Araqchi: Babu Wata Tattaunawa Da Aka Gudanar Tsakanin Amurka Da Iran
Published: 7th, April 2025 GMT
Iran ta sake nanata matsayinta na kin shiga shawarwari kai tsaye da Amurka kan shirinta na nukiliya, maimakon haka ta bukaci a ci gaba da shawarwarin ta hanyar masu shiga tsakani.
Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi ya bayyana hakan, yana mai cewa babu wata tattaunawa da aka da Washington, kuma ba za a yi irin wannan tattaunawa ba sai dai ta hanyar masu shiga tsakani.
“Mun bayyana matsayinmu, muna goyon bayan bin hanyoyi na diflomasiyya da tattaunawa, amma ta hanyar masu shiga tsakani. Tabbas, ba a gudanar da wata tattaunawa kai tsaye tsakanin Iran da Amurka ba, ” in ji Araghchi a cikin wata sanarwa da ya fitar a dandalin Telegram.
Kalaman nasa sun zo ne bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar kai wa Iran hari idan ta ki amincewa da kulla wata sabuwar yarjejeniya kan shirinta na nukiliya.
Araqchi yace, Iran ba zata taba yarda da duk wani mataki na shigo-shigo ba zurfi ba, domin kuwa irin wannan ne aka yi wa kasar Libya, a lokacin da ta yi watsa da shirinta na nukiliya kuma aka ci gaba da kakaba mata takunkumai, daga karshe kuma kasashen turai da kungiyar tsaro ta NATO suka hambarar da gwamnatin kasar a lokacin mulkin Ghaddafi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Miliyoyin Mutane Sun Gudanar Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran
A yau Asabar aka gudanar da bikin ranar ” Idin Gadir” a nan birnin Tehran, wanda ya tashi daga dandalin “Inqilab” zuwa dandalin ” Azadi” mai nisan kilo mita 10. Bisa la’akari da halin yake da ake ciki, an bai wa bikin na bana taken: Iran ce, takobin Zulfikar Na Imam Ali.”
Miliyoyin mutane ne dai su ka cika filin bikin na birnin Tehran da mutane su ka fara taruwa tun da tsakar rana, har zuwa bayan faduwar rana. A bisa kirdado kusan mutane miliyan 3 ne su ka taru a nan Tehran.
A cikin sauran birane da garuruwan Iran an yi wannan irin gangamin na raya ranar Idin Gadir wanda yake tattare da girmama shahidan da su ka kwanta dama sanadiyyar hare-haren ta’addancin HKI. Haka nan kuma mahalarta bikin na Gadir sun jinjinawa dakarun kare juyin musulunci na Iran da kuma sojojin kasar akan martanin da su ka mayarwa da HKI a daren jiya Juma’a da kuma a yau Asabar.