HausaTv:
2025-08-01@09:43:19 GMT

Kasashen Mali da Nijar da Burkina Faso sun kira jakadunsu daga Aljeriya

Published: 7th, April 2025 GMT

Kasashen Mali, Nijar da kuma Burkina faso dake hade a kawancen Sahel na AES, sun sanar da kiran jakadunsu a Aljeriya domin tuntuba.

A wata sanarwa da aka karanta a gidan talabijin na kasar Mali a yammacin jiya Lahadi, kasashen uku sun sanar da kirawo jakadunsu domin tuntuba bayan da Aljeriya ta kakkabo wani jirgi marar matuki na kasar Mali a farkon wannan wata.

Aljeriya dai ta kakkabo jirgin sojojin na Mali marar matuki a cikin daren ranar 31 ga Maris zuwa 1 ga Afrilu, matakin da kasashen uku sukayi tir da shi.

A cewar gwamnatin Algiers, jirgin mara matuki da ake magana a kai ya shiga cikin kasar ne, saidai sojojin Mali sun tabbatar da cewa jirgin bai shiga cikin kasar Aljeriya ba.

Lamarin, wanda ya faru mako guda da ya gabata, kaashen na AES a wata sanarwa ta bai daya sun bayyana shi a matsayin “rashin gaskiya” da kuma keta dokokin kasa da kasa.

Firaministan Mali Abdoulaye Maiga ya musanta ikirarin Aljeriya na cewa jirgin mara matuki ya shiga sararin samaniyar Aljeriya, yana mai cewa lamarin ya nuna yadda Aljeriya ke goyon bayan ta’addanci.

A matsayin mayar da martani, Mali ta gayyaci jakadan Aljeriya tare da yanke shawarar janyewa daga kawancen sojan yankin na tsawon shekaru goma sha biyar.

Bidiyon da kungiyoyin ‘yan tawaye suka fitar ya nuna tarkacen jirgin da kamfanin Baykar na Turkiyya ya kera.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Za a kashe biliyan 712.26 don yi wa filin jirgin saman Legas garanbawul

Majalisar Zartarwa ta Kasa ta amince da kashe Naira biliyan 712.26 don yi wa wani sashe na filin jirgin saman a Murtala Muhammad da ke Legas garambawul.

Hakan dai ya biyo bayan zaman majalisar wanda Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya jagoranta a Abuja ranar Laraba.

NAJERIYA A YAU: Me dokar kasa ta ce kan karin wa’adin aiki da Shugaban Kasa ke yi? Za a fara yi wa ɗaliban jami’o’i gwajin ƙwaya — Gwamnatin Nijeriya

Aikin dai wani bangare ne na Naira biliyan 900 da aka ware domin inganta harkokin sufurin jiragen sama a fadin Najeriya.

Ministan Harkokin Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo ne ya bayyana hakan jim kadan da kammala taron majalisar, inda ya ce tuni har an ba da kwangilar aikin ga kamfanin gine-gine na kasar China (CCECC).

A cewar Ministan, aikin ya kuma kunshi canza kayayyakin da ake amfani da su a wurin saukar jirage na filin daga na da zuwa na zamani.

Keyamo ya kuma ce majalisar ta kuma amince a kashe Naira biliyan 49.9 wajen aikin katange filin jirgin na Legas domin a inganta tsaro a cikin shi,

Katangar mai tsawon kilomita 14.6 wacce ta karfe ce, za kuma a saka mata na’urori a jikinta da kyamarorin CCTV da fitilu masu amfani da hasken rana da kuma tituna a gefenta.

“Duk wanda ko kuma duk abin da ya rabi katangar za mu gan shi cikin gaggawa sannan a nuna wajen da yake,” in ji Minista Keyamo.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za a kashe biliyan 712.26 don yi wa filin jirgin saman Legas garanbawul
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
  • Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana
  • Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace
  • Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Nijar da Rasha sun ƙulla yarjejeniyar makamashin nukiliya
  • Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  •  Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta