HausaTv:
2025-05-01@00:36:08 GMT

Araqchi: Babu Wata Tattaunawa Da Aka Gudanar Tsakanin Amurka Da Iran

Published: 7th, April 2025 GMT

Iran ta sake nanata matsayinta na kin shiga shawarwari kai tsaye da Amurka kan shirinta na nukiliya, maimakon haka ta bukaci a ci gaba da shawarwarin ta hanyar masu shiga tsakani.

Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi ya bayyana hakan, yana mai cewa babu wata tattaunawa da aka da Washington, kuma ba za a yi irin wannan tattaunawa ba sai dai ta hanyar masu shiga tsakani.

“Mun bayyana matsayinmu, muna goyon bayan bin hanyoyi na  diflomasiyya da tattaunawa, amma ta hanyar masu shiga tsakani. Tabbas, ba a gudanar da wata tattaunawa kai tsaye tsakanin Iran da Amurka ba, ” in ji Araghchi a cikin wata sanarwa da ya fitar a dandalin Telegram.

Kalaman nasa sun zo ne bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar kai wa Iran hari idan ta ki amincewa da kulla wata sabuwar yarjejeniya kan shirinta na nukiliya.

Araqchi yace, Iran ba zata taba yarda da duk wani mataki na shigo-shigo ba zurfi ba, domin kuwa irin wannan ne aka yi wa kasar Libya, a lokacin da ta yi watsa da shirinta na nukiliya kuma aka ci gaba da kakaba mata takunkumai, daga karshe kuma kasashen turai da kungiyar tsaro ta NATO suka hambarar da gwamnatin kasar a lokacin mulkin Ghaddafi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Riza’i: Babu Hannun  Waje A Cikin Hatsarin Da Ya Faru A Tashar Ruwa Ta Shahid Raja’i

Kakakin kwamitin tsaron kasa a majalisar shawarar musulunci ta Iran ya bayyana cewa; ” Ya zuwa yanzu ba za mu iya yin hukunci akan dalilan da su ka haddasa fashewar abubuwa a tashar ruwa ta Shahid Raja’i ba, amma za mu iya cewa babu hannu waje a ciki.

Kakakin kwamitin tsaron kasar ta Iran Ibrahim Rizai wanda ya halarci taron da aka yi a Majalisa akan fashewar da aka samu a tashar ruwan ta shahid Raja’i, ya kuma kara da cewa; Fahimtata da abinda na ji daga abokan aikina dangane da abinda ya faru a tashar ruwa ta Shahid Raja’i, da kuma rahotannin da su ka iso mana, shi ne cewa abinda ya farun ba shi da alaka da waje.”

 A ranar Asabar da ta gabata ne dai wasu abubuwa su ka fashe a tashar ruwa ta Shahid Raja’i dake Bandar Abbas a kudancin Iran, wanda ya haddasa asarar rayuka da kuma jikkatar daruruwan mutane.

An bude kwamitin bincike domin gano hakikanin abinda ya faru a tashar da kuma haddas fashewar abubuwan masu karfi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Binciken Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Cin Zali Ta Hanyar Kakaba Haraji Ya Illata Kimar Amurka
  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Yanayin Rudani Na Tsawon Kwanaki 100 Kashedi Ne Ga Amurka
  • Iran Da Iraki Sun Ce An Kammala Shimfida Layin Dogo Daga Shalamcheh Zuwa Basra
  • Riza’i: Babu Hannun  Waje A Cikin Hatsarin Da Ya Faru A Tashar Ruwa Ta Shahid Raja’i
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Babu Wata Tattaunawa Tsakanin Sin Da Amurka Game Da Batun Haraji
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Talata ce ɗaya ga watan Zhul Qi’ida — Sarkin Musulmi
  • Takht Ravanji: Iran Ba Za Ta Taba Yin Tattaunawa Akan Dakatar Da Tace Sanadarin Uranium Ba