HKI Ta Kai Munanan Hare-hare Akan Yankin Khan-Yunus
Published: 7th, April 2025 GMT
A rana ta 21 da Isra’ila ta sake komawa yaki da al’ummar Falasdinu a Gaza, jiragen yakinta sun kai hare-hare munanan a yankin Khan-Yunus da ya yi sanadiyyar shahadar mutane da dama, da kuma jikkata wani adadin Falaasidinawa mai yawa.
Jim kadan bayan kai wannan harin ne dai kungiyar ta mayar da martini ta hanyar harba makamai masu linzami akan matsugunin ‘yan share wuri zauna a Asqalan da hakan ya yi sanadiyyar jikkatar ‘yan sahayoniya.
A gafe daya ana gudanar da yajin aiki na gama gari a yankin yammacin kogin Jordan saboda nuna kin amincewa da yadda ‘yan sahayoniya suke yi wa al’ummar Falasdinu kisan kiyashi. Kungiyoyin fararen hula ne su kirayi wannan yajin aikin, wanda ya game yankin na yammacin kogin Jordan.
A wani labarin daga Gaza, ma’aikatar kiwon lafiya ta sanar da cewa da akwai mutanen da sun haura miliyan biyu da suke fama da matsalar rashin abinci mai gina jiki.
Ma’aikatar ta yi wannan sanarwar ne adaidai lokacin da ake raya ranar lafiya ta duniya, tana mai kara da cewa; a kowane lokaci yanayin kiwon lafiya a zirin Gaza yana kara tabarbarewa.” Haka nan kuma ta yi gargadi akan rufe dukkanin hanyoyin shigar da abinci cikin yankin da hakan yake jefa rayuwar yara masu yawan gaske cikin hatsari.
Wani batu da hukumar kiwon lafiya ta yankin na Gaza, ta yi gargadi a kansa, shi ne yadda Isra’ila ta hana a shigar da riga-kafin shan inna cikin yakin, da hakan zai rusa kokarin da aka yin a watanni 7 a baya na fada da wannan cuta.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ƴan Ta’adda Sun Kashe Maharba 10 A Adamawa
Ƴan ta’adda da ake zargin Boko Haram ne sun kashe mutane 10 na yawucin dabbobi da kuma mambobin jami’an tsaron sa kai (CJTF) a garin Kwapre, dake cikin ƙaramar hukuma ta Hong a Jihar Adamawa.
Shugaban ƙaramar hukuma, Hon Usman Wa’aganda, ya tabbatar da wannan lamarin ga LEADERSHIP ta waya a ranar Lahadi a Yola, inda ya bayyana cewa wani mutum da ya samu raunuka daga harin ‘yan ta’addan yana samun kulawar likita a wani asibiti da ba a bayyana sunansa ba.
Daidaikun Kasashe Za Su Kara Karfi Idan Suka Hada Hannu Tare ‘Yansanda Sun Kama Wani Kato Bisa Zargin Cin Zarafin Wata Mata A AdamawaWa’aganda ya ce ‘yan ta’addan sun ƙone gidaje da dama da kuma amfanin gona, yana mai cewa wannan harin ba na farko bane, domin garin ya sha hare-hare sau da dama wanda ya haifar da asarar rayuka da dukiyoyi.
Ya nemi hukumomin tsaro su ƙara tura jami’ai a yankin domin taimakawa wajen kare al’umma da kuma tabbatar da tsaro.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp