HausaTv:
2025-06-15@09:44:57 GMT

Iran: Akwai damammaki na diflomasiyya da za mu jarraba aniyar Amurka a kansu

Published: 11th, April 2025 GMT

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmaeil Baqaei ya bayyana cewa, ma’a, kwana guda gabanin tattaunawar da ake jira a kasar Oman tsakanin Amurka da Iran kan shirin nukiliyar kasar Iran, damammaki da daman a diflomasiyya da Amurka za ta iya tabbatar da aniyarta a kansu

Baqaei ya rubuta a dandalin  X, “Ya kamata Amurka ta mutunta wannan shawarar da aka yanke duk da cewa ana fama da rikici.

“Ba za mu yanke hukunci ba, Muna da niyyar tantance niyyar dayan bangaren kuma za mu tabbatar da hakan a wannan Asabar,” in ji jami’in diflomasiyyar na Iran, ya kara da cewa Iran “za ta yi tunani kuma ta mayar da martani ga kowane mtaki.”

A ranar Litinin shugaban Amurka Donald Trump ya ba da sanarwar cewa gwamnatinsa za ta shiga tattaunawa da Iran.

A ci gaba da tattaunawar da za a yi a ranar Asabar, bangarorin biyu  sun yi musayar kalamai masu zafi, inda Trump ya yi barazanar daukar matakin soji idan tattaunawar ta ci tura.

Dangane da gargadin na Trump, wani babban mataimaki ga jagoran Iran Ayatollah Sayyed Ali Khamenei ya ce Iran za ta iya daukar matakan da duk ta ga sun dace a kan wannan lamari.

Taron na ranar Asabar na zuwa biyo bayan wata wasika da Trump ya aikewa Sayyed Khamenei a watan da ya gabata, inda ya bukaci Tehran da ta shiga tattaunawa tare da yin gargadin cewa matakin soji na kan teburi idan Iran ta ki amincewa.

Tehran ta bayyana aniyar ta na shiga tattaunawar kai tsaye amma muddin Washington ta ci gaba da manufofinta na “mafi girman matsin lamba”.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba

Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya ce sojojin kasar Iran ba za su sararawa gwamnatin Isra’ila ba.

Jagoran ya bayyana hakan ne a wani sakon bidiyo ga al’ummar Iran ranar Juma’a biyo bayan hare-haren wuce gona da iri da Isra’ila ta yi kan kasar wanda ya kashe fararen hula, masana kimiyya da kwamandojin soji.

Ayatullah Khamenei ya kara da cewa gwamnatin Isra’ila ba za ta kubuta daga wannan aika-aika ba, yana mai tabbatar wa al’ummar Iran cewa ba za a yi sakaci kan hakan ba.

Jagoran ya jaddada cewa muguwar gwamnatin sahyoniya ta tafka babban kuskure, sannan kuma shelanta yaki ne kan Iran.

Ayatullah Khamenei ya ci gaba da cewa: dukkanin jami’an kasar Iran da bangarori daban-daban na siyasa da kuma al’ummar Iran suna da ra’ayi daya dangane da wajabcin daukar wani mataki mai karfi wajen tunkarar gwamnatin sahyoniya ta ‘yan ta’adda.

Jagoran ya kara da cewa, bai kamata gwamnatin Isra’ila ta yi tunanin cewa ta ci bulus ba, kuma komi ya wuce.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran
  • Oman ta tabbatar da soke tattaunawar Iran da Amurka zagaye na shida
  • Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin
  • Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa
  • Ranar Dimokuraɗiyya: Gwaman Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa