Ana kashe ’yan Najeriya amma Tinubu ya fi damuwa da Zaɓen 2027 — SDP
Published: 19th, April 2025 GMT
Jam’iyyar adawa ta SDP buƙaci Shugaba Bola Tinubu da sauran shugabannin siyasa a Najeriya su dai shagala da batun zaɓen 2027, su mayar da hankalinsu wajen magance matsalar tsaro da ke ƙara mayar da ƙasar tamkar filin kisa.
SDP ta bayyana cewa kashe-kashe ɗaruruwan mutane da ke faruwa a faɗin ƙasar nan – Arewa da Kudu – musamman a makonnin da suka gabata, na da matuƙar tayar da hankali.
Sakataren Yaɗa Labarai na Ƙasa na SDP, Araba Rufus Aiyenigba, ya bayyana a wata sanarwa da ya fitar a daren Juma’a, cewa abubuwan takaicin sun hada da da kisan mafarautan Jihar Kano a jihar Delta, baya ga ayyukan ’yan ta’adda da hare-haren da a ka yi wa mutane sama da 100 a sassan jihar Filato.
Ya ce gwamnatin da ke kan mulki a yau ta rasa duk wata dabara mai ma’ana kuma ta kasa samar da wata mafita da za ta dakatar da wannan zubar da jini da ke gudana, yayin da ƙasar nan ke saurin zama filin kisa.
Makarantar Bare: Shekara 20 dalibai na karatu a matsanancin yanayi Masu garkuwa za su mutu ta hanyar rataya a Edo – Okepebolo“A wasu makonnin da suka gabata, an kai munanan hare-hare da kisan gilla da ƙona wasu maharba daga Jihar Kano a yankin Edo, a yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa arewa daga wani farauta a yankin Neja Delta.
“Haka kuma, a makon da ya gabata, an kashe sama da mutane ɗari ta hanyar kisan gilla tare da ƙona gidaje da yawa a Filato!
“An kuma ruwaito cewa wata sabuwar ƙungiyar ta’addanci mai suna ‘Makmuda’ ta kashe mutane da yawa, wanda ya ƙara dagula al’amuran ƙasarmu,” in ji Aiyenigba.
Ya yi zargin cewa jami’an tsaron ƙasar nan suna ƙara kasala da rashin ƙarfi, yayin da gwamnatin da ke kan mulki ta rasa duk wata dabara mai ma’ana kuma ta kasa samar da wata mafita.
Ya ce, “Abin damuwa ne yadda duk waɗannan kashe-kashe da ɓarna ke faruwa ba tare da an yi wani abu ba.
“’Yan siyasa a bayyane yake cewa, sun fi damuwa ne kawai da batun zaɓen 2027 da ke tafe. Muna buƙatar yin aiki don tabbatar da tsaron masu zaɓe kuma mu mallaki ƙasa kafin ma a fara maganar zaɓe,” in ji shi.
Kakakin jam’iyyar SDP na ƙasa ya ce yanzu ne lokacin da Tinubu zai nuna ƙarfin hali da ƙarfin zuciya a matsayinsa na shugaba, ya kuma yi abin da ya dace don tabbatar da tsaron al’ummar Najeriya.
“A matsayinsa na shugaban ƙasa, wajibi ne ya tabbatar da tsaron ’yan ƙasa, kamar yadda Kundin Tsarin Mulkin Najeriya ya tanada, cewa jin daɗin jama’a da tsaro su ne babban manufar gwamnati.”
Ya ci gaba da mika ta’aziyyar jam’iyyar bisa rashe-rashen da aka yi a sakamakon wadannan matsalolin tsaro.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Rashin Tsaro Siyasa Tsaro Zaɓen 2027
এছাড়াও পড়ুন:
Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu
Isra’ila ta kai hare-hare da dama a safiyar Alhamis kan yankunan gabashin Khan Younis, a kudancin Zirin wanda ke nuna yadda isra’ila ke ci gaba da keta yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma.
A cewar kafofin watsa labaran Falasdinawa, sama da hare-hare 10 a jere Isra’ila ta kai.
Bidiyo da ke yawo a shafukan sada zumunta sun nuna makamai masu linzami na dira akan wuraren zama a gabashin birnin.
A lokaci guda, tankunan yaki na Isra’ila da motocin sulke sun yi ruwan bama-bamai a yankunan zama a gabashin Gaza.
Sojojin Isra’ila sun kuma lalata gidaje da dama a gabashin birnin Gaza. Kasa da awa daya bayan haka, sojojin gwamnatin sun sake kai hari kan gidajen fararen hula a wannan yanki.
Hakazalika, sojojin Isra’ila na ci gaba da kai hari kan yankunan arewa maso gabashin Khan Younis, da kuma unguwannin Ma’an, Sheikh Nasser, da Joura al-Lout a kudancin birnin.
Wannan mummunan harin sama ya biyo bayan wani mummunan harin bam da ya kashe mutane sama da 109, ciki har da akalla yara 52, a fadin yankin Falasdinawa da yaki ya daidaita.
Hamas ta zargi gwamnatin Sahyoniya da karya yarjejeniyar tsagaita wuta.
Kungiyar ta yi kira ga bangaroron da suka shiga tsakani a yarjejeniyar tsagaita wutar, wato Masar, Qatar, Turkiyya da Amurka, da su dauki mataki nan take don matsa lamba ga gwamnatin isra’ila.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sudan : Kasashen duniya na tir da cin zarafi a El-Fasher October 30, 2025 Iran Ta Jaddada Bin Hanyar Diflomasiya Ko Da A Lokacin Yaki Ne Amma Ba Zata Amince Da Bin Umarni Ba October 30, 2025 Qalibaf: Amurka Tana Yaudarar Duniya Da Zaman Lafiya, Alhalin Tana Ci Gaba Da Kai Harin Wuce Gona Da Iri October 30, 2025 Ci Gaba Da Killace Gaza Bayan Tsagaita Bude Wuta Ya Janyo Mutuwar Mutane 1000 A Yankin October 30, 2025 Kungiyar Rapid Support Forces Ta Sanar Da Kafa Kwamitin Bincike Kan Cin Zarafin Al’umma A El Fasher October 30, 2025 An Kafa Dokar Ta Baci A Darul-Salam Saboda Tarzoman Zaben Shugaban Kasa A Tanzania October 30, 2025 Rasha Da Amurka Sun Sake Dawo Da Gwaje-gwajen Makaman Nukiliya October 30, 2025 Kasar Czech Ta Hana Wa Wani Sojan HKI Shiga Kasar Bisa Gargadin Faransa October 30, 2025 Sojojin HKI Sun Kutsa Kudancin Lebanon October 30, 2025 Adadin Falasdinawan Da Su Ka Yi Shahada A Cikin Sa’o’i 24 Sun Haura 100 October 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci