Ambaliya Ta Hallaka Mutum 30 A Birnin Kinshasa Na Jamhuriyar Demokradiyar Congo
Published: 7th, April 2025 GMT
Ruwan sama kamar da bakin ƙwarya a Kinshasa, babban birnin Jamhuriyar Dimokaraɗiyyar Congo ya kashe aƙalla mutane 30 tare da haddasa ɓarna mai tarin yawa.
Ruwan saman ya janyo tsaiko wajen gudanar da al’amura a babban birnin tare da katse zirga-zirgan ababen hawa a kan titin Kinshasa, wanda ya taso daga tsakiyar birnin zuwa filin jirgin sama.
A gundumar Debonhomme da ke gabashin ƙasar, ruwan ya laƙume motoci da dama, lamarin da ya tilastawa wasu mazauna ƙasar yin hijira a yayin da wasu suka yi amfani da kwale-kwale kamar yadda jam’in kamfanin dillancin labaran AFP ya shaida.
Wasu daga cikin waɗanda abun ya shafa, sun maƙale a saman gidajensu bayan da ruwan ya mamaye matakalar shiga gidanjensu.
Bugu da ƙari, Ambaliyar ya haifar da cunkoson ababen hawa a birnin da ake fama da yawan zirga zirga.
Mazauna yankin da abin ya shafa sun shaidawa manema labarai cewa sun fusata bayan da gwamnati ta ƙi kawo musu agajin gaggawa.
rfi
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Ambaliya
এছাড়াও পড়ুন:
An Kaddamar Da Bikin Gabatar Da Jerin Shirye-shiryen Telebijin Da Fina-finai Na CMG A Birnin Astana
Gabanin tafiyar shugaban kasar Sin Xi Jinping birnin Astana na kasar Kazakhstan, inda zai halarci taron koli na Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya karo na biyu, an kaddamar da bikin gabatar da jerin shirye-shiryen shirye-shiryen telebijin da fina-finai, na babban gidan rediyo da telebijin na kasar Sin wato CMG na shekarar 2025 a birnin Astana.
Za a gabatar da shirye-shiryen CMG guda 12, ciki har da alakar dake tsakanin shugaba Xi Jinping da al’adun kasar Sin, da hanyar zamanintar da kasa mai salon kasar Sin na musamman da sauransu, a manyan kafofin watsa labaru na kasashen Kazakhstan, da Kyrgyzstan, da Tajikistan, da Turkmenistan, da Uzbekistan da dai sauransu.
Shugaban gidan CMG Shen Haixiong ya bayyana cewa, a ta bakin shugaba Xi Jinping, kasar Sin kyakkyawar abokiya ce ta kasashen tsakiyar Asiya, don haka ya kamata a kara yin kokari wajen raya makomar bai daya ta Sin da kasashen tsakiyar Asiya. Kuma kafar CMG ta yi hadin gwiwa tare da kafofin watsa labaru na kasashen tsakiyar Asiya, wajen gabatar da shirye-shirye, don sa kaimi ga aiwatar da ayyukan da aka cimma, a taron koli na Sin da tsakiyar Asiya na shekarar 2023, da kara gudanar da mu’amalar al’adu, da sada zumunta a tsakaninsu bisa manufofin da shugaba Xi ya gabatar. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp