Iran ba ta amince da Amurka ba, amma za ta gwada su (Araghchi)
Published: 9th, April 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya ce Amurka na da masaniya kan irin karfin kare kai da Jamhuriyar Musulunci ta Iran ke da shi, yayin da ya ce kasar ta shirya tsaf domin kare kanta.
Ya kuma jaddada cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba ta yarda da Washington ba, amma duk da haka za ta gwada ta yayin tattaunawar da za a yi nan gaba a ranar Asabar mai zuwa,” in ji Abbas Araghchi yayin wani taron manema labara a Aljeriya.
Babban jami’in diflomasiyyar ya bayyana cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba ta neman yaki, amma idan ya zama dole ta san yadda za ta kare kanta. »
“Muna shakkar aniyar Amurka kuma ba mu da tabbacin cewa suna da niyyar gudanar da tattaunawa ta gaske, amma za mu gwada su.”
Kalaman na baya-bayan nan sun shafi tattaunawar da ake sa ran za a fara tsakanin Araghchi da manzon Amurka na yankin Steve Witkoff a Muscat babban birnin kasar Omani ranar Asabar tare da ministan harkokin wajen Omani Badr bin Hamad Al Busaidi a matsayin mai shiga tsakani.
Haka nan kuma jami’in diflomasiyyar na Iran ya yi watsi da zargin kasashen yamma – karkashin jagorancin Washington – cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran na neman mallakar makamin nukiliya.
Ya ce zargin da ake yi wa Iran na neman mallakar makamin nukiliya, zargi ne mara tushe.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Jamhuriyar Musulunci ta Iran
এছাড়াও পড়ুন:
Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Bayyana Sabon Salon Mayar Da Martani Kan Isra’ila
Dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran sun yi bayani kan sabon salon mayar da martani kan Isra’ila a harin ‘Alkawarin Gaskiya na 3″
Ma’aikatar hulda da jama’a ta dakarun kare juyin juya halin Musulunci ta Iran a cikin wata sanarwa da ta fitar a yammacin jiya Asabar ta sanar da cewa: Dakarun tsaron sararin samaniyar IRGC sun kaddamar da wani sabon farmakin hadin gwiwa na “Alkawarin Gaskiya na 3” ta hanyar amfani da makamai masu linzami da jirage masu saukar ungulu a matsayin mayar da martani ga sabon farmakin da yahudawan sahayoniyya suka yi kan yankunan Iran.
A cikin wata sanarwa da ma’aikatar hulda da jama’a ta IRGC ta fitar ta bayyana cewa: Dakarun tsaron sararin samaniyar IRGC sun kaddamar da wani sabon salon farmakin hadin gwiwa na “Alkawarin Gaskiya na 3” kan yankunan haramtaciyar kasar Isra’ila da muhimman cibiyoyinta ta hanyar amfani da makamai masu linzami da jirage marasa matuka don mayar da martani ga sabon harin wuce gona da iri da yahudawan sahayoniyya suka yi kan yankunan kasar Iran.