HausaTv:
2025-08-01@09:16:24 GMT

An sake zanga-zangar kin jinin gwamnatin Netanyahu a Tel-Aviv

Published: 8th, April 2025 GMT

A Isra’ila dubban masu zanga-zanga ne suka fito kan titunan birnin Tel Aviv a wata sabuwar zanga-zangar kin jinin gwamnati a daidai lokacin da firaminista Benjamin Netanyahu ya gana da shugaban Amurka Donald Trump a birnin Washington.

Masu zanga-zangar a ranar Litinin sun yi Allah wadai da manufofin Netanyahu, ciki har da yunkurinsa na korar manyan jami’an tsaro da na shari’a na gwamnatin.

Sun kuma yi Allah wadai da sake dawo da yakin kisan kare dangi da ake yi wa al’ummar Gaza.

Iyalan ‘yan Isra’ilar da aka yi garkuwa da su a Gaza su ma sun shiga zanga-zangar, inda suka bukaci a kawo karshen yakin da kuma kulla yarjejeniyar tabbatar da sakin mutanen da aka kama.

Kungiyar dai ta ce za ta saki sauran mutanen da ake garkuwa da su ne kawai idan an sako sauren fursunonin Falasdinawa da Isra’ila ke rike da a gidajen yarinta, da kuma tabbatar da tsagaita bude wuta, da kuma janyewar Isra’ila gaba daya daga Gaza.

A ranar 18 ga watan Maris da ya gabata ne, Isra’ila ta sake kaddamar hari a Gaza wanda ya keta yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma a watan Janairu, inda ta kai hare-haren wuce gona da iri tare da kashe daruruwan Falasdinawa, ciki har da yara sama da 100.

Tun daga wannan lokacin, adadin wadanda suka mutu ya kai 1,391, yayin da wasu 3,434 suka jikkata, a cewar majiyoyin lafiya na Gaza.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: zanga zangar

এছাড়াও পড়ুন:

DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Wasu al’ummomi sun bayyana dalilan da suka sa suka karbi tsarin yin gwajin lafiyar ma’aurata kafin a daura musu aure.

A wasu lokutan, akan samu matsaloli sakamakon rashin gwajin jini kafin a hada mace da na miji aure. Matsalolin sun hada da yaduwar cututtuka, samun ‘ya’ya marasa lafiya da sauran wasu matsalolin.

NAJERIYA A YAU: Yadda Za A Dama Da Matan Arewa A Fannin Kimiyya DAGA LARABA: Abubuwan da ya kamata yara su yi yayin hutun makaranta

Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi nazari ne kan dalilan da suka sa wasu alummomin suka rungumi yin gwajin jini kafin aure.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza
  • Tallafin matar Tinubu na N1bn ga ’yan gudun hijirar Binuwai ya bar baya da kura
  • Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana
  • Adadin Falasdinawan da Isra’ila take kashewa a Gaza yanzu ya haura 60,000
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Amincewa Da Kasar Falasɗinu: Birtaniya Ta Gindaya Wa Isra’ila Sharuɗɗa
  • DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure
  • Shugaban Ivory Coast Ouattara zai sake takara wa’adi na huɗu
  • Za mu halasta kafa ƙasar Falasɗinu muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba — Birtaniya
  • Muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba za mu amince da kafa ƙasar Falasɗinu — Birtaniya