG) masu dakon mai sun fara aiki a duk faɗin ƙasar, rage farashin zai fi tasiri.
Ya kuma bayyana cewa sabbin motocin CNG 4,000 za su samar da aƙalla ayyukan yi 24,000, ciki har da direbobi, makanikai da sauran ma’aikata.
“Ba mu kore kowa daga aiki ba, sai dai muna ƙara samar da ayyuka,” in ji shi.
Ɗangote ya zargi masu harkar mai da haɗa kai da ’yan kasuwa na cikin gida da na waje da ƙoƙarin hana nasarar matatar.
“Yadda aka hallaka masana’antar yadi, haka suke ƙoƙarin kashe matatar mu,” in ji shi.
A kan zargin cewa bai wadatar da ƙasa da fetur ba, sai ya mayar da martani da cewa: “Idan ba mu da ƙarfin samar da mai, me ya sa muke fitarwa zuwa ƙasashen waje?”
Ya kuma yi ba’a ga Ƙungiyar Ma’aikatan Mai (NUPENG) wadda ta ce rage farashin fetur na matatar Dangote “kyautar Girka ce.” Dangote ya ce: “Ko da kuwa kyautar Girka ce, ai kyauta ce, za ta kuma ci gaba da kasancewa.”
Ya jaddada cewa abin da Najeriya ke buƙata yanzu shi ne kare masana’antunta, domin ci-gaban tattalin arziki da kuma rage dogaro da shigo da kaya daga waje.