Iran ta bakin kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar, Esmail Baghai, ta ce nahiyar turai sun tafka kure na tarihi, ta hanyar goyon bayan Isra’ila ta hanyar yin watsi da sammacin kama Benjamin Netanyahu.

Esmail Baghai ya bayyana haka ne a cikin wani sako a asusunsa na X, bayan ziyarar aiki da Netanyahu ya kai kasar Hungary duk da sammacin kame shi da kotun ICC ta bayar kan laifukan yaki da cin zarafin bil adama da gwamnatinsa ta yi a zirin Gaza.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya ce : Sammacin kame jami’an gwamnatin Isra’ila da kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa ta yi na nuni da yadda duniya ke nuna bacin rai kan kisan kiyashi, laifukan yaki, da laifukan cin zarafin bil’adama a Gaza, da kuma babbar bukatar kiyaye dokokin kasa da kasa da kuma kawo karshen rashin hukunta masu aikata munanan laifuka kan Falasdinawa.

A yammacin ranar Laraba ne Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya sauka a Budapest domin gudanar da ziyarar kwanaki hudu bisa gayyatar firaministan kasar Hungary Viktor Orban.

Shugaban masu tsattsauran ra’ayi na kasar Hungary ya gayyaci takwaransa na Isra’ila duk da cewa ana zargin Netanyahu da amfani da yunwa a matsayin hanyar yaki da kuma aikata laifukan cin zarafin bil’adama da suka hada da halaka a lokacin yakin kare dangi a Gaza.

A matsayinsa na mamba a kotun ICC, ya kamata kasar Hungary ta kama Netanyahu da ya isa kasar ta tsakiyar Turai tare da mika shi ga kotu, amma haka ya bar kasar salin alin.

Kotun ICC ta yi Allah wadai da Hungary saboda kin bin sammacin kama Netanyahu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Arsenal Da PSG: Wa Zai Yi Nasara A Gasar Zakarun Turai A Yau?

Wannan ya sa wasan yau zai zama mai ɗaukar hankali, domin kowanne daga cikinsu na burin ɗaukar kofin a karo na farko, domin a dakatar da yawan dariyar da ‘yan adawa ke musu.

A zagayen rukuni da suka haɗu a farkon wannan kakar, Arsenal ta lallasa PSG da ci 2-0.

Kocin Arsenal yanzu, Mikel Arteta, ya taɓa buga wasa a duka ƙungiyoyin.

Yana fatan ya zama kocin farko da zai jagoranci Arsenal ta lashe kofin Zakarun Turai.

Wannan ya sa magoya bayan Arsenal ke fatan ganin ƙungiyarsu ta yi abin mamaki a wasan da za a fara da misalin ƙarfe 8 na dare agogon Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • Iran ta sha alwashin ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Nijar
  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • Iran Da Iraki Sun Ce An Kammala Shimfida Layin Dogo Daga Shalamcheh Zuwa Basra
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Arsenal Da PSG: Wa Zai Yi Nasara A Gasar Zakarun Turai A Yau?
  • Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
  • Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje
  • Kasar Sin Za Ta Samar Da Dokar Da Ta Shafi Raya Kasa