Bugu da kari, saboda karancin masu sayen Kwan, musamman sakamakon matsin tattalin arziki da ake fama da shi, ana kara samun masu sayen Kwan don amfani da shi, wanda hakan ya sanya ake ci gaba da samun Kwan da ba a sayar ba.

Misali, a makwanni biyu da suka gabata a garin Jos, an samu matukar raguwar farashin Kwan, inda ake sayar da shi kasa da Naira 3,900 zuwa Naira 4,000.

Sai dai, a wannan makon an dan samu karin farashin, wanda ya kai daga Naira 4,200 zuwa 4,300.

Daya daga cikin irin wadannan masu kiwon Kajin na gidan gona, Muhammad Bello Ibrahim, ya bayyana bacin ransa kan yadda wannan matsala ke ci gaba da faruwa.

“Masu sana’ar kiwon Kajin a yanzu haka, suna ci gaba da fuskantar kalubalen rashin samun masu sayen Kwan,” in ji Bello.

Ya ci gaba da cewa, a baya; a karkashin shirye-shiryen ciyarwa na gwamnati, ana karfafa wa wasu jihohin sayen Kwan da ake bai wa ‘yan makarantar firamere, domin amfanin marasa lafiya da aka kwantar a asibiti da kuma amfanin wadanda ake tsare da su a gidan gyaran hali, amma kusan yanzu, shirye-shiryen sun tsaya cak.

Bisa wani bincike da aka gudanar a garin na Jos, duk da raguwar da aka samu na farashin Kwan, ana ci gaba da fuskatar karancin masu saye, wanda kuma hakan ya sa ake samun kwantan Kwan.

Hakan na kuma faruwa ne a yayin da ake ci gaba da fuskantar tsananin zafi, a jihohin kasar ciki har da garin na Jos.

Wata mai kiwon Kajin gidan gona a Jihar Filato, Nanji Gambo-Oke, ta sanar da cewa, kiwon Kajin a jihar, na fuskanta babban kalubale.

A cewar tata, kashi 80 cikin dari na Kwan da ake kyankyashewa a jihar, makwabtan jihar ne ke zuwa saye, ciki har da babban birnin tarayyar Abuja.

Ta kara da cewa, a bangaren gwamnatin jihar kuma tana nuna halin ko in kula dangane da kwantan Kwan da masu kiwon a jihar ke ci gaba da samu.

“Babu wani dauki da masu kiwon Kajin gidan gonar a jihar ke samu daga bangaren gwamnatin jihar, wanda hakan ke ci gaba da jefa su cikin halin tsaka mai wuya”, in ji Nanji.

Sai dai, Shugabar Kungiyar Masu Kiwon Kajin Gidan Gonar, reshen jihar Madam Shinkur Angela Jima, ta sanar da cewa, gwamnatin jihar na nuna goyon baya ga fannin.

Ta kara da cewa, a yanzu haka, gwamnatin na kokarin samar da tsare-tsaren da za ta tallafa wa masu kiwon a jihar.

Bugu da kari, a Jihar Neja ma, masu kiwon Kajin na ci gaba da fuskantar kalubalen rashin samun masu sayen Kwan da kuma rashin samun kayan aiki na zamani, wanda hakan ke jawo lalacewar Kwan nasu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Asara masu sayen Kwan

এছাড়াও পড়ুন:

Rashin wutar lantarki ya durƙusar da kasuwanci a Arewa Maso Gabas

Rashin wutar lantarki a Arewa maso Gabashin Najeriya ya tilasta wa jama’a da ’yan kasuwa zaman ɗari-ɗari da asarar dukiya, sakamakon aikin da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Ƙasa (TCN), ke yi na aikin sabbin turakun wutar lantarki.

Rashin wutar, wanda ya fara daga ranar 10 zuwa 14 ga watan Yuni, ya shafi layin wutar lantarki na Jos–Bauchi–Gombe mai ƙarfin 132kV.

An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a Filato  Hajjin 2025: Jihohi 11 sun kashe N6.2bn wajen tallafa wa Alhazai

A Jihar Adamawa, musamman a birnin Yola, jama’a na cikin matsanancin hali.

Hajiya Aisha Babangida daga Jimeta, ta ce rashin wutar ya tilasta masa soye dukkanin naman ragon sallarta domin babu wutar da za ta ajiye shi a firinji.

“Na fi son dafawa, amma dole na soya gaba ɗaya. Wannan matsala ta wuta ta zo ne a lokacin da ake buƙatar wutar,” in ji ta.

Kasuwanci da harkokin yau da kullum sun tsaya cak a wurare da dama.

Adamu Abubakar, mai sayar da lemun kwalba a kasuwar Jimeta, ya koka da cewa rashin sanyin ruwa ya rage masa yawan kwastomomi.

“Mutane na so ruwan sanyi, amma ba zan iya samun mai sanyi ba. Ina amfani da ƙanƙara ne yanzu don na ci gaba da kasuwancina,” in ji shi.

Muhammad Zaharaddeen, wani barber mai shagon aski a Bauchi, ya ce kasuwancinsa ya durƙushe sakamakon rashin wutar lantarki.

“Shagona na buƙatar wutar lantarki sosai. Ko da na kunna janareta, farashin mai ya tashi fiye da yadda mutane ke biya a baya,” in ji shi.

“Da ba don wani ɗan kasuwanci da nake yi a gefe ba, da ko abinci ba zan iya siya ba.”

A Jalingo, babban birnin Jihar Taraba, asibitoci da ƙananan ‘yan kasuwa na kokawa kan hauhawar kuɗin aiki.

Asibitin Federal Medical Centre ya koma amfani da janareta, wanda hakan ke sa wa ana biyan maƙudan kuɗaɗe wajen zuba man fetur.

“An daɗe da yanke wutarmu, yanzu da aka dawo mana da ita, sai kuma ga wannan matsalar. Duk manyan na’urorinmu suna amfani ne da dizal,” in ji Dokta Aisha Adamu Sani, daraktar asibitin.

Masu niƙa, masu walda da masu ɗinki a Jalingo sun dakatar da aiki.

Mallam Haruna Garba, wanda ke da injin niƙa, ya ce ya rufe shagonsa gaba ɗaya.

“Ba zan iya niƙa babu wutar lantarki ba. Man fetur ya yi tsada sosai. Na rufe kasuwancina na ɗan lokaci,” in ji shi.

A Damaturu, babban birnin Jihar Yobe, al’umma na fama da ƙarancin ruwa da hauhawar farashin ruwan sanyi da kayan masarufi.

Musa Adamu, mai sayar da lemu, ya ce: “Babu wuta, babu sanyi. Dole na ɗan kara farashi, amma ya kamata jama’a su fahimtci rayuwar da ake ciki,” in ji shi.

Masu ƙananan sana’o’i irin su Yusuf Bukar, wani masassaƙa a Damaturu, na kashe dubban Naira kullum wajen siyan mai domin kammala ayyukansu.

“Idan wannan hali ya ci gaba, zan rasa kwastomomina. Na kashe Naira 10,000 a jiya kacal a kan mai,” in ji shi cikin baƙin ciki.

TCN ta bayyana cewa katse wutar na da matuƙar muhimmanci domin kammala gina sabbin turakun wuta masu ƙarfin 330kV domin inganta tsarin samar da wutar a yankin.

Kakakin TCN, Ndidi Mbah, ta ce turakun za su zama mafita daga yawan katsewar wuta a gaba.

“Da zarar an kammala aikin, za a iya amfani da layin Bauchi da Gombe. Jos ma za ta iya riƙa kai wa Bauchi wuta kai-tsaye,” in ji ta.

Sai dai masana sun ɗora alhakin matsalar kan rashin wata hanya da za ake samar wa Arewa maso Gabas wuta.

Wani tsohon ma’aikacin TCN da ya nemi a sakaya sunansa ya ce: “Idan layin Jos-Bauchi-Gombe ya faɗi, kowa zai tsunduma cikin duhu. Ya kamata a ce an gina wata hanya ta biyu tun da daɗewa.”

Wannan ba shi ne karon farko da yankin ke faɗawa cikin duhu ba.

A baya, wasu da ba a san ko su waye ba sun lalata turakun wuta da bam, wanda ya sa aka ɗauke wuta gaba ɗaya a Arewa maso Gabas.

Sai dai wannan katsewar wutar wata hujja ce ta gaggawar sake fasalin tsarin wutar lantarki a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba
  • Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara
  • Rashin wutar lantarki ya durƙusar da kasuwanci a Arewa Maso Gabas