HausaTv:
2025-06-15@13:05:42 GMT

An sake zanga-zangar kin jinin gwamnatin Netanyahu a Tel-Aviv

Published: 8th, April 2025 GMT

A Isra’ila dubban masu zanga-zanga ne suka fito kan titunan birnin Tel Aviv a wata sabuwar zanga-zangar kin jinin gwamnati a daidai lokacin da firaminista Benjamin Netanyahu ya gana da shugaban Amurka Donald Trump a birnin Washington.

Masu zanga-zangar a ranar Litinin sun yi Allah wadai da manufofin Netanyahu, ciki har da yunkurinsa na korar manyan jami’an tsaro da na shari’a na gwamnatin.

Sun kuma yi Allah wadai da sake dawo da yakin kisan kare dangi da ake yi wa al’ummar Gaza.

Iyalan ‘yan Isra’ilar da aka yi garkuwa da su a Gaza su ma sun shiga zanga-zangar, inda suka bukaci a kawo karshen yakin da kuma kulla yarjejeniyar tabbatar da sakin mutanen da aka kama.

Kungiyar dai ta ce za ta saki sauran mutanen da ake garkuwa da su ne kawai idan an sako sauren fursunonin Falasdinawa da Isra’ila ke rike da a gidajen yarinta, da kuma tabbatar da tsagaita bude wuta, da kuma janyewar Isra’ila gaba daya daga Gaza.

A ranar 18 ga watan Maris da ya gabata ne, Isra’ila ta sake kaddamar hari a Gaza wanda ya keta yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma a watan Janairu, inda ta kai hare-haren wuce gona da iri tare da kashe daruruwan Falasdinawa, ciki har da yara sama da 100.

Tun daga wannan lokacin, adadin wadanda suka mutu ya kai 1,391, yayin da wasu 3,434 suka jikkata, a cewar majiyoyin lafiya na Gaza.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: zanga zangar

এছাড়াও পড়ুন:

Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba

Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya ce sojojin kasar Iran ba za su sararawa gwamnatin Isra’ila ba.

Jagoran ya bayyana hakan ne a wani sakon bidiyo ga al’ummar Iran ranar Juma’a biyo bayan hare-haren wuce gona da iri da Isra’ila ta yi kan kasar wanda ya kashe fararen hula, masana kimiyya da kwamandojin soji.

Ayatullah Khamenei ya kara da cewa gwamnatin Isra’ila ba za ta kubuta daga wannan aika-aika ba, yana mai tabbatar wa al’ummar Iran cewa ba za a yi sakaci kan hakan ba.

Jagoran ya jaddada cewa muguwar gwamnatin sahyoniya ta tafka babban kuskure, sannan kuma shelanta yaki ne kan Iran.

Ayatullah Khamenei ya ci gaba da cewa: dukkanin jami’an kasar Iran da bangarori daban-daban na siyasa da kuma al’ummar Iran suna da ra’ayi daya dangane da wajabcin daukar wani mataki mai karfi wajen tunkarar gwamnatin sahyoniya ta ‘yan ta’adda.

Jagoran ya kara da cewa, bai kamata gwamnatin Isra’ila ta yi tunanin cewa ta ci bulus ba, kuma komi ya wuce.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila
  • Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka
  • An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 
  • Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila
  • Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa
  • Iran, ta yi wa Isra’ila ruwan makamai masu linzami
  • Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba
  • Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Isra’ila ta hana ayarin motocin agaji na arewacin Afrika shiga Gaza