Rahoto : Amurka za ta iya janye sojoji 10,000 daga Tsakiyar Turai
Published: 9th, April 2025 GMT
Amurka za ta iya janye sojoji 10,000 daga Gabashin Turai, kamar yadda rahoton NBC News ya bayyana.
A shekarar 2022, tsohon shugaban Amurka Joe Biden ya tura karin sojoji 20,000 zuwa yankin bayan Rasha ta kai hari Ukraine.
A ranar Talata, NBC ta ruwaito cewa jami’ai shida daga Amurka da Turai sun tabbatar da tattaunawa kan rage yawan sojojin da aka tura, inda aka fi mayar da hankali kan rage adadin a Romania da Poland.
Shugaba Donald Trump yana kokarin kawo karshen yakin Ukraine da aka shafe fiye da shekaru uku anayi tun bayan hawansa mulki, amma har yanzu bai cimma nasarar warware matsalar ba.
Ya sha sukar NATO, yana mai jaddada cewa ya kamata Turai ta dauki karin nauyi wajen kare kanta ta hanyar kara kashe kudi kan harkokin tsaro, da kuma jagorantar samar da makamai ga Ukraine.
A halin yanzu, akwai kimanin sojojin Amurka 100,000 da ke Turai, inda 65,000 daga cikinsu ke zama a nahiyar ta dindindin, to saidai masana na ganin janye dakarun na Amurka zai karawa Rasha karfi ne a yakin da ta ke yi Ukraine.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Katafaren Jirgin Daukar Jiragen Yaki Na Kasar Amurka Harry Truman Zai Fice Daga Tekun Maliya
Rahotannin da suke fitowa daga kasar Yemen na cewa katafaren jirgin ruwa mai daukar jiragen saman yaki malakar klasarAmurka wato USS Harry Truman zai fice daga tekun red sea da nan kusa saboda makaman kasar Yemen da suka fada mata.
Tashar talabijin ta Almasirah ta kasar Yemen ta nakalto wani jami’in ma’aikatar tsaron kasar wanda baya son a bayyana sunansa yana cewa, saboda yawan hare haren da sojojin Yemen suka kaiwa jirgin, wadanda suka hada da amfani da makamai masu linzami samfurin Crusse da kuma Balistic, har ila yau da jiragen yaki masu kunan bakin waken da suka fada a kansa. A yanzun ya zama dole jirgin ya fice daga tekun.
Tun cikin watan Maris da ya gabata ne gwamnatin shugaba Trump ta fara kaiwa kasar yemen hare-hare da jiragen sama wadanda suke tashi daga sansanin jiragen yaki da ke kan wannan jirgin. Saboda tilastawa kasar Yemen dakatar da kai hare-hare a kan HKI, don ta kawo karshen tallafawa Falasdinawa a Gaza.
Amma ya zuwa yanzu hare-haren na Amurka sun kasa kaiwa ga bukata, majiyar gwamnatin kasar ta yemen ta ce hare-haren Amurka a kasar ba zasu sa ta dakatar da tallafawa Falasdinawa, da kuma hanata kai hare hare kan jiragen kasuwanci na HKI masu wucewa ta tekun red sea ba.
A wani labarin kuma hare haren na sojojin yemen sun sa wani jiegin yakin Amurka samfurin F-18 ya fada cikin ruwa a tekun na Red Sea a kokarin kaucewa makaman sojojin Yemen.