Masarautar Gumel ta ce za ta bayar da dukkan goyon baya da hadin kai da ake bukata domin ci gaban yankin kasuwancin da ba shida shinge na Maigatari a jihar Jigawa.

 

Mai Martaba Sarkin Gumel Alhaji Ahmad Mohammad Sani ya bayyana haka a lokacin da ya karbi bakuncin mambobin kwamitin Jiha mai kula da shiyyar fitar da kaya ko kasuwanci maras shinge na Maigatari a fadar sa.

 

Ya ce, nan ba da dadewa ba majalisar masarautar za ta shirya taro da hakiman Gundumomi da Unguwanni da Kauyuka domin fadakar da al’ummarsu kan gudunmawar da suke bukata domin samun nasarar wannan yankin.

 

Sarkin wanda ya samu wakilcin Dallatun Gumel, Alhaji Musa Ayuba ya ce aikin noman rani da asibitin kashi da cibiyar dialysis da gwamnatin Malam Umar Namadi ta kafa a Gumel ayyuka ne da ke yin tasiri kai tsaye ga rayuwar al’ummar yankin.

 

Tun da farko shugaban kwamitin kula da shiyyar fitar da kaya da babu haraji ko shinge na jiha kuma kwamishinan kasafin kudi da kididdiga Alhaji Babangida Umar Gantsa ya ce sun je fadar sarkin ne domin sanar da shi irin nasarorin da aka samu tare da neman hadin kan sa da addu’o’i na uba.

 

Gantsa, ya kara da cewa gwamnati ta kashe makudan kudade wajen samun Amincewa da Lasisi domin sanya Maigatari fa matsayin wata kasuwa ko yanki da za a yi cinikayya maras shinge ko haraji don bunkasar Jihar Jigawa da kasa baki daya.

 

Shima da yake nasa jawabin Hakimin Gumel Arewa, Alhaji Sani Abdullahi Babandi ya yi kira ga ‘yan kwamitin da su tuntubi hukumomin da abin ya shafa don gyara hanyar gwamnatin tarayya da ta hada Gumel zuwa Maigatari domin samun damar shiga yankin cikin kwanciyar hankali.

 

USMAN MZ

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Maigatari

এছাড়াও পড়ুন:

EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Zargi Aikata Damfara A Intanet A Kaduna

Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙi Zagon Ƙasa (EFCC), ta kama mutane 11 da ake zargi da aikata damfara a Intanet a Jihar Kaduna.

Kakakin hukumar EFCC, Dele Oyewale, ya bayyana cewa an kama waɗanda ake zargin ne a unguwannin Mahuta da Barnawa bayan samun sahihan bayanai game da ayyukansu na yaudara ta yanar gizo.

Yadda Kasar Sin Ta Zo Da Sabon Salon Zamanantar Da Sashen Jigilar Kayayyaki Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Kaso Kusan 80% Sun Soki Musabbabin Barkewar Tarzoma A Amurka

A lokacin da aka kama su, EFCC ta ƙwace wasu kayayyaki daga hannunsu da suka haɗa da mota ƙirar Mercedes Benz C300 mai launin baƙi, wayoyi 14, kwamfutoci guda biyu, iPad, na’urorin mifi guda biyu, lasifikar JBL guda ɗaya, da kuma lasifikar zealot guda ɗaya.

EFCC ta ce za a gurfanar da su gaban kotu da zarar ta kammala bincike.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Miliyoyin Mutane Sun Gudanar  Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya
  • Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki
  • EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Zargi Aikata Damfara A Intanet A Kaduna
  • NAJERIYA A YAU: 12 Ga Yuni: Me Ranar Dimokuraɗiyya Ke Nufi Ga Talakan Najeriya?
  • Kasashen Iran Masar Da Kuma Omman Sun Gudanar Da Taro A Oslo